← Book details Uncle Ne Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 86 OF 87

Sashe 86

Uncle Ne Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A can Birnin nufar kam kullum sai Jabir ya ƙara kuyar da dukkan wanda ya amshi addinin Musulunci karatu kuma Allahamdulillah da yawan mutane sun amsa, Jabir ya fara soyayya shida matarsa hankali kwance,wannan sauyin da aka samu yasa uwa sundu ta shiga tashin hankali ga gari ya fara ƙyau shukoki sun fara fitowa,ruwan daya ƙafe duk sun dawo,da sauri ta nufi wani ɗaki domin ɗauko wani ƙahonta wanda tana busa shi wuta take fitowa ta jikinsa ta nufi wajan da akeso,tayi hakanne a son ta na halakar da Birnin baki ɗaya wanda suka goyi bayan ta kuma ta rabu da su wannan shi ne,tana zuwa ta ɗauko cikin hanzari tayi waje cikin rashin Sa'a ƙahon ya faɗi itama ta faɗi gefe guda,baki ta buɗe ta saki ihu sbd gatarin daya faɗo a bayanta, ihun da tayi ya sauka a cikin ƙahon wata iriyar wutace ta fita daga cikin ƙahon tayi sama bata tsaya ko ina ba sai jikin Uwa sundu cikin ƙaramin lokaci wutar ta ƙone komai na wajan,gaba ɗaya fadar Uwa sundu ta zama toka, birnin ya rikice wasu kuma tsoran Allah ya kamasu Uwa sundu da kanta ta kasa kare kanta bare su?gaba ɗaya suka cika fadar Papa aka basu musulunci. Duk Binciken Jalal kasu ganu komai yay abun ya fara damunsa gashi kullum ɓarnar ake masa,duk yadda yasu danne abinda yake damunsa sai da Mameey ta fahimta tambayar duniya tace masa babu komai,yana shiga part ɗinsa ya samu Jalilerh na kwance a saman bed tana bacci wanka yay sosai ya shirya cikin wasu English dressing sleep ya ƙara kyau da fari da kuma ƙiba sosai yake samun nutsuwa wajan matarsa duk da kullum sai tayi masa kuka ga zazzaɓin, kwanciya yay kusa da ita yana jawota jikinsa tare da zare ƴar rigar baccin buɗe ido tayi tana ganinsa ta ƙara shigewa jikinsa tana sakin ajjiyar zuciya,kanta ya shafa yace "sorry Wify babyna ke wahalar dako?" Kallonsa tayi domin bata fahimci komai yace "Yeah! Nasan nayi ajjiya ai,kuma ita ta fara aiki nanta 9months am going to be father WOW! Can you imagine" lafewa ta ƙara yi ajikinsa tana shafa ƙirjinsa,daga nan kuma ya fara juyata ganin zatai masa kuka kuma yasan ba lafiya gareta ba yasa ya rungome ta ya shiga tofa masu addu'a har bacci ya ɗauke su. A Ranar da aka ɗauki azumi na farko Lamir yazu amma aka hana shi shiga surutai ya farayi yana faɗin shine ya haukata shine yay mata gaza,a haka harya nufi Babban titi cikin rashin Sa'a wata ƙatuwar mota tayi gaba da shi nan take ƙafarsa guda ɗaya ta fita,ana zuwa dashi asibiti ya fara ihu yana cirar gashin gabansa yana ci,ganin hakan yasa suka nufi dawanau dashi domin hauka yake sosai. Ranar da akai sati ga azumi Jalal na office ɗinsa yana duba wasu takardu masu amfani,jin kiran Asr yasa ya miƙe cike da nutsuwa ya shiga bathroom yin alwala yana fitowa yaga babu takardun dafe kansa yay yana kiran sunan Allah gaba ɗaya ya rasa me ke shirin faruwa dashi gashi har anfara yi masa surutai, Jafar ya kira yace "where are you?" Jafar yace "ina gida vanay jin daɗin ne" Jalal yace "i want to see you now idan ba damuwa" Jafar yace "ok I'll try my best ganin cewa nazu but zazzaɓi nake olser na ya tashi kasan azumi"daga nan sukai sallama,kasa zuwa Masjid yay sai a office ɗin yay sallar Jafar ne yay sallama ya shigo cikin parlour'n da ƙyar Jalal ya amsa ganin Jalal cikin damuwa yasa Jafar faɗin "ur excellence is anything happen ?" Numfashi Jalal ya sauke yace "kawai na gaji da aiki shine nace ko zaka tayani" tsaki yaja yace "kai amma dai ka rai nan hankali dana san wanne wlh ban zuwa" miƙewa tsaye Jalal yay yace "I'm coming" yana faɗin hakan ya shige cikin wani bedroom,da sauri Jafar ya miƙe tare da fara duba tarin takardun wajan wata paper ta kwangilar 20.5m ya gani da sauri ya ɗauka tare da ɗaukan abu ya buga stem ya juya zai sanya paper a cikin aljihu yaji Jalal yace "i knew Jafar,Nasan you're the one da kake min haka,kawai ina son na tabbatar ne kuma thank God na gani da idona,why Jafar? Why? Me nai maka har haka da kake neman daƙusar dani?" Wani kallo Jafar yaywa Jalal kafin yace "wlh na tsaneka Jalal,ban taɓa ganin abinda na tsana sama dakai ba,ka kwace komai nawa dukkan abinda nayi niyyar yi a raina saika rigani firtawa, duk sanda na ganka ina jin kamar na saka wuƙa na yanka kona harbeka" idanun Jalal ne ya sauya kala yay jaaa yama rasa mema zaifi,how long Jafar ya ɗauka yana cutar da shi? Mene yay masa? Cikin sanyin murya Jalal yace "me nai maka?" Dariya Jafar yay yace "me kake min kake tambaya? Tun a Paris ka fara cutar da zuciyata yarinyar da nakeso taƙi ni sbd soyayar da take maka,gaba ɗaya students da lectures basu da magana sai na Muhammad Jalal Kabeer bobo,naga kai scholarship ma aka ɗauke kuma ni da kuɗin uba naje makarantar,amma komai sai ace bobo....," Ƙwafa yayi yace "na shirya fitowa takarar shugaban ɗalibai a Paris ka rigani,a zahiri nabi bayanka amma ta ƙarƙashin ƙasa nake cin dunduniyyarka,nan ma dai banyi Sa'a ba duk exam kana fita da good results amma banda ni,daga nan na yanke shawarar zama Governor a Ibadan idan mun dawo,ƙwatsam naji wai ka fito takara,dukkan abinda kake tunanin Mubarak Yahya cibo ya akaita maka nine sanadi na nake sashi komai,kuma nina sashi ya kashe ƴarsa ta cikinsa sbd gudun matsala,na huce dukkan yadda kake tunani Malam au ur excellence,ni mugune ina da wayo kai kuma baka dashi miskilanci ka yay min daɗi ina gudanar da abinda na keso cikin sauƙi, Mubarak Yahya cibo ya shirya tuzarta rayuwarka ta hanyar yi maka asiri ka dinga bin mata,sai dai shima ya makara sbd na riga shi ƙudirin haka,ka tuna sanda nazu da safe kana bacci nace wajan Abbou nazu? Ko ɗaya ba Wannan ya kawoni ba nazu domin cimma burina na zuba maka gani a inda kake kwance,shima Mubarak cibo wawa ne domin na sanya matarsa ɗauke maganin yanzu haka kafin ya bawa Lamir ya saka maka,ita kuma ta barbaɗa masa maganin a wajan barcinsa,yanzu haka yana can yana bin mata shi,abin baƙin cikin daka kaƙi lalata Jalilerh domin nasu ka lalata yadda abin zai min daɗi,rashin samun baby matsayin mata bai taɓa damuna ba saboda ba son Allah nake mata,sai na AURETA nai mata filla-filla sannan zan saketa a ranar,to yanzu Muhammad Jalal bobo wakake tunanin zai taimake ka?idan kasan halina wasu sun sani? Ko kuma kana da shaidar kamani a hannunka" And...," Bai ƙarasa magana yaji an daki kansa da ƙasan gun,da sauri wasu sojoji suka fara shigowa sai da suka cika office ɗin yadda wani saurayi, murmushi Jalal yay yana ɗan lumshe idanunsa kafin ya kalli Jafar yace "now is my turn to talk malam Jafar,tunaninka Jalal bobo shasha ne? tunanin bobo bai san makashinsa ba?to tabbas kayi kuskuren na daɗe da sanin dawa nake tare since before,Duk Wannan bai daman ba sai ɗauke JALILERH da kasa akai na fahimci haka a lokacin da Hibba ta kirani FRIST sunanka ta fara kira daga nan nai saurin kashe wayar bawai ita ta kashe ba kuma nayi hakan ne sbd kada kaji abinda take faɗa,kuma sosai na fahimci tashin hankali a fuskarka,kasa Aryan ya ɗauki photona da JALILERH dalilin hakan nai restore ɗin wayarsa amma sai da na ɗauke komai na kan wayar, shi bashi da tunanin da zai fahimci komai,abu na gaba kai ne kasa aka yaɗa cewa mahaifiyata mahaukaciya ce,kuma kai ne mutum na farko daya faɗa min haka,ina da bambanci dakai,kai kana da gaggawa ni kuma a hankali nake bin komai,Nasan cewa sa hannun da ake kai ne kake yinsa domin na tuna sanda kace sa hannuna hana birgeka harna koya maka.." ajjiyar zuciya ya sauke yana juya girgiza kansa tare da fesar da numfashi,matashin saurayin ya kalla yace "bani wayar"da sauri ya bashi kai tsaye vedio ya shiga har yanzu vedio'n da sukaiwa JALILERH ha Jafar can a gefe tana ganinsa tayi saurin cewa "yaya Jafar.." da sauri kuma ya koma ya ɓuya,nuna masa vedio'n yayi yace "akan wannan vedio'n aka kashe mutum ko?to kuma gashi abinda kuke gudu ya faru, wannan ya sace wayar ganin abu mai muhimmanci ya nemi tare nuna min komai,tun a lokacin na ƙara sanya idanuna a kanka,ka shirya min dinner na murnar zaɓe na gefe guda kuma ka shirya a harbeni, Wannan dalilin yasa nace bana zuwa, baƙin cikin hakan kai kuma ko gidanmu baka dawo ba ka nufi gida,to yahhhh? Ya kaga salon takun nawa kaje ka ƙara ilimi na zama da mutane"yana faɗin hakan ya cire abun recording ɗin da yay na all maganar da Jafar ya faɗa ɗazo ya bawa sojojin kana ya kalli Jafar yace "Hausawa sunyi gsky da sukace makashinka yana tare da kai,yanzu na tabbatar ba kowa zaka iya yarda da shi ba, tunda wanda ka ɗauka matsayin amini yay maka haka bare wani,kaje ka girbi abunda ka shuka zaka samu abokan naka Mubarak Yahya cibo da Faisal Lawan a gidan yari"yana faɗin hakan ya shige cikin bedroom hana sauke numfashi bai taɓa jin zafin abota irin ta yau ba,yasu Jafar har ransa Amma gashi shi ne yake cin dudduniyyarsa. A shirin ga azumi ya ɗauki Matarsa zuwa umara yabar ƙasar baki ɗaya.
Chapter 86 · 0% Book details