Sashe 61
Uncle Ne Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gaba ɗaya suka haɗu saman daining sbd gaba ɗaya ɗayansu babu wanda yay breakfast,baka jin komai sai ƙarar spoon,fork, and knives, Mameey tuni ta koma ɓangaren masu zuwa gaisuwa tana zuwa ta samu Mama zaune tana jan casbawa sai kuma Hajiya Atine mahaifiyar Nusaibat da kuma wasu mata da suka zo daga maƙota,itama dai Mameey danginta suna hanya gasancewar ba ƴar nan bace ita can cameron county take da zama shiya ba koda yaushe familynta suke zuwa ba, wayoyin Jalal Abbou ya kwasa ya nufi side ɗin samarin yaran nasa yana zuwa ya shiga part ɗin Jalal, ƙwance ya samesa saman 3seater daga shi sai 3gauter da farar singlet wacce ta kamasa ya ƙure a.c sam baya iya zama babu sanyi ya sama da Paris su da kullum suke cikin yayyafin ƙanƙara, idanunsa a lumshe kamar mai bacci ganin yana bacci yasa Abbou ajjiye masa wayoyinsa a kusa dashi kana ya gyara masa ƙafarsa data lanƙwashe,samun kansa yay da shiga bedroom ɗin Jalal yana shiga ya dinga bin ko ina da kallo,har idanunsa ya tsaya akan photon Jalilerh wanda ya manna,cikin ransa yake faɗin "yanzu lokacin yayi da gaba ɗaya zaku hqr da juna, Jalal ya zauna da Nihila da kuma wacce na aura masa, Aryan ya zauna da Jalilerh matsayin matarsa, Jafar kuma zan masa bayanin komai yadda zai fahimta daga nan ya nemo wata,su Irfan ma duk su nemo mata a haɗa ai auran lokaci guda kowa ya huta"da wanan tunanin yasa hannu ya cire photon Jalilerh ya saka cikin aljihun wandonsa kana ya fice daga ɗakin,yana fita Jalal ya buɗe idanunsa yabi bayan Abbou da kallo,wyarsa ya ɗauka na yaga kira sama da 50 hadda hukumar INEC da kuma gidan gwamnati sai kuma different numbers sai kuma DM shima babu a dadi, wani message ya gani kai tsaye ya shiga ciki yana shiga ya fara karantawa kamar haka _Assalamu alaika ur excellence hukumar INEC na tayaka murna da samun damar dakai na zama Gwamnan jihar Ibadan congratulations once again yallaɓai, za'a rantsar dakai a ranar 29 ga wanann watan kafin nan kana da meeting a gidan gwamnati by tomorrow morning I have a nice day sir_ _~from~ RETURNING OFFICER_ Yana gama karantawa ya saki wani lafiyayyan murmushi wanda ya sanya dimples ɗinsa suka loma,gadai mulki ya samu kamar yadda yake buƙata kuma yadda yake cikin burinsa amma mai yasa baya cikin farin ciki ne gaba ɗaya? Mai yasa ya keji gabansa na faɗuwa? Mai yasa zucyarsa take ciki da zullumi da kuma faɗuwar?" Runtsa idanunsa yay yana ƙara jin ransa nai masa suya ƙirjinsa ya kalla nan yaga sunan raɗau kamar yadda yake ko yashe yankan na warkewa sunan na ƙara fitowa,shafar sunan yay kana ya lumshe idanunsa tunawa da Aryan da yay yasa yaja tsaki,wani DM ɗin ne ya ƙara shigowa wannan kuma na ta'aziyya ne da ake ta turo masa tun jiya, lumshe idanunsa yay babu jimawa bacci ya ɗauke sa yama manta da Lokaci domin time ɗin sallar zuhur ya kusa haka ya fara bacci wanda yinsa kawai yake ba dan daɗi ba,Aryan bai dawo da Jalilerh gida ba sai wajan asr prayer wasu masjid ɗin ma alrdy sun idar, parking yay a harabar gidan yana parking ya hangi Alhaji khamal tsaye yana latsa waya, fitowa yay daga cikin motar itama Jalilerh ta fito tana lumshe idanu sbd baccin da ta keji ga jikinta babu daɗi rabonta da wanka tun jiyan,ga wata yunwa dake damunta,bata tsaya sauraran maganar Aryan wacce yake cewa "kada ki faɗawa ko ina mukaji, kawai motarmu ya samu matsala"bata kulasa ba ta shige gida,babu kowa a main parlour da sauri da haura upstairs, Aryan ya nufi ciki da sauri Alhaji khamal ya tsayar dashi yana tsaya yace "ina wuni?" Yace "lfy, Allhamdulillah kiramin Abbou'nnaka" Aryan yace "ok" ciki ya shiga yana shiga ya nufi upstairs,sakin labulan window'n Jalal yay ta saman upstairs bayan ya gama ganin shigowar su cikin gida, dwonstrais ya nufa a hanya yaci karo da Jalilerh bai ko kallo inda take ba ya shige ta tsaye tana kallonsa,haka Aryan ma,yana sauka ya nufi lambun gidan wata farar kujera yaja kusa da ƙaramar dake wakana a wajan,shiru yay tare da tsorawa ruwan dake gabansa idanu,bai taɓa sanin nada daɗi ba sai yau,da Mummy na nan bazai taɓa kawowa iyanzu bai kai komai cikinsa ba, baya yay tare da kwanciya jikinsa kujerar yana fesar da numfashi, shi Mulkin nan tun ba'a je ko ina ba ya fara damunsa kira kota ina tun kafin ma ya fara shiga office,a hankali Aryan ya tura ƙofar ɗakin tare dayin sallama cikin zcy Abbou ya amsa,yana zaune saman duguwar kujera yana operating system sai coffee dake gabansa dan ya kasa kai komai cikinsa, Aryan ne ya zube gabansa yace "am so sorry Abbou Wlh....,? Dagatar dashi Abbou yay yace "idan wanan ya kawo ka get out of my room,ka riga ka nuna ban isa da kai ba" girgiza kai Aryan yay yace "Wlh Abbou..,"tsawa ya daka masa tace "nace idan wannan maganar ya kawoka ka fice min daga nan tun ranka mai ɓaci Aryan" tsoro yaji sbd Abbou bai taɓa matsa tsawa irin wanann ba miƙewa yay har yaje ƙofa sai kuma ya tsaya yace "Abban Nusaibat na kiraka a compound" yana faɗin haka ya fita waje yana jin ransa babu daɗi, miƙewa Abbou yay ko coffee ya kasa sha,dake a shirye yake tsaf wayarsa kawai ya ɗauka yay waje,yana sauka dwonstrais ya haɗu da Mameey hannunta riƙe da babban tray zatai waje kallonta yay yace "sai ina?" Tace "lambu wajan Bobo tun da suka dawo bai ci komai ba" da sauri ya kalleta sai kuma kawai ya ɗauke kansa ya nufi wajen shima,gaisawa sukai da Alhaji khamal,numfasawa Alhaji khamal yay yace "ni mai laifi ne gareka Alhaji Kabeeru ban san da yaushe na aikata hakan ba,ban san kuma sanda zai daina baka hqr da nai manyan ya fiyarka,dan Allah Alhaji Kabeeru kayi....,"cikin takaici da kuma zallar damuwa ya kalli Alhaji khamal sai kuma ya saki Murmushi yana gyara tsaiwa kafin ya sanya idanunsa cikin na Alhaji khamal yace... *NIMCYLUV* 7/11/21, 8:44 PM - Buhainat: UCL NE End book 2 _90-91_ "Me yasa kake damun kanka Alhaji khamal?na gaya maka komai ya huce kuma yanci gaba da riƙe Nihila as my daughter"kallonsa kawai Alhaji khamal kafin yace "ina jin kamar ban zame maka amini na gari ba,na cuceka cutar da bai dace amini yaywa amininsa ba,na cuci kaina na cuci baby,dan Allah dan Annabi kayi hqr ka yafemin Wlh bana jin daɗi zcyta babu daɗi,gani nake kamar kana riƙe dani kana jin haushina kamar kana gaba dani" ya faɗa idanunsa cike da hawaye, girgiza kai Abbou yay yace "kada ka damu gareni komai ya huce komai da sanadinsa Allah ya rufa mana asiri baki ɗaya" da Ameen Alhaji khamal ya amsa jiki kuma a sanyaye ya ƙara yiwa Abbou gaisuwa kana ya bar gida zcyarsa babu daɗi,shima Abbou juyawa yay ya shige cikin gida kai tsaye upstairs, Mameey na shiga lambun ta hangesa can kusa da ƙorama ya zura ƙafafunsa ciki yana ɗan wasa da ruwan yayinda idanunsa suke kallon cikin ruwan amma a zahirance bawai ruwan yake kalla ba, tunaninsa yana can wani wajan daban, ƙarasawa wajansa tayi tare dajan wata kujerar ta zauna,bayan ta zauna da kallesa sosai taga gaba ɗaya hankalinsa yana ga wani waje domin ko zuwanta wajan bai sani ba,hannu tasa ta taɓosa da ɗan sauri ya sauke ajjiyar zcy tare da juyawa sbd yasan shi ɗaya ne a wajan,ganin Mameey yasa ya ɗan saki murmushin gefen baki,kallonsa kawai Mameey tayi kafin tace "meyasa zaka zauna kai ɗaya?"shiru kawai yay mata baice komai ba, Mameey tace "ina lura dakai tun safe ba kaci komai ba,anya zama zai yiwu babu cin abinci?ai saka ɗaurawa kanka wani ciwon nada ban kuma,ohhyaa ga abinci" kallonta yay ya kalli abincin kamar bazai magana ba sai kuma yace "i lost my appetite" Mameey tace "ayaa,dole haka zaka daure kaci ko babu yawa ko kuma a matse maka lemon kasha za kaji dai-dai" baice komai ba ganin ta ɗauki wayarta can kuma ta kara wayar a kunne tace "baby matsewa bobo lemon guda 10 a cup ki ɗan saka suger half spoon" Nihila dake zaune tana kallon Jalilerh wacce take ƙwance tai lamo saman bed ta rungome pillow tana sauke ajjiyar zcy tace "ok Mameey,part ɗinsa za'a kai masa?" Mameey tace "no yana lambu" tana faɗin haka tai rejecting call ɗin, Jalal ne ya fesar da numfashi yace "Mameey bana shan lemon" da mmki Mameey tace "yaushe hakan ya faro,bayan kowa yasan kana sha"lumshe idanunsa kawai yay yace "kawai na daina" gyara zama Mameey tayi cikin serious magana tace" ina tunanin zan maye maka gurbin Oum Jalal,ina tunanin zan baka farin ciki irin wanda kake samu wajan Oum Jalal,amma naga kamar baka nema daga waje na, Muhammad tunda nake da mahaifiyarka Zulfa musu bai taɓa haɗani da ita ba,kusan zan iya cewa nafi kowa baƙin cikin abinda ya faru,Wlh tllh ni kallon su Irfan nake maka gani nake kaima nina haifeka,bana ganin wani banbanci tsakani,dan Allah nima kayi min kallon uwa,bawai ka gayan damuwarka ba domin nasan wannan halittar ka ce ba kowa yake sanin abinda ke ranka ba,amma ko yaya ne ka dinga sharing damuwarka dani in sha Allah zan zame maka madadin abinda ka rasa"ta ƙare maganar tana buɗe wasu warmers,kafin ta buɗe yay saurin riƙe hannunta yana ɗan kwaɓe fuska yace "noo please Mameey, coffee kawai" bata kallesa ba itama tace "eat something than sai kasha coffee ɗin" shiru yay mata harta gama zuba masa Chucus plantain wanda yaji nama, aƙwai kana ta sanya masa spoon ta ɗora masa a cinya tace "eat" bai son musu da ita hakan yasa ya ɗauka ya fara sanyawa cikin bakinsa kamar bai so, yadda yake taunawa kawai zai nuna maka ba daɗin abincin ya keji ba,a haka ya samu yaci rabi kana ya ture plate ɗin, kallonsa tayi tace "meye wannan?" Cikin ƙasa da murya yace "Mameey I'm full" kafin tai magana Nihila ta ƙarasu wajan hannunta riƙe da ƙaramin tray ta ɗura cup a samansa, durƙusawa tayi idanunta akan bobo tace Mameey gashi, girgiza kai Mameey tayi tace "no baida kawai" Nihila ta kalli bobo tace "bobo ya jikin?"idanunsa akan ruwan dake kwaranya