Sashe 16
Uwani Yar Kashin Gwuiwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Uwani ta furta a lokacin da ta fita da Naziru tsakar gida da ke ƙwala ihu. A yadda ta lura kusan ilahirin mutanen gidan duka sun tashi, wata dabara ce ta faɗo mata don haka ta buga tsalle a tsakar gidan ta ce.
"Waɗanda kuke leƙenmu muna gano ku, ke wato har da ke ko. Wallahi ɗaya bayan ɗaya za mu bi ku mu ƙwaƙwale idanunku idan ba ku koma kun kwanta ba." Ta saki hannun Naziru ai kuwa da gudu ya faɗa ɗaki yana ihu, sai ta tafi da gudu ta nufi ɗakin mahaifiyarta, a guje ta ji mutanen ɗakin suna shigewa uwar ɗaki wasu na hantsilawa. Nan ma ta nufi ɗakin kishiyar mahaifiyarta ta razana su, sai da ta tabbatar da sun gama tsorata kowa ya shige uwar ɗaki sannan ta lallaɓa ta isa banɗaki ta wanke fuskarta. Ta duƙunƙune hijabin Inna Suwaiba ta soke a hammata, sai da ta shirya sosai sannan ta nufi ɗakin mahaifiyarta da gudu tana faɗin. "Wayyo Allah! Ku taimaka mini za su ƙara janye ni." Tana shiga ɗakin ta tarar falon mahaifiyarta babu kowa an banke uwar ɗaki sai ƙananan yara da ke kuka suna buga ƙofa, saboda kada a gano Uwani ita ma ta fara bubbuga ƙofar tana ihu. Da ta lura ba za su buɗe mata ba sai ta janyo ƙofar falo ta datse.
Har aka yi assalatu babu wanda ya yunƙurin fitowa daga ɗakin, duk da duka baƙin gidan a zuciyarsu kowa ya ayyana gari na wayewa tafiya zai yi. Amma da sun tuna kashedin da aka yi musu a kan kada wanda ya bar gidan har sai an yi sadakar uku sai jikin kowannensu ya yi sanyi. Sai da gari ya yi tangararan sannan Indo ta yi ƙarfin halin buɗe ƙofa, kamar sababin munafukai haka mutane suka dinga leƙowa ɗaya bayan ɗaya suna fitowa suna yin alwala suna sallah. Duk wannan abin da ya faru bayan da gari ya waye babu mutum ɗaya da ya jajantawa kowa, domin kowa a tsorace yake. Su Uwani suna zaune sai ga Aramma ya shiga ɗakin kansa ya yi waɗansu ƙulalai sun fi biyar, daidai tsakiyar hancinsa har wani ja ya yi yana maiƙo. Da mamaki suka bi shi da kallo, Aramma ya zauna daɓar jikinsa zafi zau da zazzabi. Gaishe shi mutanen ɗakin suka yi, suna son jin abin da ya faru da shi suna tsoro. Hannu ya sa a aljihu ya zaro kuɗin ya ce. "Ungo wannan Maryama, kuɗinki na jiya ne. Wannan kuma kyautar dubu hamsin ce na ba ki ita ma Indo zan miƙa mata nata." Baki sake Maryama ta bi shi da kallo, ta ce.
"Malam dubu hamsin fa? An ya ba mantawa ka yi ba?" Aramma ya dube ta a fusace da ya tuna gargaɗin fatalwa sai ya wayance ya sassauta murya ya furta. "Maryama shaidar da za ki yi wa mijinki kenan? Kyautatawa ce kawai ta sa na ba ku." Maryama hannu na rawa ta sa ta karɓa tana zuba masa godiya, Aramma har ya miƙe zai fita Inna Suwaiba ta ce. "Aramma ungo shafa-shafa sai ka shafa a malolon nan na ka, Allah dai ya sawaƙe sanyi haka yake lokaci ɗaya ka ga wuri ya luluye. Ko kuma bige wa ka yi ne da dare?" Aramma da ba ya son a ja doguwar magana ya karɓa ya yi gaba ba tare da ya amsa mata ba, ɗakin Indo ya faɗa ita ma ya sallame ta ya koma ɗakinsa don ilahirin jikinsa ciwo yake masa. Aramma na shiga ɗaki sai ga Indo jiki na rawa ta shiga wurin Maryama suka fara tattaunawa cikin mamaki, ba su ƙara nutsa wa a tekun mamaki ba sai da suka ji Aramma ya ce a yi shinkafa da miyar dage-dage da rana. Wannan sabon sauyi da suka samu daga wurin Aramma ba ƙaramin daɗi ya yi musu.
A na gobe Uwani za ta koma gida wurin ƙarfe goma sha biyu na dare ana zaune ana ɗan hira, ta hangi Aramma ya suri buta ya yi banɗaki. Sai da ta tabbatar da hankulan mutane ba ya kanta ta saci jiki ta nufi banɗaki, da yake banɗakin ya yi nesa da ɗakuna don haka ta laɓe a can kusurwar bango ta fara magana.
"Baba ga tawagar 'ya'yanka sun dawo. Kada ka tsorata mune dai fatalen nan." Aramma da ke tsugunne a kan masai sai abin ya yi masa a daidai, saboda wata sabuwar gudawa ce ta tsarge shi. Gumi ya fara tsattsafo masa ya ce. "To 'ya'yana don Allah kada ku taɓa lafiyata, wallahi har yanzu ban warke ba."
"Ba za mu sake cutar da kai ba, domin ƙawarmu wato matacciyar 'yarka ta ce ta ga irin kyautatawar da kake yi wa iyayenta da 'yan uwanta. Ki yi masa magana ya ji sabuwar muryarki ta cikin jinsin fatalwa." Uwani ta yi maganar tana wani fuffuka, sannan ta maƙale murya ta furta.
"Baba ni zan tafi da kai na fi so na dinga ganinka." Tamkar an buɗe fanfo haka cikin Aramma ya birge, ya ci gaba da sakin gudawa babu ƙaƙƙautawa. Cikin tashin hankali ya ce. "Na yafe don Allah ki je ki ɗauki mahaifiyarki."
"Shi kenan Baba zan dai dinga kawo muku ziyara a ɓoye duk dare ina ganin rayuwar da kuke yi, idan na ga saɓanin abin da ka fara yi wallahi cikin tumbinka zan shiga, na kannaɗe hanjinka ita kuma kodarka na fansarwa shugaba." Uwani ta furta tana gimtse dariyarta.
"Wallahi komai zan ci gaba da yi idan na saɓa ki mini duk abin da za ki yi mini."
"Mu zamu tafi Baba sai mun sake zagayowa." Uwani na gama faɗar haka ta fara wata fuffuka tana gurnani sannan ta saɗaɗa ta bar wurin. Saboda yadda Aramma ya razana bayan da ya gama uzurinsa a duƙe ya dinga tafiya, saboda yadda ya ji ƙafafuwansa sun yi sanyi har sun gagara ɗaukar nauyin gangar jikinsa.
Ranar da aka yi sadakar uku dai tun da safe wasu daga cikin 'yan gaisuwa suka fara watsewa, domin dama wasu tamkar a kan ƙaya suke. Ita ma Uwani sai da aka yi sallar la'asar sannan Aramma ya zo ya sanar da Maryama an zo ɗaukan Uwani, ta so Uwani ta ƙara kwanaki amma babu yadda ta iya haka ta danne. Wasu daga cikin 'yan uwan mahaifiyarta sai tsokanarta suke suna amarya sai sun zo biki. Kafin Uwani ta fita sai da Maryama ta sata a gaba ta yi mata nasiha sosai.
Fakare Uwani ta yi tana sauraronta kamar nasihar na shigarta, sai gyaɗai kai take tana amsawa. Sai da ta gama sauraron mahaifiyarsa sannan ta ce. "Ni kam Inna don Allah zan faɗa miki wata magana amma don Allah kada ki faɗa wa kowa." Take gaban Maryama ya faɗi amma sai ta basar ta ce. "Ina jin ki babu wanda zai ji Uwanina." Duk abin da ya faru tun daga farko har ƙarshe ta sanar da ita tana dariya, ita kanta Maryama dariya take sheƙawa sanna ta riƙe baki ta furta. "Allah Ya shirye ki Uwani ni dai wallahi ban san halin wa kika ɗauka ba, mahaifinki dai har ya fi ni sauƙin kai. Allah Ya shirya ki ko ba komai kin samar mana 'yanci." Suna cikin haka suka ji ƙarar horn da sauri Uwani ta sungumi jakar kayanta, ta ɗauko hijabinta ta saka. Sai da ta yi wa mutanen gidan sallama da Aramma sannan ta ƙarasa bakin motar cikin murna, don tun daga nesa ta hango motar baba Mamman. Don haka da saurinta ta buɗe motar tana faɗin.
"Daddy wallahi na yi kewar Dada, ƙila ma ita tana can ko a jikin..." Kalamanta suka maƙale a maƙoshi sakamakon ido biyu da suka yi da Jafar. Wata uwar harara ya banka mata, ta yamutsa fuska tana ƙare masa kallo ta ce.
"To kai kuma ina motarka ka É—auko ta Daddy?" Jafar bai tanka mata ba ya fisgi motar da gudun gaske har sai da wasu yara suka matsa a guje.
Suna cikin tafiya babu wanda ya tanka wa wani sai Uwani ta fashe da dariya har da ƙyaƙyatawa, a fusace Jafar ya waigo ya zuba mata manyan idonsa. Sai kuwa Uwani ta sake kwashewa da dariya, gangara motar ya yi ya faka ya ɗauke kai gefe a daƙile ya ce. "Fice mini daga mota."
Uwani ta gimtse dariyarta sannan ta ce. "Kamar ya na sauka ai ba motarka ba ce."
"Uban me kike wa dariya?"
Uwani ta yi murmushi ta ce, "Wallahi dariya ka ba ni, ni dai ba baƙuwa ba ce a wurinka atoh. Kuma dai komai na ka Dada ta ba ni labari tun kana jariri har fa tunbiɗin da ka dinga yi kana yaro. Sai kuma na ga ka fafaki mota kana yin wani irin tuƙin 'yan Kaduna-Zaria, to wai ni birgar me za ka yi mini?" Jafar ya haɗiyi wani yawu mai ɗaci haɗe da fusgar da iska mai zafi, jin irin maganganun da Uwani ta faɗa masa. Yana shirin yin magana Uwani ta sake sakin wata dariyar tana faɗin.
"Kasan Allah yadda ka iya fafakar motar nan da Inuwan Toyota zai ganka tsaf zai É—auke ka kwandasta, saboda wataran idan ya gaji ya ba ka É—ani..."
"Fice mini a mota." Ya furta mata cikin tsawa.
"Wallahi ba zan fita ba ai motar Daddy ce, malam kada ka yi mini gori ni nan gaba ma jirgin sama zan tuƙa." Kalamanta na ƙarshe suka kusa ba shi dariya. 'Yarinyar da cikakkun sentence na hausa ma ba ta iya haɗawa ba ita ce za ta tuƙa jirgin sama.' Ya raya a ransa. Ganin za ta ɓata masa lokaci ya sa ya fisgi motar ya ci gaba da sharara gudu, har suka ƙarasa gida wani bai sake kula kowa ba.
Tun Jafar bai gama faka motar ba Uwani ta suri jakar kayanta ta ɓalle murfin motar ta fice a guje ko rufe motar ba ta tsaya yi ba, tun daga soro ta fara ƙwalla wa Dada kira tana washe baki. Mami da ta rako aminiyarta Hajiya Falmata ganin Uwani ya sake tado mata da wani malolon baƙin ciki.
"Waɗanda kuke leƙenmu muna gano ku, ke wato har da ke ko. Wallahi ɗaya bayan ɗaya za mu bi ku mu ƙwaƙwale idanunku idan ba ku koma kun kwanta ba." Ta saki hannun Naziru ai kuwa da gudu ya faɗa ɗaki yana ihu, sai ta tafi da gudu ta nufi ɗakin mahaifiyarta, a guje ta ji mutanen ɗakin suna shigewa uwar ɗaki wasu na hantsilawa. Nan ma ta nufi ɗakin kishiyar mahaifiyarta ta razana su, sai da ta tabbatar da sun gama tsorata kowa ya shige uwar ɗaki sannan ta lallaɓa ta isa banɗaki ta wanke fuskarta. Ta duƙunƙune hijabin Inna Suwaiba ta soke a hammata, sai da ta shirya sosai sannan ta nufi ɗakin mahaifiyarta da gudu tana faɗin. "Wayyo Allah! Ku taimaka mini za su ƙara janye ni." Tana shiga ɗakin ta tarar falon mahaifiyarta babu kowa an banke uwar ɗaki sai ƙananan yara da ke kuka suna buga ƙofa, saboda kada a gano Uwani ita ma ta fara bubbuga ƙofar tana ihu. Da ta lura ba za su buɗe mata ba sai ta janyo ƙofar falo ta datse.
Har aka yi assalatu babu wanda ya yunƙurin fitowa daga ɗakin, duk da duka baƙin gidan a zuciyarsu kowa ya ayyana gari na wayewa tafiya zai yi. Amma da sun tuna kashedin da aka yi musu a kan kada wanda ya bar gidan har sai an yi sadakar uku sai jikin kowannensu ya yi sanyi. Sai da gari ya yi tangararan sannan Indo ta yi ƙarfin halin buɗe ƙofa, kamar sababin munafukai haka mutane suka dinga leƙowa ɗaya bayan ɗaya suna fitowa suna yin alwala suna sallah. Duk wannan abin da ya faru bayan da gari ya waye babu mutum ɗaya da ya jajantawa kowa, domin kowa a tsorace yake. Su Uwani suna zaune sai ga Aramma ya shiga ɗakin kansa ya yi waɗansu ƙulalai sun fi biyar, daidai tsakiyar hancinsa har wani ja ya yi yana maiƙo. Da mamaki suka bi shi da kallo, Aramma ya zauna daɓar jikinsa zafi zau da zazzabi. Gaishe shi mutanen ɗakin suka yi, suna son jin abin da ya faru da shi suna tsoro. Hannu ya sa a aljihu ya zaro kuɗin ya ce. "Ungo wannan Maryama, kuɗinki na jiya ne. Wannan kuma kyautar dubu hamsin ce na ba ki ita ma Indo zan miƙa mata nata." Baki sake Maryama ta bi shi da kallo, ta ce.
"Malam dubu hamsin fa? An ya ba mantawa ka yi ba?" Aramma ya dube ta a fusace da ya tuna gargaɗin fatalwa sai ya wayance ya sassauta murya ya furta. "Maryama shaidar da za ki yi wa mijinki kenan? Kyautatawa ce kawai ta sa na ba ku." Maryama hannu na rawa ta sa ta karɓa tana zuba masa godiya, Aramma har ya miƙe zai fita Inna Suwaiba ta ce. "Aramma ungo shafa-shafa sai ka shafa a malolon nan na ka, Allah dai ya sawaƙe sanyi haka yake lokaci ɗaya ka ga wuri ya luluye. Ko kuma bige wa ka yi ne da dare?" Aramma da ba ya son a ja doguwar magana ya karɓa ya yi gaba ba tare da ya amsa mata ba, ɗakin Indo ya faɗa ita ma ya sallame ta ya koma ɗakinsa don ilahirin jikinsa ciwo yake masa. Aramma na shiga ɗaki sai ga Indo jiki na rawa ta shiga wurin Maryama suka fara tattaunawa cikin mamaki, ba su ƙara nutsa wa a tekun mamaki ba sai da suka ji Aramma ya ce a yi shinkafa da miyar dage-dage da rana. Wannan sabon sauyi da suka samu daga wurin Aramma ba ƙaramin daɗi ya yi musu.
A na gobe Uwani za ta koma gida wurin ƙarfe goma sha biyu na dare ana zaune ana ɗan hira, ta hangi Aramma ya suri buta ya yi banɗaki. Sai da ta tabbatar da hankulan mutane ba ya kanta ta saci jiki ta nufi banɗaki, da yake banɗakin ya yi nesa da ɗakuna don haka ta laɓe a can kusurwar bango ta fara magana.
"Baba ga tawagar 'ya'yanka sun dawo. Kada ka tsorata mune dai fatalen nan." Aramma da ke tsugunne a kan masai sai abin ya yi masa a daidai, saboda wata sabuwar gudawa ce ta tsarge shi. Gumi ya fara tsattsafo masa ya ce. "To 'ya'yana don Allah kada ku taɓa lafiyata, wallahi har yanzu ban warke ba."
"Ba za mu sake cutar da kai ba, domin ƙawarmu wato matacciyar 'yarka ta ce ta ga irin kyautatawar da kake yi wa iyayenta da 'yan uwanta. Ki yi masa magana ya ji sabuwar muryarki ta cikin jinsin fatalwa." Uwani ta yi maganar tana wani fuffuka, sannan ta maƙale murya ta furta.
"Baba ni zan tafi da kai na fi so na dinga ganinka." Tamkar an buɗe fanfo haka cikin Aramma ya birge, ya ci gaba da sakin gudawa babu ƙaƙƙautawa. Cikin tashin hankali ya ce. "Na yafe don Allah ki je ki ɗauki mahaifiyarki."
"Shi kenan Baba zan dai dinga kawo muku ziyara a ɓoye duk dare ina ganin rayuwar da kuke yi, idan na ga saɓanin abin da ka fara yi wallahi cikin tumbinka zan shiga, na kannaɗe hanjinka ita kuma kodarka na fansarwa shugaba." Uwani ta furta tana gimtse dariyarta.
"Wallahi komai zan ci gaba da yi idan na saɓa ki mini duk abin da za ki yi mini."
"Mu zamu tafi Baba sai mun sake zagayowa." Uwani na gama faɗar haka ta fara wata fuffuka tana gurnani sannan ta saɗaɗa ta bar wurin. Saboda yadda Aramma ya razana bayan da ya gama uzurinsa a duƙe ya dinga tafiya, saboda yadda ya ji ƙafafuwansa sun yi sanyi har sun gagara ɗaukar nauyin gangar jikinsa.
Ranar da aka yi sadakar uku dai tun da safe wasu daga cikin 'yan gaisuwa suka fara watsewa, domin dama wasu tamkar a kan ƙaya suke. Ita ma Uwani sai da aka yi sallar la'asar sannan Aramma ya zo ya sanar da Maryama an zo ɗaukan Uwani, ta so Uwani ta ƙara kwanaki amma babu yadda ta iya haka ta danne. Wasu daga cikin 'yan uwan mahaifiyarta sai tsokanarta suke suna amarya sai sun zo biki. Kafin Uwani ta fita sai da Maryama ta sata a gaba ta yi mata nasiha sosai.
Fakare Uwani ta yi tana sauraronta kamar nasihar na shigarta, sai gyaɗai kai take tana amsawa. Sai da ta gama sauraron mahaifiyarsa sannan ta ce. "Ni kam Inna don Allah zan faɗa miki wata magana amma don Allah kada ki faɗa wa kowa." Take gaban Maryama ya faɗi amma sai ta basar ta ce. "Ina jin ki babu wanda zai ji Uwanina." Duk abin da ya faru tun daga farko har ƙarshe ta sanar da ita tana dariya, ita kanta Maryama dariya take sheƙawa sanna ta riƙe baki ta furta. "Allah Ya shirye ki Uwani ni dai wallahi ban san halin wa kika ɗauka ba, mahaifinki dai har ya fi ni sauƙin kai. Allah Ya shirya ki ko ba komai kin samar mana 'yanci." Suna cikin haka suka ji ƙarar horn da sauri Uwani ta sungumi jakar kayanta, ta ɗauko hijabinta ta saka. Sai da ta yi wa mutanen gidan sallama da Aramma sannan ta ƙarasa bakin motar cikin murna, don tun daga nesa ta hango motar baba Mamman. Don haka da saurinta ta buɗe motar tana faɗin.
"Daddy wallahi na yi kewar Dada, ƙila ma ita tana can ko a jikin..." Kalamanta suka maƙale a maƙoshi sakamakon ido biyu da suka yi da Jafar. Wata uwar harara ya banka mata, ta yamutsa fuska tana ƙare masa kallo ta ce.
"To kai kuma ina motarka ka É—auko ta Daddy?" Jafar bai tanka mata ba ya fisgi motar da gudun gaske har sai da wasu yara suka matsa a guje.
Suna cikin tafiya babu wanda ya tanka wa wani sai Uwani ta fashe da dariya har da ƙyaƙyatawa, a fusace Jafar ya waigo ya zuba mata manyan idonsa. Sai kuwa Uwani ta sake kwashewa da dariya, gangara motar ya yi ya faka ya ɗauke kai gefe a daƙile ya ce. "Fice mini daga mota."
Uwani ta gimtse dariyarta sannan ta ce. "Kamar ya na sauka ai ba motarka ba ce."
"Uban me kike wa dariya?"
Uwani ta yi murmushi ta ce, "Wallahi dariya ka ba ni, ni dai ba baƙuwa ba ce a wurinka atoh. Kuma dai komai na ka Dada ta ba ni labari tun kana jariri har fa tunbiɗin da ka dinga yi kana yaro. Sai kuma na ga ka fafaki mota kana yin wani irin tuƙin 'yan Kaduna-Zaria, to wai ni birgar me za ka yi mini?" Jafar ya haɗiyi wani yawu mai ɗaci haɗe da fusgar da iska mai zafi, jin irin maganganun da Uwani ta faɗa masa. Yana shirin yin magana Uwani ta sake sakin wata dariyar tana faɗin.
"Kasan Allah yadda ka iya fafakar motar nan da Inuwan Toyota zai ganka tsaf zai É—auke ka kwandasta, saboda wataran idan ya gaji ya ba ka É—ani..."
"Fice mini a mota." Ya furta mata cikin tsawa.
"Wallahi ba zan fita ba ai motar Daddy ce, malam kada ka yi mini gori ni nan gaba ma jirgin sama zan tuƙa." Kalamanta na ƙarshe suka kusa ba shi dariya. 'Yarinyar da cikakkun sentence na hausa ma ba ta iya haɗawa ba ita ce za ta tuƙa jirgin sama.' Ya raya a ransa. Ganin za ta ɓata masa lokaci ya sa ya fisgi motar ya ci gaba da sharara gudu, har suka ƙarasa gida wani bai sake kula kowa ba.
Tun Jafar bai gama faka motar ba Uwani ta suri jakar kayanta ta ɓalle murfin motar ta fice a guje ko rufe motar ba ta tsaya yi ba, tun daga soro ta fara ƙwalla wa Dada kira tana washe baki. Mami da ta rako aminiyarta Hajiya Falmata ganin Uwani ya sake tado mata da wani malolon baƙin ciki.