Sashe 75
Oga Habeeb Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hajiya Turai kallan Habib ta yi, ta ce, "Habib ina son ka yafe ma Farida dan ta aikaita abubuwa masu girma gareka, ban yi niyyar sanar da kai ba, amma zan fad'a maka sabo da nai man mata yafiya da zan yi". Habib kallan Hajiya Turai ya yi ya ce, "Mommy duk abin da kike son sanar da ni Farida ta sanar da ni da kan ta, shine ma maganar ta ta k'arshe. Tabbas alokacin da take sanar da ni abin da tai min raina ya b'ace sosai, amma kuma bayan mutuwar ta sai naji tausan ta, na yafe mata Mommy Allah ya yafe mana baki d'aya ". 'Ameen". Hajiya Turai ta ce".
Hajiya Turai ta shi ta yi ta nufi ciki ta watsa ruwa. Habib ko naganin Hajiya Turai ta tashi ya bubbuga Hassana ya ce, "Sanat tashi mu tafi kafin Mommy tazo please ". Hassana kafad'a ta mak'ema Habib ta ce, "Naki d'in, Habib tada Hassana ya yi zau ne, ya ce, "Sanat dan Allah kin san tun jiya Mommy ta so in dawo da ke, tom yan zu idan ta fito ta kangi Allah na san ba zata bari ba mu tafi". Hassana kwanciya ta yi kan kafad'ar Habib ta ce, " Ni kam yau ba zan bika ba". Habib da ke jin tsoran kar Hajiya Turai ta fito, tashi ya yi yana tada Hassana ya ce, "Sanat ki tashi mana, kar Mommy ta zo".Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Ni fa ba zan bika ba". Habib da fe kai ya yi, ya ce, "Sanat kizo muje ina son muyi maganar tafiyar ki garin ku ne". Hassana cikin jin dad'i ta kalli Habib ta ce, "Allah da gaske kake? ". Kai Habib ya d'aga ma Hassana.
Hassana tashi tai suka tafi".
Bayan su Hassana sun tafi ne Hajiya Turai ta fito falon tan bayar Habib shi mai zai ci. Amma abin mamaki Hajiya Turai bata ga kowa ba. Dariya Hajiya Turai ta yi, ta ce, "Allah sarki Habib wai guduwa ka yi da matar taka ba Sallama, in banda abin ka ai tun da naga Hassana ta kwaremin baya na hak'ura, Allah ya baku zaman lafiya". Hajiya Turai kiran Habib tai awaya, yana d'agawa ta ce, "Habib tafiya kuma babu sallama". Habib da ga can, sosa kai ya yi, ya ce, "Mommy na zaci kin kwanta ne, shine wai kar in tada ki". Hajiya Turai dai dariya kawai ta yi, ta kashe wayarta".
Habib sai da suka biya ta Alheri suya ya sai masu gasassar kaza sannan suka tafi gida".
Suna zuwa Habib ya kamo hannun Hassan ya ce, "zo ki wanka , mun yi bacci da wuri, yau kin gaji da yawa".
"Uhm ni ban gaji ba, zan yi da kai na ma".
Cewar Hassana ".
Habib hannun Hassana ya kamo ya ce, "Haba 'yan matana, zan hutashshe ki ne, bazan kalli ko mai ". Habib haka ya shigar da Hassana toilet d'in ya taya ta tai wankan, tun tana nok'ewa har ta hak'ura Habib ya jajjagulata ahaka dai aka yi wankan aka gama".
Hassana na fitowa ta kalli Habib ta ce, "Oga Habib sai da safe".Hassana ta juya ta nufi side d'in ta. Habib bai tan ka ma Hassana ba, rabuwa ya yi da ita sai da ya yi sallar issha'i ya gama duk abin da zai yi sannan ya nufi side d'in Hassana. Hassana ko lokacin har ta kwanta,ta fara bacci. Habib bai tada Hassana ba gefanta ya je ya kwanta ya rungumota ta gefe gudin karta farka".
Hassana ko sai asuba da Habib ya ta data yin Sallah sanan ta san d'akinta ya kwana, Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib yau she ka shigo". "Kina can kina bacci". Habib ya ba Hassana amsa".
Hassana ko bayan ta yi sallah batare da Habib ya sani ba, ta fita ta shiga kitchen ta dama mai kunun gyad'a. Lokacin da Hassana ta shiga bedroom d'in ta bata iske Habib, wanka ta shiga, tana fitowa ta zauna ta yi shafa, yau Hassana har da su safa powder da lipstick, sannan ta d'akko cikin atamfofin da Hajiya Turai ta d'inka mata tasa wata,ta d'au aribian perfume ta feshe jikinta da shi, Hassana na fitowa da Cup d'in kunun Habib ta ci karo da Habib ya fito. Kallan kallo aka tsaya yi, Habib ringumo Hassana ya yi ya had'e bakin sa da nata yana tsotsa sannan ya rad'a mata cikin kunnan ta ahankali ya ce, "Nayi missing d'in sweet lips d'inki, anya ko zan iya fita". Hassana murmushi ta yi ta ce, "Uhm Oga Habib ina zaka da wuri haka? ". "Zan je Company ne, yan zu zan dawo". Habib ya ba Hassana amsa ".
Hassana hannun Habib ta kama ta ce, "Oga Habib na dama ma kunu, kasha tukun, nima zan rakaka". Habib jama ya yi Hassana ta mik'a mai kunun ya amsa yana sha, ya kai Cup d'in kunun bakin Hassana. Hassana kauda kai tayi ta ce, "Nasha ".Habib sha ya yi yabar Hassana dan ya lura ita kunun bai da meta ba. Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib manager ya dawo aiki? ". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Yauwa kin tuna min, bai dawo ba, na ce sai kin yarda". Hassana turo baki ta yi, ta ce, "Ni fa ban wani ji haushin manager , haushin Billy naji ai ita ce tasa ya maran". Habib da bai son Hassana ta je Sanat, kallan ta ya yi ya ce, "Sanat ki bari ba yau ba zaki je". Hassana mak'ema Habib kafad'a ta yi, ta ce, "Ni dai yau nake son zuwa, dan Allah, akwai abin da zan yi acan". Habib kallan Hassana ya yi ya ce, "Me zaki yi acan? ". "Mu je zaka gani".
Habib ba dan yaso ba ya tafi da Hassana Sanat Yoghurt".
Hasana bayan sun je, Habib ya nufi Office d'in shi, zai shiga Hassana ta yi saurin kamo hannun Habib ta ce, "Muje karaka ni in ga ya gurin ya yi, ka ga na rabu da zuwa ". Habib bin Hassana ya yi dan shima ya rabu da duba cikin Company yaga yadda ya yi. Duk in da su kai staff d'in gurin kallan su ka wai ake, inda duk in aka gaida Habib sai an gaida Hassana, Hassana da fara'arta ta ke amsawa.Dan yan zu kowa ya san matsayin Hasssana a Sanat. Billy tun daga nesa ta hango Hassana da Habib na zuwa. Hassana dai-dai saitin Billy ta tsaya ta kalli Habib ta ce, " Uhm Sweetheart yama sunan wannan? ". Hassana ta fad'i maganar tana nuna Billy. Habib ko sai da ya rintse ido dan jin dad'in su nan da Hassana ta kira shi da shi. Habib batare da tunanin komai ba, dan shi ya za ci Hassana da gaske ne ta manta sunan Billy, ya ce, "Billy ". Hassana kallan Billy ta yi, da fara'arta ta ce, "Sannu da aiki Billy gaskiya kina k'ok'ari, Ina manager fa? ". Billy bacin agaban Habib ne tabbas da babu abin zai sa taba Hassana amsa, amma babu yadda za tai dole ta ba Hassana amsa".
Billy d'agowa ta yi tana kalli Hassana ta ce, "Bai zo aiki ba". Hassana cikin sakin fuska ta kuma cewa, " Lafiya bai zo aiki ba". Billy kallan Habib ta yi taga hankalin shi yana kan waya, ta harari Hassana ta ce, " an dakar da shine". "Ok, ki kira shi awaya yazo yan zu, idan ya zo ku zo tare". Hassana na fad'in haka ta kamo hannun Habib ta ce, "Wayyo Sweetheart wannan tafiyar da nai har nagaji Allah, mu koma Office d'in ka". Habib kama hannun Hassana ya yi suka koma ya ce, "Dama ke kika matsa sai kin biyoni ai".
Billy kamar zuciyarta zata fashe haka taji. Da harara tabi bayan Hassana da shi, sannan ta tura ma manager text massage akan yazo yan zu".
Hassana ko suna zuwa ta zauna kan chair d'in da Habib ya ke zama ta ce, "Oga Habib yau zan futassheka zan yi duk aikin da za kai". Murmushi Habib ya yi, ya ce, "Wane ke yarinya".
Habib suna nan zau ne suna fira da Hassana Manager da Billy su kai nocking k'ofar. Habib izinin shiga ya basu".
Manager cikin girmama Habib kamar yadda ya saba ya gaida shi. Habib babu yabo babu fallasa ya amsa ma manager. Manager kallan Hassana ya yi, ya ce, "Barka da hutawa ranki shi dad'e". Hassana ma ta b'angaran ta babu ya bo ba sallasa ta amsa ma manager ".
Billy ko sosai taji ta kaicin gaida Hassanar da manager ya yi. Manager mai da kallan shi ga Habib ya yi, ya ce, "M.D, ance kana kirana? ". Habib nuna Hassana ya yi, ya ce, "Ga mai nai manka nan". Manager mai da kallan shi ga Hassana ya yi ya na jiran abin da zata ce".
Hassana kallan Billy ta yi ta ce, "Billy kawo min Yoghurt mai sanyi". Billy kamar ta ce bazata ba amma kuma babu damar haka ga Habib kusa, hakan yasa kamar zata sa ihu ta fita ta je kawo ma Hassana". Hassana kuma bata cema manager ko mai ba har sai da Billy ta dawo sannan ta kalli manager ta ce, "manager ka dawo kaci gaba da aikin ka, babu komai, ko mai ya wuce"."Godiya na ke ranki shi dad'e ". Cewar manager ".
Hassana kallan Billy ta yi da ke tsaye ta ce, "Ke fa lafiya? ". Billy cikin daurewa da yadda ta ke ji ta kalli Hassana ta ce, "ke ki ka ce in zo". Hassana kallanta ta yi sannan ta ce, "Babu da muwa zaki iya tafiya ki ci gaba da aikin ki". Billy fita ta yi tana mai jin zafin Hassana, sai dai ta san Hassana tai mata nisa nesa ba kusa ba, kuma tabbas yan zu Hassana duk wanda ta kora aiki ya koru".
Hajiya Turai ta shi ta yi ta nufi ciki ta watsa ruwa. Habib ko naganin Hajiya Turai ta tashi ya bubbuga Hassana ya ce, "Sanat tashi mu tafi kafin Mommy tazo please ". Hassana kafad'a ta mak'ema Habib ta ce, "Naki d'in, Habib tada Hassana ya yi zau ne, ya ce, "Sanat dan Allah kin san tun jiya Mommy ta so in dawo da ke, tom yan zu idan ta fito ta kangi Allah na san ba zata bari ba mu tafi". Hassana kwanciya ta yi kan kafad'ar Habib ta ce, " Ni kam yau ba zan bika ba". Habib da ke jin tsoran kar Hajiya Turai ta fito, tashi ya yi yana tada Hassana ya ce, "Sanat ki tashi mana, kar Mommy ta zo".Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Ni fa ba zan bika ba". Habib da fe kai ya yi, ya ce, "Sanat kizo muje ina son muyi maganar tafiyar ki garin ku ne". Hassana cikin jin dad'i ta kalli Habib ta ce, "Allah da gaske kake? ". Kai Habib ya d'aga ma Hassana.
Hassana tashi tai suka tafi".
Bayan su Hassana sun tafi ne Hajiya Turai ta fito falon tan bayar Habib shi mai zai ci. Amma abin mamaki Hajiya Turai bata ga kowa ba. Dariya Hajiya Turai ta yi, ta ce, "Allah sarki Habib wai guduwa ka yi da matar taka ba Sallama, in banda abin ka ai tun da naga Hassana ta kwaremin baya na hak'ura, Allah ya baku zaman lafiya". Hajiya Turai kiran Habib tai awaya, yana d'agawa ta ce, "Habib tafiya kuma babu sallama". Habib da ga can, sosa kai ya yi, ya ce, "Mommy na zaci kin kwanta ne, shine wai kar in tada ki". Hajiya Turai dai dariya kawai ta yi, ta kashe wayarta".
Habib sai da suka biya ta Alheri suya ya sai masu gasassar kaza sannan suka tafi gida".
Suna zuwa Habib ya kamo hannun Hassan ya ce, "zo ki wanka , mun yi bacci da wuri, yau kin gaji da yawa".
"Uhm ni ban gaji ba, zan yi da kai na ma".
Cewar Hassana ".
Habib hannun Hassana ya kamo ya ce, "Haba 'yan matana, zan hutashshe ki ne, bazan kalli ko mai ". Habib haka ya shigar da Hassana toilet d'in ya taya ta tai wankan, tun tana nok'ewa har ta hak'ura Habib ya jajjagulata ahaka dai aka yi wankan aka gama".
Hassana na fitowa ta kalli Habib ta ce, "Oga Habib sai da safe".Hassana ta juya ta nufi side d'in ta. Habib bai tan ka ma Hassana ba, rabuwa ya yi da ita sai da ya yi sallar issha'i ya gama duk abin da zai yi sannan ya nufi side d'in Hassana. Hassana ko lokacin har ta kwanta,ta fara bacci. Habib bai tada Hassana ba gefanta ya je ya kwanta ya rungumota ta gefe gudin karta farka".
Hassana ko sai asuba da Habib ya ta data yin Sallah sanan ta san d'akinta ya kwana, Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib yau she ka shigo". "Kina can kina bacci". Habib ya ba Hassana amsa".
Hassana ko bayan ta yi sallah batare da Habib ya sani ba, ta fita ta shiga kitchen ta dama mai kunun gyad'a. Lokacin da Hassana ta shiga bedroom d'in ta bata iske Habib, wanka ta shiga, tana fitowa ta zauna ta yi shafa, yau Hassana har da su safa powder da lipstick, sannan ta d'akko cikin atamfofin da Hajiya Turai ta d'inka mata tasa wata,ta d'au aribian perfume ta feshe jikinta da shi, Hassana na fitowa da Cup d'in kunun Habib ta ci karo da Habib ya fito. Kallan kallo aka tsaya yi, Habib ringumo Hassana ya yi ya had'e bakin sa da nata yana tsotsa sannan ya rad'a mata cikin kunnan ta ahankali ya ce, "Nayi missing d'in sweet lips d'inki, anya ko zan iya fita". Hassana murmushi ta yi ta ce, "Uhm Oga Habib ina zaka da wuri haka? ". "Zan je Company ne, yan zu zan dawo". Habib ya ba Hassana amsa ".
Hassana hannun Habib ta kama ta ce, "Oga Habib na dama ma kunu, kasha tukun, nima zan rakaka". Habib jama ya yi Hassana ta mik'a mai kunun ya amsa yana sha, ya kai Cup d'in kunun bakin Hassana. Hassana kauda kai tayi ta ce, "Nasha ".Habib sha ya yi yabar Hassana dan ya lura ita kunun bai da meta ba. Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib manager ya dawo aiki? ". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Yauwa kin tuna min, bai dawo ba, na ce sai kin yarda". Hassana turo baki ta yi, ta ce, "Ni fa ban wani ji haushin manager , haushin Billy naji ai ita ce tasa ya maran". Habib da bai son Hassana ta je Sanat, kallan ta ya yi ya ce, "Sanat ki bari ba yau ba zaki je". Hassana mak'ema Habib kafad'a ta yi, ta ce, "Ni dai yau nake son zuwa, dan Allah, akwai abin da zan yi acan". Habib kallan Hassana ya yi ya ce, "Me zaki yi acan? ". "Mu je zaka gani".
Habib ba dan yaso ba ya tafi da Hassana Sanat Yoghurt".
Hasana bayan sun je, Habib ya nufi Office d'in shi, zai shiga Hassana ta yi saurin kamo hannun Habib ta ce, "Muje karaka ni in ga ya gurin ya yi, ka ga na rabu da zuwa ". Habib bin Hassana ya yi dan shima ya rabu da duba cikin Company yaga yadda ya yi. Duk in da su kai staff d'in gurin kallan su ka wai ake, inda duk in aka gaida Habib sai an gaida Hassana, Hassana da fara'arta ta ke amsawa.Dan yan zu kowa ya san matsayin Hasssana a Sanat. Billy tun daga nesa ta hango Hassana da Habib na zuwa. Hassana dai-dai saitin Billy ta tsaya ta kalli Habib ta ce, " Uhm Sweetheart yama sunan wannan? ". Hassana ta fad'i maganar tana nuna Billy. Habib ko sai da ya rintse ido dan jin dad'in su nan da Hassana ta kira shi da shi. Habib batare da tunanin komai ba, dan shi ya za ci Hassana da gaske ne ta manta sunan Billy, ya ce, "Billy ". Hassana kallan Billy ta yi, da fara'arta ta ce, "Sannu da aiki Billy gaskiya kina k'ok'ari, Ina manager fa? ". Billy bacin agaban Habib ne tabbas da babu abin zai sa taba Hassana amsa, amma babu yadda za tai dole ta ba Hassana amsa".
Billy d'agowa ta yi tana kalli Hassana ta ce, "Bai zo aiki ba". Hassana cikin sakin fuska ta kuma cewa, " Lafiya bai zo aiki ba". Billy kallan Habib ta yi taga hankalin shi yana kan waya, ta harari Hassana ta ce, " an dakar da shine". "Ok, ki kira shi awaya yazo yan zu, idan ya zo ku zo tare". Hassana na fad'in haka ta kamo hannun Habib ta ce, "Wayyo Sweetheart wannan tafiyar da nai har nagaji Allah, mu koma Office d'in ka". Habib kama hannun Hassana ya yi suka koma ya ce, "Dama ke kika matsa sai kin biyoni ai".
Billy kamar zuciyarta zata fashe haka taji. Da harara tabi bayan Hassana da shi, sannan ta tura ma manager text massage akan yazo yan zu".
Hassana ko suna zuwa ta zauna kan chair d'in da Habib ya ke zama ta ce, "Oga Habib yau zan futassheka zan yi duk aikin da za kai". Murmushi Habib ya yi, ya ce, "Wane ke yarinya".
Habib suna nan zau ne suna fira da Hassana Manager da Billy su kai nocking k'ofar. Habib izinin shiga ya basu".
Manager cikin girmama Habib kamar yadda ya saba ya gaida shi. Habib babu yabo babu fallasa ya amsa ma manager. Manager kallan Hassana ya yi, ya ce, "Barka da hutawa ranki shi dad'e". Hassana ma ta b'angaran ta babu ya bo ba sallasa ta amsa ma manager ".
Billy ko sosai taji ta kaicin gaida Hassanar da manager ya yi. Manager mai da kallan shi ga Habib ya yi, ya ce, "M.D, ance kana kirana? ". Habib nuna Hassana ya yi, ya ce, "Ga mai nai manka nan". Manager mai da kallan shi ga Hassana ya yi ya na jiran abin da zata ce".
Hassana kallan Billy ta yi ta ce, "Billy kawo min Yoghurt mai sanyi". Billy kamar ta ce bazata ba amma kuma babu damar haka ga Habib kusa, hakan yasa kamar zata sa ihu ta fita ta je kawo ma Hassana". Hassana kuma bata cema manager ko mai ba har sai da Billy ta dawo sannan ta kalli manager ta ce, "manager ka dawo kaci gaba da aikin ka, babu komai, ko mai ya wuce"."Godiya na ke ranki shi dad'e ". Cewar manager ".
Hassana kallan Billy ta yi da ke tsaye ta ce, "Ke fa lafiya? ". Billy cikin daurewa da yadda ta ke ji ta kalli Hassana ta ce, "ke ki ka ce in zo". Hassana kallanta ta yi sannan ta ce, "Babu da muwa zaki iya tafiya ki ci gaba da aikin ki". Billy fita ta yi tana mai jin zafin Hassana, sai dai ta san Hassana tai mata nisa nesa ba kusa ba, kuma tabbas yan zu Hassana duk wanda ta kora aiki ya koru".