← Book details Uwani Yar Kashin Gwuiwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 71

Sashe 25

Uwani Yar Kashin Gwuiwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Beb an ya zan iya jiran sati ukun nan masu zuwa kuwa? Kin ga yadda kika yi kyau." Salim ya furta cikin shauƙin soyayya, Shukra ba ƙaramin daɗi ta ji ba kin kissa ta ce.

"Well mu je mu zauna, ga 'yar aikin Mami za ta wanke maka mota."
"Za ta iya kuwa Baby? Na ga mata ba sa wankin mota." Salim ya faɗa yana bin Uwani da ke rakaɓe a gefe. Shukra ta dubi Uwani a tsawace ta ce. "Ke ba ki iya gaisuwa ba ne?" Jikin Uwani na rawa ta tsugunna ta gaishe da Salim, sannan Shukra ta ɗan yi murmushi ta furta.

"Ai in gaya maka daga motar Daddy har ta ya Jafar ita take wankewa za ka sha mamaki." Shukra da Salim suka wuce wurin wasu fararen kujeru, daga wurin da suke zauna suna iya hango Uwani da duk abin da take yi.

Sai da ta goge ƙwallar idonta sannan ta ɗauki bokiti ta fara ɗebo ruwa, da yake wurin ɗiban ruwan yana da ɗan nisa da wurin wankin motar a galabaice ta fara wankin motar har ta gama.

Gaban Shukra Uwani ta je ta tsaya ta ce, "Na gama wankewa." Shukra ta bi ta da harara sannan ta ce.
"Matso nan."
Ba musu Uwani ta matsa gaban Shukra, da ƙarfin tsiya ta fisgo Uwani har sai da ta bugu da ɗan ƙaramin table ɗin da ke gabansu ta ce.
"Don ubanki ke ba ki da ladabi ba za ki iya tsugunnawa ba?" Shukra ta ƙarasa maganar tana zuba wa Uwani ranƙwashi.

"Haba Beb da kin ƙyale ta kin san irin yaran nan ba wani tarbiyya suke samu ba, so don sun yi haka ni ba zan yi mamaki ba." Salim ya faɗa a ɗan ƙyamace yana duban Uwani da ta gama jiƙe wa da ruwa sharkaf.

"Dallah tashi ki ba ni wuri kina tafe da baƙi kamar na zunubi." Dariya sosai Salim ya yi jin abin da Shukra ta faɗa ya furta. "Wai yaushe kika koyi masifa ne love?"

"Haba ka rabu da ni na tsani yarinyar nan wallahi." Uwani na laɓe a ta bayan fulawiyin da ke zagaye da harabar gidan, takaici ya mamaye zuciyarta. Wani tunani ne ya faɗo mata don haka da sauri ta zagaya can bayan gidan, ta ɗebo irin manyan bokitan fentin nan guda biyu waɗanda ta gama wanki da su. Sai da ta yagi wata igiya ta haɗa hannuwansu ta ɗaure, sannan ta saki murmushin mugunta. Cikin sanɗa ta fara tafiya ta cikin fulawoyi, a daidai bayan su Shukra ta tsaya ta ji Salim yana faɗin.

"Haba ke dai Baby ba kya mantuwa, wannan fa mahaukacin ma shammatata kawai ya yi amma yadda nake ƙaunarki akwai abin da zan ga zai cutar da ke na gudu ban taimaki rayuwata ba, ke ce fa rayuwata ke ni fa idan za ki rayu da farinciki zan iya sadaukar da komai ciki kuwa har da numfashin da nake zuƙa." Shukra ta rangwaɗa kai cikin farinciki, tana shirin ba shi amsa Uwani ta saki murmushi duk da zazzaɓin da ke jikinta. Sai da ta daidaita saitin kansu sannan ta ɗaga bokitan fentin hannunta, ta kifa musu a kansu ta saka iya ƙarfinta ta danne saman ta yadda ba za su iya fisgewa ba. Salim da abin ya haɗe masa biyu ga zafin hula ga na bokiti ya ware murya cikin ihu ya ce. "Wayyo Allah wuyana!"

"Wayyo kaina, Baby kana ina!" Shukra ta faɗa a ɗimauce. Daga Salim har ita sai ɗaga hannuwa suke cikin neman taimako. Sai da Uwani ta ga sun fara galabaita sannan ta fisgo hannun bokitin ta baya, da yake ƙafafuwansu na ƙasan table ɗin da ke gabansu faɗuwar da za su yi ta baya sai suka taho da table ɗin da ƙafafuwansu. Uwani na ganin za su kai ƙasa ta yi saurin matsawa a guje, sai ji kake rugugum! kacacar kofuna da ruwan jarkar duka sun watso kansu. Ga bokiti ya sarƙafe su ga kuma ƙafafuwasu sarƙafe a cikin table, Uwani ta laɓe a cikin shukoki tana dariya ƙasa-ƙasa don duk ƙwaƙwar mutum ba zai gano da mutum ɓoye a wurin ba.

Da ƙyar Salim ya samu ya zaro ƙafarsa daga cikin Table, ya tashi zai zuba a guje Uwani da ke laɓe ta sake fisgo shi da yake igiyar tana hannunta. Daɓar Salim ya koma ya faɗi hankali a tashe ya ce. "Jama'a a taimaka mana wallahi jana ake yi."

Shukra ce ta yunƙura ta tashi a guje saboda tashin hankali ko yunƙurin cire bokitin ba ta yi ba, ita da Salim suka zuba a guje a daidai lokacin Jafar ya shigo harabar gidan. Turus ya yi ya ɗan fara ja da baya ganin ƙafafuwan mace da namiji suna tafe da bokiti a kai, da yake ba sa ganin gabansu yana ganin sun tunkaro shi ya zube takalmansa shi ma ya shige a guje yana ihun. "Wayyo Allah! Lado kana ina?" Jin ihun Jafar ya sake ruɗa su Salim, a wannan lokacin Lado ya zagayo da buta a hannu shi ma turus ya yi yana kallon ikon Allah. Da ƙyar Salim ya samu ya cire bokitin kansa, hular ta faɗi can gefe. Dama takalminsa na cikin ƙasan table ya jima da fita, iya ƙarfinsa ya tattara ya fita a guje yana faɗin, "Jama'a ku duba mini kaina idan yana gangar jikina." Sai a lokacin Lado ya gane shi, ya bi bayansa yana faɗin.

"Alhaji ka bar motarka." Lado na ƙarasawa bakin gate ko ƙurar Salim bai gani ba sai agogonsa da links ɗin hannun rigarsa da suka zube a wurin.

Littafin kuɗi ne 500 idan kina buƙata za ki turo ta Acc Aisha Adam 3090957579 Firstbank sai shaidar biya ta wannan lambar 07062062624 idan littafi ya kammala za ki turo 800
Free pgs ɗinmu ya kusa ƙarewa🫠

#Ummou Aslam Bint Adam🌚

*UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA*

©AMEERA ADAM

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye.

SHAFI NA SHA HUÆŠU

*BOJUWA HERBAL'S & SCENTS*
*Suna kawo Saiwowin da suke dagargaza sanyin mara da na jijiya.*
*Haka nan suna kawo Saiwowi daban daban daga Chad da Sudan, kuma marasa illah*
*Saiwowin tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza/tattabaru*
*Saiwowin matsi gangariya*
*Original gadalin mata*
*Ƴaƴan gadali na asali*
*Original gumba*
*Tsumin Saiwowi*
*Tsumin kwakwa da Dabino*
*Igiyar alkairi*
*Zumar goran tula*
*Hakkin daka na musamman na asali*
*Bayan haka suna dafa kazar amare da masu jego da ma uwayen gida*.
*Akwai bridal package*
*Mai jego package*
*Ƴar gata package*.
*Dukkan kayan kuma available ne for pickup or immediate delivery.*
*A Kano nake amma kuma nationwide delivery ne*
*Ku tuntubi Surayya Halin yau a wannan lambar dan samun naku cikin musulmin farashi*
*08032773332*
*Iyah Basiru na gaisuwa*😅

A sanyaye Lado ya ɗebo agogo da links ɗin Salim ya dawo cikin gidan, sai dai yana shiga ga wutar harabar wajen ta ɗauke. Ga kuma ƙarar duka da ake yi wa Shukra tana ihu, zuwa can kuma sai ya ji an yi wurgi da bokiti an zuba cikin gida a guje. Gudun kada abin da ya same su, shi ma ya zo kansa ya sa Lado ya shige ɗakinsa ya danno ƙofa ya rufe don shi kansa bai manta abin da aka yi masa a tsakar dare ba.

Da gudu Uwani ta bi bayan Shukra tana gurnani tana zabga mata igiyar a baya har Shukra ta fara kama ƙafar bene Uwani ba ta daina dukanta ba, tana hawa sai ga Shukra na rarrafe tana kuka saboda tashin hankali. Sai da ta ga Shukra ta shige sannan Uwani ta yi saurin ɗebe bokitan ta mayar da su wurin da suke, ta je ta ɗaga table ɗin ta mayar da ruwan jarkokin kai sannan ta koma ta kunna ƙwan fitilar harabar wurin ta wuce sashenta.

A lokacin da ta shiga sashenta shiru babu motsin Jafar, ta zube a kan kujera kanta na matsanancin ciwo kamar zai tsage gida biyu. Uwar ɗakinta ta wuce don ta sauya kayan jikinta saboda rawar ɗarin da take yi, ɗrower kayanta ta buɗe tana shirin miƙa hannu ta yi ido biyu da Jafar tsugunne a cikin.

Uwani ta basar kaman ba ta san abin da ya faru ba ta ce, "Kai kuma Ya Jafar mene ne haka?" Jafar ya fara wuri-wuri sannan ya ce.

"Wai Uwani ke ce kika zama biyu ko ya aka yi?" Jafar ya wurga mata tambaya.

"Wai me ka mayar da ni ne ya Jafar? Ni fa yanzu na gama yi wa saurayin Shukra wankin mota bayan na gama yi wa Mami wanki..." Cikin sauri ya katse ta.
"Wankin me? Ke kika wanke wa Salim mota? To su waye na gani da bokiti a kansu suna ihu?" Uwani ta wara hannu ta ce. "Ni kam ban sani ba, ƙila dai mutanen gidan ne suke son buɗe maka ido." Jafar ya yi fakare yana nazari, abu ɗaya ne ya fi tsaye masa a rai wai Uwani ce ta wanke wa Salim mota. A fili ta ji ya furta, "Dole sai na ɗauki mataki a kanta." Uwani ta yi saurin tambayarsa. "Wace ce?" Ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya furta. "Babu komai."

Saboda tsabar gajiya Uwani na sauya kaya ta É—auro alwalar Isha'i ta gabatar da sallah, a nan kan dadduma bacci ya yi awon gaba da ita.
A yadda ya ga tana sauke numfashi sama-sama ba ƙaramin tausayi ta ba shi ba, ya ƙarasa ya cire mata hijabin ya ji jikinta ya ɗauki zafi zau! Cikin jakarsa ya duba ya ɗauko Paracetamol, ya jima yana tashinta sannan ta tashi ya ba ta magani. Duk yadda ya yi da ta tashi ta ci abinci ƙi ya yi, ya rabu da ita ya haye gado ya kwanta.

Shukra da rarrafe ta ƙarasa falon Mami, babu ɗankwali ballantana mayafi ko takalmi, a razane Mami ta fara tambayar Shukra.

"Ke Shukra lafiyarki kuwa?"
Chapter 25 · 0% Book details