← Book details Uncle Ne Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 62 OF 87

Sashe 62

Uncle Ne Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

yace "Allahamdulillah"zata ƙara magana Mameey tace "leave" komawa tayi da tray ɗin lemon tana tafe tana juyawa,bayan yasha ruwan da Mameey ta bashi ya miƙe tsaye zai fita Mameey tace "koma ka zauna i want talk to you Muhammad" zama yay yana ɗura idanunsa akan Mameey,itama kallonsa tayi tace "mene ra'ayinka akan baby?" With much surprise ya dinga kallonta kafin ta ɗura da faɗin "nasan baka da niyyar aure yanzu,amma yanayin da kake jiki auren shine mafita,kuma kasan idanun jama'a akan ka suke dole ne ka ajjiye iyali ka fara mulkarsu kafin ka mulki jama'ar gari,ban san yaya matsayin baby yake a ranka ba,kana sonta da aure ko akasin haka? duk yadda yake a ranka inma kallon sister kake mata ko baka da feelings a kanta,ya zama dole ka dinga sanya sonta da son kasancewa da ita a cikin zcyarka,nasan bata da wata damuwa komai aka zartai zata amsa,amma ga namiji auren macen da bai so matsala ne,duk da cewa ina da tabbacin ba zaka taɓa yin wani abu da zai cuci Nihila ba,amma rayuwar aure da kuma zamantakewarsa daban yake,dole yadda kuke ada ba haka zaku kasance ba,anawa tunanin ya kamata ka fara jin ta bakinta ma'ana ka fara keɓewa da ita"ware idanunsa wanda suke a rufe yay kafin ya cije lips ɗinsa yace "what about Jafar?" Shiru Mameey itama tayi kafin ta miƙe tace "don't worry about him, Abbou Jalal zai masa magana ok" tana faɗin hakan ta miƙe tsaye tare da ɗaukan tray ɗin tai gaba da kallo kawai ya bita,kafin ya sauke wasu tagwayen ajjiyar zuciya. Bayan sallar issha'i Jafar yay parking da motarsa kana ya nufi cikin gida,a main parlour ya samu Mameey sai kuma Mama zama yay kansa a ƙasa ya gaishesu kana ya ƙara yi masu ta'aziyya,satar kallon Nihila yay sai kuma ya ɗauke kansa, miƙewa Mameey tayi tace "bari nasa Laure ta kawo maka ruwa"bai ce komai ba sai Murmushi da yayi, Nihila ce tace "Yaya Jafar ina yini?" Murmushi yay wanda yake nuna zallar jin daɗi yace "bana amsawa" idanunta ta ɗauke daga kan littafin da take dubawa tace "why?" Shima ya kwaikwayi muryarta yace "why?" Salati yaji an zabga da sauri ya juya sbd a tunaninsa tuni Mama tabar parlour'n tsaye ya ganta tana tafa hannu tace "huuuu³ yaushe ka zama sallamamme bani da labari,a'a Wlh wannan halin banza ne,ina ruwanka dayin Muryar mace? Banda neman magana, yuuuu ko daudo zaka koma ne bana da labari Jafaru? a'a wlh wannan gantalewa ce yaya ina ya bonka sallah zaka kasa alwala?" Ɓata fuska yay yace "to ina ruwanki ne?" Haɓa ta riƙe tace "Mahadurrasulillah zagina zakai? Daga faɗin gsky sai cin mutunci ya biyo baya? To Allah ya baka hqr tunda ka zama gantalalle" shi dai baice komai ba harta gama surutanta tai gaba,tana barin parlour'n ya koma kusa da Nihila yace "me kike ne?" Idanunta akan littafi tace "study" jinjina kai yay yace "ok you can continue my wife to be soon in sha Allah" ɗago kai tayi ta kallesa suka haɗa ido kasa ɗauke idanunta tayi sbd gabanta daya faɗi taba rasa mene za tace masa,tarin da sukaji yasa gaba ɗaya suka dawo cikin nutsuwarsu,bobo ya fito daga shi sai 3gauter da farar singlet kai tsaye kitchen ya nufa ko inda suke bai kalla ba, duk da cewa shida Jalal abokai ne amma hakan bai hana yaji wata kunyarsa ta kama sa ba,dalilin haka yasa ya miƙe da sauri ya ɗauki key ɗin motarsa yace da Nihila "goodnight wify,luv u Soo much" yana faɗin hakan ya fice daga cikin gidan ya nufi waje,bobo na shiga kitchen yaga da aƙwai ruwan zafi a flast tea ya haɗa a mug ya zuba milk da bonvita da obalti,sai suger guda uku, spoon yasa ya juya tea ɗin, yana kitchen ɗin zaune saman stool kasan cewar ta kashe wutar kitchen ɗin yasa ba kowa zai san yana ciki ba, tun daga bakin ƙofa ya hango ta tana tafiya a hankali kamar wacce ƙwai ya fashewa a ciki,tana tafe hannunta a mararta wacce tun safe take mata ciwo, idanu ta fara rarraba wa sbd duhun data gani a kitchen ɗin, ƙarasa shiga ciki tayi ta nufi inda makunnin ƙwan yake,tsayawa tai cak a tsakiyar kitchen ɗin sbd wani murɗawa da marta tai har sai da ta saki ƙara ta durƙoshe a wajan ta fara kuka,sbd Allah yana gani ciwon ya fara cin ƙarfinta,ga wani amai dake taso mata haɗe da ciwon kai zazzaɓi duk lokaci guda,duk abinda take a kan idanunsa yana zaune yana shan tea hankali ƙwance time to time yana lumshe idanunsa,amma idanunsa ko mutsawa basayi a kanta, lokaci ɗaya kuma ya fahimci abinda ke damunta,ganin bata da niyyar miƙewa ga kukan dake cin ƙarfinta,yasa ya sakko daga saman stool tare da ajjiye cup ɗin wajan sink,kai tsaye wajanta ya nufa yana tafe a hankali sbd bai son taka wani abu ko taka hannunta sbd ba sosai yake ganin komai na kitchen ɗin ba,a haka harya ƙarasa zuwa inda take,fesar da numfashi yay tare da sunkuyawa yasa duk hannayensa biyun ya ɗagota sosai ta tsorata zata saki ihu yay saurin saka hannu ya toshe mata baki, tura ta ya dingayi har zuwa jikin bango kafin ya haɗata da jikin bangon ya ɗan ranƙwafo dai-dai fuskarta yana leƙawa, bakinta kawai yake iya gani suma dalilin jan da sukai ga kuma hawaye da yawon da suka jiƙasa,ita dai Jalilerh sai leƙa fuskarsa take amma ta kasa ganin ko waye sbd duhu ga kuma wani a zaɓaɓɓen ciwo dake cinta hakan yasa ta ƙara sakin wani kukan tana zabewa zata faɗi yay saurin haɗata da jikinsa a tare suka sauke ajjiyar zcya mai ƙarfi,da sauri Nihila wacce take bakin kitchen ɗin ta juya idanunta cike da hawaye,shiru gaba ɗaya sukai sai Jalilerh dake sauke ajjiyar zcy,a hankali kuma ya dinga bubbuga bayanta yana shafa ƙwantaccen gashin kanta,a hankali kuma ta dingani ciwon na sauka sai wani gumi daya dinga sakko mata, idanunsa ya sauke a red lips ɗinsa kafin a hankali kuma ya ƙarasa kusanta bakinsa da nata ya ɗan lumshe idanunsa cikin ɗaukewar numfashi ya sauke lips ɗinsa saman nata kafin ya bata wani special hurt kiss a gefen lips ɗinta,kana ya juya da sauri yabar kitchen ɗin,yana fita ya samu Aryan a parlour ko kallansa bai ba ya ƙarasa shigewa part ɗinta, Aryan kuma kitchen ɗin ya shiga yana shiga yaji bugi abu da sauri kuma yasa hannu ya kunna hasken kitchen ɗin,tsaye ya ganta kanta a ƙasa, ƙarasawa yay inda take tsayen tare da leƙa fuskarta ganin hawaye ƙwance saman fuskarta yasa shi faɗin "Hubby...!!"saurin ɗago kai tayi yayinda zcyarta ta buga da ƙarfi,zallar tsoro ya bai yana a Zcyarta tunaninta shine badai Aryan shine ya rungome ta ba?to idan ba shi bane waye? Tabbas shine tunda gashi taji muryarsa kuma shi ta gani tsaye,to mene yake cikin kitchen ɗin?ganin tai shiru tana kallonsa yasa yace "what wrong?" Nan ma shiru tai masa hannu ya miƙa zai riƙe ta tayi sauri matsawa baya tana girgiza kanta,kallon fararan kayan baccin dake jikinta yay sai kuma ya ɗauke kai tace "You are Staired" da sauri ta kalli jikin ta sai kuma tai waje da gudu bayanta yabi da kallo yana sauke ɓoyayyiyar ajjiyar zuciya. washegari kamar yadda aka buƙata Jalal ya shirya cikin wata jumper mai shegen ƙyau maroon color ya saka babbar rigar,sai Black hula da black covert shoe,hannunsa ya ɗaura agogon gucci ga farin bluetooth daya saka,da sauri ya ƙarasa fesa parfume ɗin hannunsa,kana ya ɗauki wayoyinsa ya riƙe,fita yay yana fita ya zamu Mameey ita ɗaya a main parlour kowa ya tafi wajan aiki dake Monday ce, Nihila kuma na makaranta Jalilerh na ɗaki tana bacci sbd bata jin daɗi, Abbou yana wajan masu karɓar gaisuwar da suka zo masa,kallon Mameey yay yace "Mameey I'm going,a gyaran part ɗina before I'm coming back" murmushin jin daɗi tayi ganin yay fesa kamar ango sai zabga ƙamshi yake,ga wata cikar zati haiba kwarjini daya ƙara fitowa saman fuskarsa,tace "in sha Allah, Allah ya tsare ya kiyaye" da Ameen ya amsa kana yay waje,yana fita securities suka rufa masa baya,wata lafiyayyiyar mota aka buɗe masa back seat ya zauna kana driver ya shiga,su kuma su shiga taso motar guda biyu,suka saka motar Jalal a tsakiya a hankali motocin suka fara barin gidan,da yammacin ranar Mubarak Yahya cibo ne zaune a gaban boka Saƙib yana sauraran abinda yake faɗa,boka Saƙib yaci gaba da faɗin "kayi kuskure domin abinda mukace ka aikata bashi kai ba,dole ne ka samu matsala akan zaɓen ka,dole ne kujerar tai rawa,kaci Sa'a kazo da wuri banda haka da bazan iya komai akai ba"da sauri Mubarak Yahya cibo yace "Ni dai burina kawai bai huce na Jalal a ƙasa ba, farin ciki na shi ne dukkan abinda ya sawa hannu a harkar mulkinsa ace ya lalace abun bai albarka ba,ai tasa masa ɓarnar kuɗi,idan har zai yiwu ma kawai a sa ya zama Mazinaci..
Chapter 62 · 0% Book details