Sashe 49
Uncle Ne Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A tsorace Aryan yake bin wayar da kallo, lokacin daya tabbar komai na kan wayar ya tafi yasa hannu ya dame kansa, zcyarsa cike da ƙunci yana mmkin yadda hakan ta kasance,yasan cewa rabonsa da wayar tun jiya da daddare sabida killace tan da yay,yana jiran lokacin da Baaba Lamir zai masa magana ya turo masa,sai gashi yanzu babu komai akan wayar ya rasa muhimman abubuwa bayan photonan da vedio'n,cikin takaici ya koma cikin gida,yana shiga ya shige part ɗinsa, Jalal na zaune yana cin ƙwaɗon zugalan ko kallon Aryan bai ba, cikin nutsuwa yake komai,ganin yana zaune kuma ya tabbatar Mummy baza ta barsa ya tashi ba,kawai sai data ya shiga network,kai tsaye twitter ya shiga ya fara duba news harya zo tweet ɗin wani mutum daya sanya photon Jalal a ƙasa kuma yasa _Garkuwar al'ummar gari Ibadan,dukkan farin ciki da kwanciyar hankali su tabba a gareka,in sha Allah garin Ibadan naka ne,nasara takace,kai ne jagoran mu ur excellence Dr Muhammad Jalal Kabeer bobo_ Murmushi ne ya subuce masa lokacin da ya ga Retweet ɗin mutane sama da 5k,bayan ya gama kallon Tweet ɗin daya samu lokaci,ya shiga wajan Tweet shima ya fara typing kamar haka _Allahamdulillah,Dukkan yabo ga godiya sun tabbata ga Allah subhanahu wata'ala daya bamu a ron dai da kuma lafiya kuma yake shirin nuna mana gobe,wacce ta kasance rana mai muhimmanci a gareni ta kuma dukkan masoyina,bana da wani abu dazan birgeku dashi ko zan kyautata maku dashi a halin yanzu,nasan soyayyar ku gareni daga rabbil samawati take, soyayya kuma domin Allah itace soyayya,to jama'a ban taɓa nema ba,kuma ban san yaya daɗinsa ko wahalarsa yake ba,ni nasan ina nema da dukkan lafiya ta,ilimi na,arziƙina,ina fatan kuma zaku nuna min zallar soyayya ta hanyar sanyamin albarka da kuma kaɗamin ƙuri'unku masu albarka kuma wanda zasu zamu Garkuwa gareni, ku/ki/ka tashi maza da mata aje a fita zaɓe domin tabbatar wa kanku kun zaɓe dai-dai da ra'ayinku,Ni Dr Muhammad Jalal Kabeer bobo nake cewa ƙuri'ata ƴan cina_ Yana gama rubuta yaka ya saki Tweet (posting na twitter shi ake cewa Tweet, comment kuma Retweet) tun kafin ya fita COMMENTS ɗin mutane suka fara rubdugu wasu na kurar wasu, lokacin guda aka haɗa masa COMMENTS sama da 2k screenshot yay na Tweet ɗin ya shiga account ɗinsa na I.G nan yaga flowers ɗinsa sun ƙara yawa fiye da ko yaushe,shiga yayi ya ɗura screenshot ɗin,tun kafin ya fita nan ma aka fara like and COMMENT, comment na farko ya bashi dry ina wata take cewa _Daman ka iya hausa?ko daman kai bahaushe ne i through kai Balarabe ne, serious ina son ganinka a zahiri ba photo ba,gani nake kamar photon na rage maka ƙyau,all the best_ Murmushi yay lokacin daya gama karanta comment ɗin kana ya kashe datar wayar,yana nan zaune Mummy ta sakko dwonstrais ɗin hannunta riƙe dana Jalilerh, ɗan waro manyan idanunsa yayi sbd lokacin ɗaya tayi amma ace har yanzu batai bacci ba,suna zuwa dai-dai wajansa ya ɗauke kansa,zaunar da ita tayi a kusa dashi tace "maza kici abinci idan ba su kike ranki ya ɓaci ba,shima ba kiga yaci ba saike za kiƙi ci"ta faɗi hakan tana zuba mata dambun shinkafa a plat,da mmki Mummy ta kalli Jalal,shima da sauri ya rufe idanunsa sbd yasan abinda za tace dashi tace "bobo yaushe na zama abokin wasanka?" Juya idanunsa yay ba tare kuma da yace komai ba,zama tayi tsakaninsu tare da haɗe rai,ba tare kuma da tace komai ba ta wanke hannayenta,a nutse tayi bisimillah ta ɗebo abincin ta nufi bakin Jalilerh dashi,yadda Mummy ta haɗe rai babu alamun wasa yasa dole ta buɗe bakinta ta amshi abincin,shikam Jalal yana sane ya rufe idanunsa wai ko zata ƙyalesa,amma tana ɗebo abincin tasa hannu ta ɗaka masa doka a shoulder ɗinsa,da sauri ya buɗe idanunsa yana kwaɓe fuska, Jalilerh tsayawa tayi da cin abincin tana kallonsa sbd bata taɓa ganinsa yana shagwaɓa ba,kodan bata fiya tsayawa a wajansa idan suna tare da Mummy bane ohuuu?sosai yay mata ƙyau a idanunsa gaba ɗaya ya shagwaɓe fuska yana faɗin "Allah Besty I'm full" dake something idan yana buƙatar wani abu haka yake ce mata ba,hararsa Mummy tayi tace "I'm not ur Besty,gaba ɗaya me kaci daza kace ka ƙoshi? nasan kuma haka zakai gobe kai kafin so kaita zama da yunwa kamar ƙaramin yaro?banda ma Ubangiji ya yanka da auki ai baza ka gano ba sbd siranta" ta faɗa tana nufar bakin Jalilerh ta abincin da sauri ya janye hannun Mummy daga bakin Jalilerh ya nufi nasa bakin yana Murmushi doka hannunta ya tura cikin bakinsa kana ya zare hannun yana tauna abincin, kwaɓe fuska Jalilerh tayi tare da turo baki tace "Mummy" kanta Mummy ta shafa tace "rabo dashi daughter,tunda abin hulaƙanci ne saikin ƙoshi zai ci"gwalo Jalilerh tai masa, kallonta yayi tare dajan idanunsa ya lumshe,haka Mummy ta kasance cikin su idan ta bawa Jalilerh saita bawa Jalal,duk da cewar itama yunwar ta keji amma burinta kawai taga yaci abincin,bayan sun gama Jalal ya ware idanunsa kana ya riƙe hannun Mummy yace "wait...."ya faɗi hakan shima yana ɗiban abinci a hannunsa, riƙe haɓa tayi tace "nikam kaka ka maidani ko mene?" bai ce komai ya nufi bakinta da abincin,dole ta tsaya ta amsa,sai da ƙoshi ya rabu da ita, miƙewa tayi ta nufi kitchen tana faɗin "daughter maza jeki ƙwanta kada ki manta da addu'a" idanunta ne ya cicciko da ƙwalla ganin Jalal bai kulata ba, miƙewa tayi zata bar wajan yay sauri kama hannunta juyawa tayi tana zaro idanunta waje,shima nasa idanun ya zaro yana ɗan juyasu kafin ya miƙe tsaye, hanyar kitchen ya kala yaga Mummy bata fito ba,da ɗan sauri ya rungome ta tare da bata light kiss a goshinta kafin ya saketa ya juya ya nufi part ɗinsa,da ido kawai Jalilerh ta bisa,saurin juyawa tayi sbd munsharin da taji, Mama ce ƙwance ta buɗe baki sai sharara munshari take,da ɗan saurin da take tunanin tana dashi ta nufi upstairs,ganin hakan yasa Nihila tayi sauri juyawa ta shige cikin bedroom ɗin tana shiga ta faɗa saman bed ta rufe jikinta da duvet a dole bacci take. A kasalance Jalal ya ƙarasa part ɗinsa yana zuwa ya zare wandon jikinsa da singlet ɗin,ya rage daga shi sai boxer, bathroom ya shige ya sakarwa kansa shower sosai yaji daɗin ruwan,bayan yay wanka ya ƙarasa wajan sink ya wanke bakinsa tare da ɗaura alwala,sanye da towel ya fito iya waist ɗinsa,yana zuwa ya nufi wajan dressing mirror ya shafa lotion sbd jin da gari yay yana sauyawa,comp yasa ya taje sumar kansa kafin ya fesa parfume,wasu fararan kayan bacci ya ɗauka ya sanya kana yay addu'a ya ƙwanta tare da ƙaro gudun a.c,kana ya rage hasken ɗakin,babu jimawa bacci ya ɗauke sa. _Election day_ Dukkan abinda aka sawa rana sai yanzu,idan kaga abin baizo ba to tabbas ba'a sanya masa rana ba,abinda ake jira wajan shekaru 2 da rabi yau gashi ubangiji ya nunawa duk wanda ya keson ganin ranar,ranar da mutanan gari sukaci burinta, ranar da magauta suka shirya yin zaluncin da suka daɗe suna shiryawa,ba wata rana bace face ranar Zaɓe,ranar Governor Mubarak Yahya cibo yake jin ya gama cika burinsa na zama Gwamnan jihar Ibadan,ranar da zai mulki dubban jama'ar gari,a Wannan rana kuma Dr Muhammad Jalal Kabeer bobo yake tunanin zai samu cikar muradin sa,burinsa na shekara da shekaru zai cika,farin muradin sa zai tabbatar yayinda a ranar yake saka ran sauke nauyin al'ƙawari daya ɗauka wa kansa na zama Gwamnan jihar Ibadan (Who win between two of them, Governor Mubarak Yahya cibo or Dr Muhammad Jalal Kabeer bobo?). Dukkan local government da ake zaɓe da ita ta gama cika da mutane,maza da mata yara da manya,tsofaffi da samari,kota ina mutane zuwa suke suna kaɗa ruwan ƙuri'u,kowa kuma da mazaɓarsa,haka zaɓe ya fara wakana babu tashin hankali ko kuma wasu hargitsi. Governor Mubarak Yahya cibo ne shida mayan amintattunsa a wani keɓantaccen waje suna tattaunawa akan plan ɗin da sukayi nisa a cikinsu,gyaran murya yayi yace "ina ganin zuwa yanzu lokaci yay da zamu juya masa tunaninsa,hutunsa ya ƙare farin cikinsa ya ƙare,kwanciyar hankali gidansu ya ƙare,a cikin ƙaramin lokacin zamu ruguza komai nasa" dry Lamir yyi yace "yanzu na samu Labarin zaice ya kaɗa ƙuri'a a mazaɓarsa" Hon Faisal Lawan yace "kaga abin zaifi dai-dai kenan,yana shiga cikin jama'a mu kuma saimu watsa labarai cikin sauƙi jama'a zasu fara la'antarsa"gaba ɗaya suka sanya dry,wayar Lamir ce tayi ƙara hakan tasa ya tsaya dry yay yace "Au,au,au shegen ne,bana gaya maku ba?"ya faɗa yana picking call ɗin kafin daga can ɓangaren Aryan yace "Baaba Lamir na maka magana whatsapp ka duba"Lamir yace "yawwa yaro na,bari na duba yaya zaɓan?" Aryan yace "Allahamdulillah,yanzu na dawo su kuma mutan gidan zasu fita" shuru Lamir yay kafin yace "fatan muka marawa baya?"Aryan yay dare yana mai danne zafi da raɗaɗin da zcyrsa take masa yace "haba Baaba Lamir kasan cewa zuwa yanzu babu wanda nake ganin baƙinsa irin Yaya tayaya kake tunanin zanyi abinda zai ƙara masa masoya?tayaya zanyi abinda zai kawo masa ci gaba never,babu wanda na tsana a yanzu sama dashi dan haka ni naku ne dukkan abinda kuke buƙata daga gareni ni mai biyayya ne indai zan samu cikar muradin a"dry Lamir yyi kafin yace "shikenan ka ɗauka ka samu wannan yarinyar,yanzu muna cikin jama'a dukkan abinda yake ƙasa zan kiraka" daga nan sukai sallama. A hankali Jalal ya fito daga cikin ɓangaren sa,yana sanya cikin wani Maroon ɗin boyal mai manyan zane kuma shara shara,domin har farar singlet ɗin sa ana gani,sai kuma babbar riga irinta boyal ɗin,kana baƙar hula ta tangaran,sai half covert shoe shima baƙi, hannunsa sanye cikin agogon warist mai ƙirar iphone,ya sanya farin bluetooth a kunansa,sai ƙamshi yake bazawa tamkar ranar aurensa,yana fitowa main parlour ya samu dukkan ƴan gidan suna jiransa, Mummy na sanye cikin wani Orange ɗin lace mai manyan flowers masu ƙyau,ta sanya farin mayafi a kanta,sai Mameey itama cikin milk ɗin lace irin na Mummy,sai kuma Abbou shi kuma ya saka shadda gezner,shima maroon color,gefe ya kalla yaga Nihila tasa wata rantsatsiyyar abaya black mai milk ɗin stones sai sheƙi take hannunta riƙe da waya sai faman dannawa take,tana ƙara yaɗa manufarsa da kuma tayin jama'a na suka zaɓi Yayan nata, idanunsa