← Book details Uwani Yar Kashin Gwuiwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 71

Sashe 17

Uwani Yar Kashin Gwuiwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ƙwata wannan abar ce fa aka aura wa Jafar, imagine a ce wannan ce sirikata." Hajiya Falmata ta ƙare wa Uwani kallo sannan ta saki wani malalacin murmushi ta furta.
"Haba ƙawata wai da wannan 'yar abar ce ke barazana da aurenki? Tun da ƙuruciya ba ki yi yaji ba sai yanzu? Babu inda za ki, matuƙar kin bi duk tattaunawar da muka yi wallahi na faɗa miki da ƙafarta za ta kori kanta babu boka babu malam." Sai a lokacin Mami ta ƙara jin ƙwarin gwiwa, Hajiya Falmata ta ci gaba da biya mata miyagun shawarwari sannan suka yi sallama.

Da murna Dada ta tarbi Uwani don ita kanta ba ƙaramin kewarta ta yi ba, dalilin da ya sa tun safe ta sa baba Mamman ya ɗauko ta. Shi kuma ya ce a bari zuwa bayan azahar sai Jafar ya ɗauko ta. Kuma ya yi haka ne domin so yake kafin lokacin tariyarsu su ƙara samun fahimtar juna.

Sai da aka yi sallar Margriba kamar yadda Baba Yunusa ya ce za a zauna ya tara 'yan uwansa, Dada, na Madina, Uwani, Jafar da kuma Mami. Sai da ya buÉ—e taron da addu'a bayan kowa ga gama sannan ya fara magana.

"Alhamdu Lillah! Na san wasu daga cikinku sun san dalilin wannan zaman yayin da wasu kuma ba su sani ba. Maƙasudin zamanmu a kan kai Jafar da kuma ke Uwani ne." Jafar ya sunkuyar da kai ƙasa rai a bace. Tsabar takaici ya sa Mami yin ƙwafa a fili, Dada ta dube ta haɗe da taɓe fuska ta ce.

"Aure dai Allah Ya haÉ—a duk mai hassada sai rabo ya kashe shi, yara su haihu kuma a mayar da sunansa." Mami ta shiga aika wa Dada harara a fakaice.

"Jafar a yanzu wani nauyi ya hau kanka domin aure ba wasa ba ne, ka riƙe yarinyar mutane amana don a yanzu da kake gani komai nata ya dawo ƙarƙashin ikonka. Ke kuma Uwani wannan da kike gani aljannarki na ƙarƙashin ƙafarsa, ki bi mijinki sau da ƙafa yi na yi bari na bari. Duk abin da kika san zai faranta ran mijinki shi za ki yi, abin da ba ya so sai ki haƙura da shi don zaman aure ɗan haƙuri ne." Sai da Baba Yunusa ya numfasa sannan ya ci gaba.

"Mun tattauna ni da 'yan uwana a kan za ku tare tare da Mahaifinku tun da an riga an ɗaura aure babu fa'idar a ce za a zauna har sai nan da wata biyu idan auren su Shukra ya zo. A don haka idan Allah Ya kai mu ranar Laraba mai zuwa ne mahaifinku Mamman ya ce za a ƙarasa gyara komai da saka komai na gidan, tun da akwai wadataccen wuri za ku zauna a ƙaramin part ɗin da ke gefen na Maminku." Wani irin tuƙuƙin zafi ne a zuciyar Mami har za ta ƙi amimcewa da hakan sai kuma ta tuna da huɗubar ƙawarta Hajiya Falmata.

"Saboda haka muka yanke shawarar idan Allah Ya kai mu juma'a mai zuwa ne tariyarku, kuma bayan nan za a nema wa Uwani wata makarantar za ta ci gaba da karatunta. Idan ya so bayan sun yi hutu sai ka ɗauki matarka ku wuce wurin aiki." Jafar ya yi shiru ba tare da ya amsa ba. Wannan maganar ta ƙarshe ba ƙaramin daɗi ta yi wa Mami ba, don a wannan lokacin ne za ta ci karenta babu babbaka a kan Uwani.

"Ni iya abin da zan iya ce wa kenan, Dada kafin mu zo kan ki ko akwai mai magana a cikin?" GabaÉ—aya suka girgiza kai ban da Baba Mustafa da ya ce yana da abin cewa.

"Sannu da ƙoƙari Yaya Allah Ya ƙara girma, duk bayananka a kan tsari suke. Amma abin da nake gani me zai hana a ɗaga tariyar ta su zuwa nan da kamar sati biyu zuwa uku, duba da yanayin ragowar shirye-shiryen da ya kamata a yi musu. Daga haɗa lefe har zuwa wani shirye-shirye na su na mata, sannan a wannan lokacin mahaifiyar yarinyar na cikin halin rashin 'yarta. Amma bayan wannan lokacin ita kanta za ta samu nutsuwar gudanar da bikin yadda ya kamata." Dada ta jinjina kai sannan ta furta.

"Wallahi Mustafa ka yi kyan kai, saboda Allah kamar gajiya na yi da Uwanin da za a ce nan da kwana huÉ—u a kai ta É—akin miji." Baba Yunusa ya yi murmushi ya furta. "Wannan haka ne, Dada me za kike ganin ya dace bayan haka." Dada ta yi jim sannan ta furta.

"Ni dai kam nasiha ce zan yi wa Jafaru da ita Uwani, amma kam ba yanzu zan yi musu ba sai ranar da za su tare. Don ina gudun na tofar da yawun bakina a banza, su barbaɗar da nasihar da na yi musu tun kafin tariyarsu." Tambayar Mami aka yi ko tana da abin faɗa ta ce babu, don haka suka ƙarƙaren zaman tun ba a gama addu'a ba Mami ta sa ƙafarta ta fice rai a ɓace.

07062062624
#Ummou Aslam Bint Adam🌚
*UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA*

©AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye.

SHAFI NA GOMA

Tun daga wannan ranar su baba Yunusa suka shiga hada-hadar shirye-shiryen tariyar auren Uwani da Jafar, a ɓangaren baba Mamman sai abin ya haɗe masa biyu ga tariyar su Mami ga kuma ta shirin su Jafar. Babba Mamman da kansa ya kira Jafar ya nemi da ya bada wani abin domin ba don da auren ya zo a haka ba, ba shi da tsarin haɗa wa ɗa namiji lefe sai dai ya yi komai da kansa ko ya fi ganin darajar auren da aka ba shi. Amma fir Jafar ya ce ba shi da wasu wadatattun kuɗi, sai da ya ga ran mahaifinsa ya ɓaci sosai sannan ya iya bayar da dubu ɗari uku. Su ma sai da Baba Mamman ya yi masa barazanar zai ɗaga wani filinsa ya sayar a haɗa wa Uwani lefen da shi sannan ya bayar.

Mami ban da 'yan uwanta babu wanda ta iya gaya wa sai kuma ƙawarta Hajiya Falmata da ta san da maganar, babban tashin hankalinta kada Hajiya Salima ta ji labari ta ce Safna ba za ta auri Jafar ba. Don haka ta kira Jafar a ɗaki ta gargaɗe shi a kan ko da wasa kada ya sake ya faɗa wa Safna maganar aurensa, don a yadda ta tsara auren ko wata biyu ba zai rufa ba Uwani za ta bar gidan da ƙafarta.

Dada da ƙafarta ta je har garinsu mahaifiyar Maryama ta sanar da su duk halin da ake ciki, ba ƙaramin murna suka yi ba suka yi fatan alheri. Haka Dada ta sa aka dinga sanarwa da jama'a wunin bikin Uwani, shi kuwa Jafar har kawo lokacin kallon abin yake kamar a mafarki.

Yana shiga ɗakin abokinsa Amir zama ya yi a gefen gado ya zuba uban tagumi, labule Amir ya ɗaga ya shiga hannunsa ɗauke da karan sigari yana zuƙa. Da mamaki ya dubi Jafar ya furta.

"Abokina yaushe ka shigo? Kai fa daɗina da kai ka yi wa mutum zuwan bazata, yanzu kuma da ka zuƙi warin 'yar so sai ka hau ni da sababi." Jafar bai ɗago ba ya furta.
"Miƙo mini kara ɗaya ka ba ni lighter zan zuƙa." Baki sake Amir ya ƙarasa bakin gadon ya ce. "Ko dai mafarki kake abokina?"

"Na ce ka ba ni." Jafar ya faɗa a ɗan zafafe. Ba musu ya miƙa masa, Jafar ya hau kiciniyar kunnawa. Ganin ya kasa saboda rashin sabo ya sa Amir ya karɓa ya kunna masa, Jafar ya kai baki ya zuƙa da ƙarfi lokaci ɗaya ya ƙware ya hau tari.

"Malam za ka kashe kanka a banza da wofi, wai me yake faruwa ne?"

"Da zan mutu ɗin ma ai da ya fi mini komai sauƙi." Cikin zaro ido Amir ya ce. "Wa ya ɓata maka rai ne?" Jafar ya kauda kai gefe murya a dashe ya ce.
"Aure aka yi mini."

Amir ya shafa gemu yana sakin wani murmushi sannan ya furta. "Ɗan iskan ƙarya. Kai yanzu don an maka auren ne har kake wannan..."

"Ka san wa aka aura mini? Uwani fa, wannan ƙanwar ta wa da ta taɓa sace maka tayar mashin." Jim Amir ya yi da sauri ya ce. "Wai wannan black beautyn? Amma fa kai shege ne, ka tsinci dami a kala ka zauna ka na sa kanka a damuwa?" Kalaman Amir suka ɓa ta ran Jafar bai tanka masa ba ya saka kai ya fice. Kafin ya ƙarasa fita Amir ya ce. "Billahillazi ni zan ɗauki nauyin kazar amarci idan muna raye." Jafar ya dawo da kansa a ƙufule ya ce.
"Sai dai ka cinye abarka don ubanka."

Amir ya bushe da dariya sannan ya bi bayan Jafar, sai da ya shawo kansa da ƙyar sannan ya labarta masa yadda auren na sa ya kasance. Sam Amir bai ga abin damuwa ba, don ce masa ya yi bayan auren Uwani babu jimawa kawai ya auri Safna tun da ita ce zaɓinsa.

Kamar yadda baba Mamman ya tsara juma'ar da ta zo a ita ce su Mami suka tare a sabon gidansu, babban gida ne sosai don haka Mami ta ƙara jin kanta ya daɗa girma. Ta dinga kallon Facalolinta tana basarwa don ita a yadda ta so sam ba ta so sun kwaso jiki da gayyar 'ya'yansu sun zo mata ba. Yamma liƙis suka fara haramar tafiya a nan ne kuma baba Mamman ya ce Dada ba za ta tafi ba sai ta yi kwana biyu. Da yake a part ɗin su Mami har da ɗakin Dada da banɗakinta a ciki, fasalin gidan ba ƙaramin birge Uwani ya yi ba. Don haka da ta ji Dada ta ce ba a ranar za su tafi ba ko a jikinta. Mami ba ƙaramin haushi ta ji ba, don dai tana shakkar Daddy shi ya sa ba ta yi wa Dada kora da hali ba har suka gama kwanakinsu suka koma.
Chapter 17 · 0% Book details