← Book details Uncle Ne Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 87

Sashe 59

Uncle Ne Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Shuru tayi ta shiga sauke ajjiyar zcy tare da ƙare shigewa jikinsa,sosai waƙar tai mata daɗi Musamman kalaman cikinta,jin yay shuru yasa ta ɗago kanta da sauri ta rufe idanunta sbd haɗa ido da sukai dashi, ɗauke kai yana kallon agogo yaga remain 10minutes pass 10,can kuma yace "nayi kuka kinji ko?"kaita gyaɗa masa alamar eh,jinjina kai yay yace "good,da wasa kada ki sake wani yaji cewa nai kuka kin gane" saurin kallonsa tai to ita wa zata gayawa? Dawa take surutu da Mummy kawai take shira sai shi idan yay niyyar magana amma a haka har yake tunanin kada ta faɗawa wani,gira ya ɗaga mata sauri ɗauke kai tayi cire ta yay a jikinsa yace "oyaa look at me,ina son tambayearki" gyara zamanta tayi kanta a ƙasa ta fara wasa da yatsun hannunta domin sam bata jin zata iya haɗa idanu dashi bare har ta tsaya kallon cikin idanunsa, idanunsa a kanta kamar bazai magana ba sai kuma yace "Waye Uncle ɗin da kika faɗa ɗazo?" Cikin ƙaramar muryarta mai cike da ƙuruciya tace "Mom ta cemin kada na faɗawa kowa,amma bana jin zan iya ƙin gaya maka, Abba na ne amma Mummy ta ce min na dinga cewa Uncle" jinjina kai yay yace "to meyasa ya barki har wannan muta nan suke binki?" Shuru tayi na wani lokaci kafin tace "A ranar baya cikin birnin yaje meeting, ƙilan yama manta cewa ranar ce da ake haɗa samari da ƴan mata"taɓe bakinsa yay kana yaja baya ya jingina da jikin gadon kana ya lumshe idanunsa kamar mai bacci, shuru itama tayi tare da ƙurawa fuskarsa idanu kamar daga sama taji yace "Wace Ammi last time da naji kinyi maganarta?"shiru kawai tai masa domin ba zata iya faɗa masa matsayinta a wajanta,tabbas Ammi jigoce gareta duk da cewa bawai tana fahimtar komai bane amma sosai ta kejinta har cikin ransa da jinin jikinta, wasu hawaye ne suka shiga zubuwa daga cikin idanunta ta kasa ce masa komai, kallonta kawai shima yay kafin ya taɓe baki ya janye idanunsa daga kanta,sai tai kuka dan kanta ta hqr baice mata komai ba,ganin ta sauka daga kan bed yasa ya juya harya buɗe baki zai magana sai kuma yay shiru, sauka tayi ta nufi wajan da take ganin shine bathroom tana zuwa ta cire rigar asibiti ta haɗa ruwan zafi ta fara gasa jikinta gaba ɗaya ta manta acikin asibiti take,sai da ta gama wankan tai alwala nan fa ta rasa abin sawa a jikinta,rigar asibitin ta ɗauka zata saka sai kuma taga gaba ɗaya ta jiƙe da ruwa,tana nan tsaye harta shafe 20minutes can kuma ta matsa jikin ƙofar kamar mai raɗa duk tsoro ya gama kamata cikin sanyin murya tace "Uncle.." yana jinta yay shiru kamar bai san me tace ba,kamar zatai kuka ta ƙara cewa ,"Un...cle.. Uncle" gyara kwanciyarsa yay kamar bazai magana ba sai kuma yace "uhm" sound ɗin muryarsa kawai taji tasan cewa yaji me tace sai tace "bani aron rigar ka nasa" kallon ƙofar bathroom ɗin yay kafin ya sauke numfashi yace "idan naƙi fa?" Marai-raice fuska tayi tace "Please Uncle" ɗauke idanunsa yayi kafin yace "fito ki ɗauka"kwaɓe fuska tai tace "a hakan naked?" Lumshe idanunsa yay kamar mai bacci sai kuma yace "to zauna ciki"ya faɗi hakan yana ƙara lumshe idanunsa,jin shuru yasa ta buɗe ƙofar tare da ɗan leƙawa ganin ya juya baya yasa ta fito a hankali cikin sanɗa inda taga jallabiyar sa ta nufa tana zuwa ta ɗauka yana sane ya mutsa tare da karkato kansa aikam da gudu ta kwasa tai cikin bathroom,wani lafiyayyan murmushi ya saki har sai da dimples ɗinsa suka loma,kana yaja idanunsa ya rufe,sai da ta gama saka riga taga tana ja mata har ƙasa fitowa tayi a hankali ganin babu vail ko hijab yasa ta ɗauki wani hirami ta yane kanta dashi a haka ta gabatar da sallar da ake binta kana ta shiga azkar ɗin da Jalal ya koya mata bayan ta gama ta kallesa sai kuma ta kalli basket ɗin dake kusa da ita,sai lokacin taji wata yunwa tana kawo mata farmaki,cire hiramin tayi tare da lankwasa ƙafafuwan ta,jawo basket ɗin tayi warmer ɗin farko taga soyayyan dan kalin turawa sai biyar ƙwai shi kawai ta zuba a plate ta fara ci tunda ta fara buɗe basket ɗin tsorawa bakinta ido yay ganin yadda take tauna abincin kamar bata so,komai a nutse ta keyi ta ƙara ƙyau tayi fresh girmanta ya ƙara fitowa, ajjiyar zuciya ya sauke yana ƙara ware manyan idanunsa a kanta a haka har ta gama ci ta fara neman ruwan sha, ɗago kai tayi da sauri ta rufe idanunta tare da dafe ƙirjinta,juya idanunsa yayi har sai da ta ɗan ƙware sbd wani ƙyau da yayi mata a ido,da hannu yay mata alama da fridge a hankali ta miƙe jiki a sanyaye ta nufi fridge ta ɗauki gorar ruwa mai sanyi ta sha,tana gama ta mayar da raguwar ciki,kanta a ƙasa ta ƙara so wajan sa,shima kallonta kawai yayi bai magana ba,turo baki tayi tai marai-raice fuska tace "toka matsa mana bacci zanyi" ɗauke idanunsa yayi yace "a ina zaki baccin?" Bata ce komai ba ta haye saman bed ɗin tare da kwanciya kanta ta ɗura a hannunsa kafin ta zagaye jikinsa a hannunta baice mata komai sai rufe idanunsa da yayi yana nan har yaji saukar numfashinta alamar tai bacci,ware idanunsa yayi ya sauke a fuskarta sosai take bacci cike da nutsuwa zameta yay daga jikinsa kana ya ƙaro gudun a.c sannan ya juya mata baya a haka shima yay bacci bakinsa ɗauke da azkar..INEC a can hukumar zaɓe sun daɗe da fara irga ƙuri'u dukkan wasu magoya bayan sauran ƙungiyoyin suna nan kowa yana jiran tsammani,yayinda ɓangaren jam'iyyar D.R.P Jafar da Prince Hassan da wasu manyan kusan su ashirin suke jiran abinda zaije ya dawo, Ɓangaren P.D.R kuma Lamir ne da Hon Faisal Lawan da wasu bayan tare kuma da wasu ƴan daba ma'ana dai ƴan bangar siyasa hakama sauran jami'yo kowa da wanda suke jiran jin abinda zai faru,da tafiya tai ta fiya aka fara hangen masu nasara tuni jikin Lamir yay sanyi domin duk akwatin local government ɗin da aka irga Dr Muhammad Jalal Kabeer bobo shike da rinjaye,haka governor Mubarak Yahya cibo yayta kiran Lamir domin yaji meke faruwa abinda ya keji gske ne ko yaya?sbd tuni aka fara sakin result da dukkan local government ɗin da aka irga kuma yana ganin komai koda bai gani ba labari yana iske masa, Lamir ya "kance a'a babu komai ai mune da ruwan to rinjaye ka ƙaddara ma ka zama Governor a ƙaro ma biyu rantsuwa kawai ya rage maka"sosai Governor Mubarak Yahya cibo yake jin daɗi kuma ya ƙara tabbatar masa da maganar boka Saƙib gsky ne daman ya riga ya gama yi masa alƙawarin shine da nasara ba wani ba, lokacin daya rage saura local government biyu a gama irga ƙuri'u sai hankalin sauran jami'yo suka tashi har akaso data rigima domin wasu har shirin sace akwati sukai amma da yake aƙwai ƙyakkyawan tsaro yasa aka kuri masu haddasa rigimar, ƙarfe 2:00 dai-dai shugaban inec RETURNING OFFICER ya fara faɗar sakamako tun daga sama har ƙasa inda aka fara da jam'iyyar P.D.R jam'iyyar Mubarak Yahya cibo kenan suna da ƙuri'u 6.35,165m sai jam'iyar C.C.P da ƙuri'a 4.12,24m sai kuma jam'iyyar P.P.C da ƙuri'a 3,11,12m"shiru RETURNING OFFICER ɗin yay yana ɗan kallon takardun gabansa a yayinda kuma zai faɗi jam'iyya mafi rinjaye,sai kuma yay Murmushi kana ya saita speaker a dai-dai bakinsa, Jafar kam miƙewa yay tsaye yama rasa me zai yi sai zirga-zirga yake a tsakiyar jama'a kamar daga sama babu zato babu tsammani yaji RETURNING OFFICER ɗin yace "Jam'iyyar P.D.R tana da ƙuri'u ɗai² har 20.88,159m jam'iyya kenan mafi rinjaye....
Chapter 59 · 0% Book details