Sashe 26
Oga Habeeb Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hassana tunanin ta farayi ahankali, tana tuno abinda ya faru da ita ya fara dawo mata kad'an-kad'an. Tabbas idan bata mantaba tabbas tunda tasha maganin da Farida ta bata, ta rasa natsuwarta, Hassana kallan wanda ta bata taba Habib ta yi. Alhamdulillah Hassana ta ce, ganin wanda Farida ta bata tace taba Habib bata bashi ba, dan tabbas wanan maganin nada wani sinadari na b'atar da hankali cewar Hassana, amma kuma ai Aunty Farida "yar'uwar su Oga Habib ce, bazata bashi abinda zai cutar da shiba, tom amma ni meyasa maganin ya yi min haka?, haka dai Hassana ta gama tambayar kanta ba amsa, kuma still bata bar kukan da take ba. Hassana nan zaune tana kuka, ta ji nocking. Share hawayanta ta yi, sannan ta je ta lek'a ta window ".
Hassana Bilya ta gani tsaye ya yi crossing d'in hannun shi yana mata wani irin kallo da yasa ta sha jinin jinin jikinta. Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, tana didduk'ar da kai kamar muna fuka, ta ce, "Oga Bilya ina kwana". Me makon Bilya ya amsa ma Hassana gaisuwarta sai cewa ya yi, "Hassana jiya me yasa da muka buga k'ofa biki bud'e mana ba? ". Hassana cikin rawar murya ta ce, "Oga Bilya bacci ne ya kwasheni". "Amma meyasa baki kwanta falo ba! , kika shiga bedroom d'in Oga Habib? ". Hassana sosai ta tsora da kalaman Bilya da yana yin yadda ya ke mata magana, hakan yasata, cikin rawar murya ta ce, "Oga Habib ne ya kaini". Bilya kallan Hassana ya yi, ya dad'e yana kallanta sannan ya ce, "Hassana me yasaki kuka? ". Shiru Hassana ta yi tana wasa da fingers d'inta. Bilya k'ara mai-mai ta ma Hassana tambayar shi ya yi, ya ce, "Hassana nace me yasa ki kuka? ". Hassana kuka ta sa, still ta kasa yin magana".
Farida ko da zuwanta kenan tazo ganin k'wak'waf, da sauri ta lab'e tana mai jin dad'in ganin Hassana da ta yi tana kuka, dan ko ba afad'a mata ba, tasan mai faruwa ta faru, tsakanin Hassana da Habib. Farida cikin jin dad'i ta koma d'akinta, tana zuwa ta fad'a kan bed d'inta tana jin dad'in abinda ta gani, dan tabbas Hassana kukan da ta ke yi na kusantarta ne da Habib ya yi, acewar Farida.waya Farida ta d'akko ta kira Mahaifiyarta, Hajiya Murja dan yi mata albishir.
Hajiya Murja na d'auka Farida ta ce, cikin jin dad'i, "Mommyna albishirinki? ". Daga can b'angaran, Hajiya Murja ta ce, "Goro fari k'ar kato". Farida cikin murna da d'oki ta ce, "Mommyna Wallahi na yarda da aikin Malam mai biyan buk'ata dole, Mommyna aiki ya k'arye dan Oga Habib ya kusanci Hassana, yanzu haka maganar da nake miki kuka ta ke, yanzu Mommy ki je gun Malam ya baki na barinta gidan sai kizo da shi, dan ni Wallahi bana son ta k'ara kwana a gidannan". Hajiya Murja itama cikin jin dad'in nasarar aikin da su kayi ta ce, "Tom Farida yanzu sai hankalinki ya kwanta ko, kinga dai alamun nasara, yanzu bari inyi breakfast , idan nagama inyi wanka sai in je gun Malam d'in, daga can zo nan"."Tom Mommy sai kin zo". Farida na fad'in haka ta kashe wayar, tana mai jin farinci aranta".
Can b'angaran su Hassana ko, Bilya cikin damuwa ya ce, "Hassana please mana, dan Allah karki sani confused mana, me yasa kike kuka? ". Hassana cikin shasshek'ar kuka ta ce, "Oga Bilya bana son k'ara zuwa gurin Oga Habib dan Allah ". Shiru Bilya ya yi yana mai kallan ganin yadda ta ke kuka. Sannan ya ce, "Shikenan Hassana ki shiru haka nan kar kanki ya yi ciwo,in dai gurin Oga Habib ne ki yi hak'uri, insha Allah daga yau bazaki k'ara zuwa ba, nina san mai zan cema Hajiya ".
Duk maganar nan da Hassana da Bilya su ke yi, ta Window su ke yinta. Bilya kallan Hassana ya yi, ya ce, "Bari in kira Musa muzo mu fidda ki". Kai Hassana ta d'aga ma Bilya, ya juya kai ya tafi".
Bilya ya tafi ba dad'ewa sai ga shi ya dawo da Musa. Musa kallan Bilya ya yi ya ce, "Bilya abata abin breakfast ta bashi mana, inda naji kana cewa daga yau ba zata k'ara zuwa bashi abinci ba". Shiru Bilya ya yi sannan ya ce, "Musa Wallahi anfara shiga hakin yarinyar nan, yanzu haka maganar da nakema kuka nazo na sameta ta nayi, amma bari in amso abin breakfast din in kai mata ta bashi". Bilya wajan Baba Lami ya je, ta had'o mai abin breakfast d'in Habib".
Bilya amsa ya yi, yana zuwa ya yi nocking d'in k'ofar. Hassana ta sowa ta yi. Bilya kallan Hassana ya yi ya ce, "Hassana ga breakfast d'in Oga Habib nan dan Allah ki bashi, ni nai miki alk'awari daga yau ba mai kuma k'arasaki kawo ma Oga Habib abinci ko magani". Hassana amsa ta yi tashiga da shi, kunun gyad'a abinda Habib ya fi so. Hassana zuba ma Habib ta yi ta mik'a mai ya amsa ya shanye. Doya da kwan ta bashi ita kuma ya k'i ci. Habib na gama shanye kunun Hassana tai ma Bilya magana da ya ke, Bilya na bakin k'ofar suna jiran Hassana ta gama ba Habib abin breakfast d'in .
Hassana juyowa ta yi tana kallan Habib da ke rik'e da hannunta, sannan ta kai wasu mintoci tana kallan Habib sannan ta ce, "Oga Habib sakan min hannu zan tafi, sai watarana bazan k'ara shigowa inda kake ba, jiya nariski kaina awani kallan yanayi mai wuyar fassarawa, bana fata haka ya k'ara faruwa dani, bansan nan gaba mai zai faruba, idan haka ya kuma faruwa". Hassana rik'e hannun Habib ta yi, ta ce,"Oga Habib ina maka fatan alkairi, Allah ya baka lafiya".
Hassana na fad'in haka ta juya zata fita, Habib ya rik'e hanunta.
Hassana cikin sanyin muryarta ta kira Bilya, ta ce, "Oga Bilya nagama ku shigo".
Bilya ko da Musa suna tsaye bakin k'ofar, dama Hassana suke jira suzo su fitar da ita".
Da k'arfi su Bilya suka b'amb'are Hassana daga hannun Habib kamar yadda suka saba. Hassana ko mai-makon ta je Falon Hajiya Turai, b'angaran su na "yan aiki ta wuce".
Farida ko da taji shiru, Hassana bata shigo Falon Hajiya Turai ba, tashi ta yi ta nufi part d'in worker's d'in gidan. Farida nesa da b'angaran su Hassana ta tsaya yadda babu wanda zai ji abinda zata cema Hassana. Farida na nan tsaye d'aya daga cikin worker's d'in ta zo wucewa, Farida kiran ta ta yi, ta ce ta kiramata Hassama".
Hassana ko na kwance tana jinta duk ba dad'i, ga halinda ta tashi taga kanta duk ya da meta, dan har yanzu ko mai batasa abakinta ba. Binta kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana Aunty Farida na kiranki". Hassana batare da tace mata komai ba ta tashi ta fita, dan amsa kiran Faridar".
Tsaye Hassana ta iske Farida tana jiranta. Farida kallan Hassana ta yi, ta ce, "Ke kukan me d'azu naganki kinayi? ". Hassana da mamaki ta kalli Farida dan tambayar tazo mata abazata.Farida ko jin Hassana ta yi shiru tana kallanta ya sa cikin k'osawa ta ce, "Nace me yasa ki kuka d'azu?, da naganki tsaye da Bilya a wajan window Falon Oga Habib ". Hassana rasa abinda zata ce ma Farida ta yi, ka wai sai ce mata tayi. "Aunty Farida banda lafiya ne". Farida cikin d'aga murya ta ce, dan tana tunanin Hassana so take ta b'oyemata Habib ya yi mata Fyad'e, hakan yasa cikin d'aga Murya , Farida ta ce, "K'arya kike Wallahi, me kika ce ma Bilya Oga Habib ya yi miki?, ko kina tunanin banji bane? ". Hassana da mamaki ta ke kallan Farida, sannan cikin sanyin murya ta ce, "Wallahi Aunty Farida bance ma Oga Bilya Oga Habib ya yi min ko mai ba, kawai dai ina kuka ne shine ya ke tambayata abinda ya sani kuka". Farida da saurinta kamar wani zai rigata ta ce, "Tom meye yasaki kukan? ". Hassana kallan Farida ta yi kamar za tai kuka ta ce, "Nagaji da kaima Oga Habib abinci ne, shine yasani kuka". Wani murmushi Farida ta yi ma Hassana , dan ita a d'aukarta Hassana tana karewa ne, bata son taji Habib ta yi mata Fyad'e ne. Hakan yasa Farida ta d'aurai fuska, ta kalli Hassana ta ce, "Hassana ni zaki yi ma k'arya, saboda kina tunanin bansan abinda ya faruba".
Hassana ko rud'ewa ta yi jin abinda Farida ta ce, sai ta ke ganin kamar ko taganta ne lokacinda jiya ta cire kayanta , bayan shan maganin da ta kawo mata. Hakan yasa Hassana cikin zubba kwallah ta ce, "Aunty Farida Wallahi babu komai, amma idan baki yadda ba ki kira Oga Bilya ki tambaye shi". Wani tunanine yazoma Farida, kallan Hassana ta yi, ta ce, " nasan dai kinsha maganin da na baki ko? ". Kai Hassana ta d'aga ma Farida. "Ok, tom na Oga Habib fa da nace ki bashi, kin bashi? ". "Aunty Farida ki yi hak'uri banba shiba, wani na bashi wanda Hajiya taban in bashi, nama zaci wanda kika banne, sai yau da natshi nagan shi, amma yanzu zanje in bash.......... ". Marin da Farida taima Hassana ne, yasa Hassana tai shiru. Farida nuna Hassana da d'an yatsa ta yi, ta ce, "Dan uwarki ni zaki sa in yi asara, tom Wallahi baki isaba kin yi kad'an..... ".
Ringing tone d'in wayar Farida ne yasa ta yi shiru ta maida kanta da kallan wayar. Farida na dubawa taga Mahaifiyarta ce, hakan yasa Farida ta yi saurin barin gurin, sannan ta d'aga kiran.
Hajiya Turai sanar da Farida ta yi gata nan zuwa. Farida cikin tashin hankali ta ce, "Mommy dan Allah ki yi sauri ki zo , Wallahi akwai damuwa sosai".
Farida ko cikin damuwa ta koma falon Hajiya Turai dan sanar da ita zuwan Mahaifiyarta".
Farida zaune ta iske Bilya da Baba Lami da Hajiya Turai a falon, Farida gu ta nema ta zauna, dan tana son jin tattaunawar da suke.
Hajiya Turai kallan Bilya ta yi, ta ce, "Bilya kai fa muke sauraro baka ce mana ko mai ba, kace kuma kana son magana dani". Hajiya Turai ta idasa maganar cikin damuwa".
Hassana Bilya ta gani tsaye ya yi crossing d'in hannun shi yana mata wani irin kallo da yasa ta sha jinin jinin jikinta. Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, tana didduk'ar da kai kamar muna fuka, ta ce, "Oga Bilya ina kwana". Me makon Bilya ya amsa ma Hassana gaisuwarta sai cewa ya yi, "Hassana jiya me yasa da muka buga k'ofa biki bud'e mana ba? ". Hassana cikin rawar murya ta ce, "Oga Bilya bacci ne ya kwasheni". "Amma meyasa baki kwanta falo ba! , kika shiga bedroom d'in Oga Habib? ". Hassana sosai ta tsora da kalaman Bilya da yana yin yadda ya ke mata magana, hakan yasata, cikin rawar murya ta ce, "Oga Habib ne ya kaini". Bilya kallan Hassana ya yi, ya dad'e yana kallanta sannan ya ce, "Hassana me yasaki kuka? ". Shiru Hassana ta yi tana wasa da fingers d'inta. Bilya k'ara mai-mai ta ma Hassana tambayar shi ya yi, ya ce, "Hassana nace me yasa ki kuka? ". Hassana kuka ta sa, still ta kasa yin magana".
Farida ko da zuwanta kenan tazo ganin k'wak'waf, da sauri ta lab'e tana mai jin dad'in ganin Hassana da ta yi tana kuka, dan ko ba afad'a mata ba, tasan mai faruwa ta faru, tsakanin Hassana da Habib. Farida cikin jin dad'i ta koma d'akinta, tana zuwa ta fad'a kan bed d'inta tana jin dad'in abinda ta gani, dan tabbas Hassana kukan da ta ke yi na kusantarta ne da Habib ya yi, acewar Farida.waya Farida ta d'akko ta kira Mahaifiyarta, Hajiya Murja dan yi mata albishir.
Hajiya Murja na d'auka Farida ta ce, cikin jin dad'i, "Mommyna albishirinki? ". Daga can b'angaran, Hajiya Murja ta ce, "Goro fari k'ar kato". Farida cikin murna da d'oki ta ce, "Mommyna Wallahi na yarda da aikin Malam mai biyan buk'ata dole, Mommyna aiki ya k'arye dan Oga Habib ya kusanci Hassana, yanzu haka maganar da nake miki kuka ta ke, yanzu Mommy ki je gun Malam ya baki na barinta gidan sai kizo da shi, dan ni Wallahi bana son ta k'ara kwana a gidannan". Hajiya Murja itama cikin jin dad'in nasarar aikin da su kayi ta ce, "Tom Farida yanzu sai hankalinki ya kwanta ko, kinga dai alamun nasara, yanzu bari inyi breakfast , idan nagama inyi wanka sai in je gun Malam d'in, daga can zo nan"."Tom Mommy sai kin zo". Farida na fad'in haka ta kashe wayar, tana mai jin farinci aranta".
Can b'angaran su Hassana ko, Bilya cikin damuwa ya ce, "Hassana please mana, dan Allah karki sani confused mana, me yasa kike kuka? ". Hassana cikin shasshek'ar kuka ta ce, "Oga Bilya bana son k'ara zuwa gurin Oga Habib dan Allah ". Shiru Bilya ya yi yana mai kallan ganin yadda ta ke kuka. Sannan ya ce, "Shikenan Hassana ki shiru haka nan kar kanki ya yi ciwo,in dai gurin Oga Habib ne ki yi hak'uri, insha Allah daga yau bazaki k'ara zuwa ba, nina san mai zan cema Hajiya ".
Duk maganar nan da Hassana da Bilya su ke yi, ta Window su ke yinta. Bilya kallan Hassana ya yi, ya ce, "Bari in kira Musa muzo mu fidda ki". Kai Hassana ta d'aga ma Bilya, ya juya kai ya tafi".
Bilya ya tafi ba dad'ewa sai ga shi ya dawo da Musa. Musa kallan Bilya ya yi ya ce, "Bilya abata abin breakfast ta bashi mana, inda naji kana cewa daga yau ba zata k'ara zuwa bashi abinci ba". Shiru Bilya ya yi sannan ya ce, "Musa Wallahi anfara shiga hakin yarinyar nan, yanzu haka maganar da nakema kuka nazo na sameta ta nayi, amma bari in amso abin breakfast din in kai mata ta bashi". Bilya wajan Baba Lami ya je, ta had'o mai abin breakfast d'in Habib".
Bilya amsa ya yi, yana zuwa ya yi nocking d'in k'ofar. Hassana ta sowa ta yi. Bilya kallan Hassana ya yi ya ce, "Hassana ga breakfast d'in Oga Habib nan dan Allah ki bashi, ni nai miki alk'awari daga yau ba mai kuma k'arasaki kawo ma Oga Habib abinci ko magani". Hassana amsa ta yi tashiga da shi, kunun gyad'a abinda Habib ya fi so. Hassana zuba ma Habib ta yi ta mik'a mai ya amsa ya shanye. Doya da kwan ta bashi ita kuma ya k'i ci. Habib na gama shanye kunun Hassana tai ma Bilya magana da ya ke, Bilya na bakin k'ofar suna jiran Hassana ta gama ba Habib abin breakfast d'in .
Hassana juyowa ta yi tana kallan Habib da ke rik'e da hannunta, sannan ta kai wasu mintoci tana kallan Habib sannan ta ce, "Oga Habib sakan min hannu zan tafi, sai watarana bazan k'ara shigowa inda kake ba, jiya nariski kaina awani kallan yanayi mai wuyar fassarawa, bana fata haka ya k'ara faruwa dani, bansan nan gaba mai zai faruba, idan haka ya kuma faruwa". Hassana rik'e hannun Habib ta yi, ta ce,"Oga Habib ina maka fatan alkairi, Allah ya baka lafiya".
Hassana na fad'in haka ta juya zata fita, Habib ya rik'e hanunta.
Hassana cikin sanyin muryarta ta kira Bilya, ta ce, "Oga Bilya nagama ku shigo".
Bilya ko da Musa suna tsaye bakin k'ofar, dama Hassana suke jira suzo su fitar da ita".
Da k'arfi su Bilya suka b'amb'are Hassana daga hannun Habib kamar yadda suka saba. Hassana ko mai-makon ta je Falon Hajiya Turai, b'angaran su na "yan aiki ta wuce".
Farida ko da taji shiru, Hassana bata shigo Falon Hajiya Turai ba, tashi ta yi ta nufi part d'in worker's d'in gidan. Farida nesa da b'angaran su Hassana ta tsaya yadda babu wanda zai ji abinda zata cema Hassana. Farida na nan tsaye d'aya daga cikin worker's d'in ta zo wucewa, Farida kiran ta ta yi, ta ce ta kiramata Hassama".
Hassana ko na kwance tana jinta duk ba dad'i, ga halinda ta tashi taga kanta duk ya da meta, dan har yanzu ko mai batasa abakinta ba. Binta kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana Aunty Farida na kiranki". Hassana batare da tace mata komai ba ta tashi ta fita, dan amsa kiran Faridar".
Tsaye Hassana ta iske Farida tana jiranta. Farida kallan Hassana ta yi, ta ce, "Ke kukan me d'azu naganki kinayi? ". Hassana da mamaki ta kalli Farida dan tambayar tazo mata abazata.Farida ko jin Hassana ta yi shiru tana kallanta ya sa cikin k'osawa ta ce, "Nace me yasa ki kuka d'azu?, da naganki tsaye da Bilya a wajan window Falon Oga Habib ". Hassana rasa abinda zata ce ma Farida ta yi, ka wai sai ce mata tayi. "Aunty Farida banda lafiya ne". Farida cikin d'aga murya ta ce, dan tana tunanin Hassana so take ta b'oyemata Habib ya yi mata Fyad'e, hakan yasa cikin d'aga Murya , Farida ta ce, "K'arya kike Wallahi, me kika ce ma Bilya Oga Habib ya yi miki?, ko kina tunanin banji bane? ". Hassana da mamaki ta ke kallan Farida, sannan cikin sanyin murya ta ce, "Wallahi Aunty Farida bance ma Oga Bilya Oga Habib ya yi min ko mai ba, kawai dai ina kuka ne shine ya ke tambayata abinda ya sani kuka". Farida da saurinta kamar wani zai rigata ta ce, "Tom meye yasaki kukan? ". Hassana kallan Farida ta yi kamar za tai kuka ta ce, "Nagaji da kaima Oga Habib abinci ne, shine yasani kuka". Wani murmushi Farida ta yi ma Hassana , dan ita a d'aukarta Hassana tana karewa ne, bata son taji Habib ta yi mata Fyad'e ne. Hakan yasa Farida ta d'aurai fuska, ta kalli Hassana ta ce, "Hassana ni zaki yi ma k'arya, saboda kina tunanin bansan abinda ya faruba".
Hassana ko rud'ewa ta yi jin abinda Farida ta ce, sai ta ke ganin kamar ko taganta ne lokacinda jiya ta cire kayanta , bayan shan maganin da ta kawo mata. Hakan yasa Hassana cikin zubba kwallah ta ce, "Aunty Farida Wallahi babu komai, amma idan baki yadda ba ki kira Oga Bilya ki tambaye shi". Wani tunanine yazoma Farida, kallan Hassana ta yi, ta ce, " nasan dai kinsha maganin da na baki ko? ". Kai Hassana ta d'aga ma Farida. "Ok, tom na Oga Habib fa da nace ki bashi, kin bashi? ". "Aunty Farida ki yi hak'uri banba shiba, wani na bashi wanda Hajiya taban in bashi, nama zaci wanda kika banne, sai yau da natshi nagan shi, amma yanzu zanje in bash.......... ". Marin da Farida taima Hassana ne, yasa Hassana tai shiru. Farida nuna Hassana da d'an yatsa ta yi, ta ce, "Dan uwarki ni zaki sa in yi asara, tom Wallahi baki isaba kin yi kad'an..... ".
Ringing tone d'in wayar Farida ne yasa ta yi shiru ta maida kanta da kallan wayar. Farida na dubawa taga Mahaifiyarta ce, hakan yasa Farida ta yi saurin barin gurin, sannan ta d'aga kiran.
Hajiya Turai sanar da Farida ta yi gata nan zuwa. Farida cikin tashin hankali ta ce, "Mommy dan Allah ki yi sauri ki zo , Wallahi akwai damuwa sosai".
Farida ko cikin damuwa ta koma falon Hajiya Turai dan sanar da ita zuwan Mahaifiyarta".
Farida zaune ta iske Bilya da Baba Lami da Hajiya Turai a falon, Farida gu ta nema ta zauna, dan tana son jin tattaunawar da suke.
Hajiya Turai kallan Bilya ta yi, ta ce, "Bilya kai fa muke sauraro baka ce mana ko mai ba, kace kuma kana son magana dani". Hajiya Turai ta idasa maganar cikin damuwa".