← Book details Oga Habeeb Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 78

Sashe 41

Oga Habeeb Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Farida a cikin mota ta samu su Hajiya Murja suka tafi, gidan Hajiya Bilki. Inda suna tafiya Farida na basu labarin yadda su kai da bokan. Hajiya Bilki ce ta ce, "Ai Farida karki damu tunda kikazo gun kafin gobe..., ai aikinki yagama biya, tun-tuni da muntab'a wannan hirar da Hajiya Murja ai da tuni kin auri Habib angama, nan dai suka ta hirarsu har suka isa gidan Hajiya Bilki inda a nan za su kwana sai gobe zasu wuce".

Haka ko akai, washe gari da wuri su Farida suka kama hanyar Katsina, dan daga inda suka je zuwa airport akwai nisa".

Su Hajiya Murja sai dare suka shigo Abuja, Hajiya Murja ganin dare ya yi , ta tsare Farida ta kwana awajanta".

Washer gari da sassafe Farida ta yi sammakon zuwa gidansu Habib.

B'angaran Hassana ko, tun jiya ta kasa gane kan mutuminta, sai wani irin bacci ya ke, duk yau kuma tun safe yak'i cin komai, tayi- tayi yak'i ci, yana cikin baccin ita kuma lokacin tana kitchen tana k'ok'arin had'a musu dinner ta ji wani irin k'ara wadda sai da k'arra ta firgitata, hakan yasa ta rigo da gudu daga kitchen d'in, ta nufi bedroom d'in Habib, tana zuwa zaune ta iske Habib tsayiyar gado yana dafe da kanshi da hannun wanshi guda biyu, yana jijjuya kan yana rirrintse ido. Hassana na zuwa ta hau kan gadon cikin rud'u da yanayin da taga Habib d'in, Hassana na zuwa ta rik'o Habib d'in tana tofa mai duk addu'ar da tazo bakinta. Can Hassana ta ji Habib ya yi wata uwar gyatsa da k'arfi. Can kuma sai taga ya saki kanshi da hannu wanshi da yasa ya daddafe kai d'in ".

Habib d'ago da kanshi ya yi yana kallan Hassana. Hassana kuma cikin jin dad'in ganin Habib ya bar abinda ya ke, da alamu ya ji sauk'i, ta rungumo shi, ta ce, "Ayyah Oga Habib Sannu ko, tsakanin jiya da yau kana shan wahal...... ".

Hassana tsawar da ta ji ce tare ta turota k'asan da Habib ya yi yasa bata k'arasa abinda ta ke fad'aba".

Allah sarki Hassana bata damu da abinda Habib ya yi mata ba, ta shi ta kuma yi zata hau gadon, Habib ya kuma daka mata tsawa , wadda tafi waccan, ya ce, "Ke ! , wacece ke!?, kuma me kike yi anan? ". Hassana cikin tsoro da al'ajabi ta ke kallan Habib, dan idan taji da kyau sai taji kamar Habib ne yake magana, kuma kamar yadawo hankalinshi abisa ga yadda ya ke maganar............ ✍️

Tofa wai meke faruwa ne, Habib kamar yadawo hankalin shi nake gani🤐🤐🤐🤐.

Ga kuma su Hajiya Farida da tarin Magunguna ko ya abin zai kaya???.

Idan kin karanta daure ki yi Comment sister, Comment ke k'aramin kwarin gwiwar update da wuri.

Share
&
Comment please 🙏.

📚 OGA HABIB 📚
💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*

https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl

_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_

*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*
TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI.

https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7

https://m.facebook.com/groups/565235401564189/

Lale watan alkairi, watan da ummulkairi, Amina zatil fatahi ta haifi d'a al sugaba, lale watan da duka aljanu suke ta ce wa sun bani dan basu k'ara ci gaba.
Yau ne sha biyu ga watan rabu Auwal, wata mai girma mai daraja, watan da fitayyan halitta yazo duniya, Allah kak'ara mana k'aunar annabi Muhammadu (S, A, W).
Happy maulud.

Shafi na 48&49.

Hassana cikin murna da manta waye Habib, ta kalli Habib, tana mai k'okarin k'ara hawa gadon, ta ce, "Wayyo Oga Habib ka warkene ko ko magana ce ta samu? ". Hassana ta fad'i maganar tana mai saurin rik'o hannun Habib d'in. Habib ko da al'ajabi ya bi Hassana da kallo".

Hassana ganin haka, yasa ta d'an girgiga Habib ta ce, "Wayyo Oga Habib kafara magana ko? , dan Allah ka ce wani abu, ko zanji dad'i".
Habib da ke zaune yana jin maganganun Hassana mamaki ne sosai ya cika shi, wanda yasa ya kasa cewa komai, hakan yasa yafara tunanin wai lafiya ko dai mafarki ya ke, idan kuma mafarki ne tom wacece haka tazo mai da siffar da bai sani ba".

Hassana ko ganin Habib ya yi mata shiru yana kallanta, yasa ta kuma kai hannu da niyyar ta girgiza shi. Wani ma haukacin mari Habib ya wanke Hassana dashi yana mai sake turota k'asa, ya ce, "Wacece ke?, kuma me ya shigo da ke nan? ". A hankali sosai Habib ya ke maganar.
Hassana da marin Habib ya farkar da ita ta dawo hayyacinta, da fe inda Habib ya fareta ta yi, tana kallan shi da idonta da ya kad'a ya yi ja".

Habib ko cikin d'an d'aga murya ya kuma cewa, "Fita ki bar nan kafin inyi k'asa-k'asa da ke! ". Still Hassana na tsaye dan ko motsawa bata yi ba, daga inda ta ke. Take Hassana ta shiga wani hali mai wuyar fita, dan indai dai-dai ta ke gani, kuma jinta ma dai-dai ya ke, tom tabbas Habib ya samu lafiya, dan ko daga kalar kallan da yake mata, hakan ya tabbatar mata Habib ya dawo hayyacinsa".

Habib ko ganin Hassana kamar bajin abinda ya ke cewa ta ke ba, sakkowa ya yi daga kan gadon, ya na kallan Hassana cikin ido, ya ce, "Wacece ke?, kuma me yakawo ki nan?, nace ki fita ko! ". Hassana cikin rawar murya ta fara magana, da cewa, "uhm ba komai". "Ba komai ".Habib ya mai-mai ta. Hassana d'aga ma Habib kai ta yi, ta ce, "Eh".

Kasan cewar rashin k'arfin da Habib ba ya ji ajikin shi koka d'an, dan ji yake kamar zai fad'i, dan ko maganar da yake ma Hassana da kyar yake mata ita, hakan yasa batare da Habib ya kuma cewa komai ba, ya nuna ma Hassana k'ofar fita da hannu, shi kuma ya koma bakin gadon ya zauna yana mai dafe kan shi".

Hassana juyawa ta yi ta kama hanyar fita bedroom d'in Habib, har ta kai bakin k'ofa ta juyo ta kalli Habib d'in da yake dafe da kanshi yana rirrin tse ido. Hassana da sauri ta dawo cikin bedroom d'in, dan ita har yanzu bata gama yadda Habib ya warke gaba d'aya ba. Hassana cikin damuwa da yanayin da taga Habib d'in ta kamo hannun Habib d'in ta ce, "Ayyyah Oga Habib Sannu, nasan yunwa kake ji, inda yau kak'i cin komai, in kawo ma abinci kaci? ". Habib da mamaki ya d'ago kai yana kallan Hassana, gashi abin haushi yana jin kamar baya iya magana, tsananin ciwan da kanshi ya ke. D'agowar kan da Habib ya yi Hassana ta kalli k'wayar idon shi ta ga ta yi jawur. Hassana cikin tausan Habib d'in kamar zatai kuka, dan ita harga Allah bata mai kallan wanda ya warke gaba d'aya, kawai dai tana mai kallan ciwan nashi ya canza sifiri ne. Hakan yasa Hassana ta kuma cewa, "Oga Habib in kawo ma abinci ko? ". Hassana ganin Habib ba amsa mata zai yi ba, yasa ta rabu tashi ta je kitchen ta zibo mai jolop rice d'in da ta yi, ta kawo mai, dan dan tun jiya take fama da Habib akan cin abinci yak'i".

Hassana kusa da Habib ta zauna ta d'ibo abincin a spoon, kamar yadda ta saba yi ma Habib d'in wani lotun, ta ce, "Oga Habib bud'e bakinka please kaci ko kad'an, kaga tun jiya baka ci abinci ba". Habib ko da ciwan kai ya dama, da mamaki ya ke kallan Hassana ga magana ma wuyar yi ta ke mai. Haka nan Habib cikin k'arfin hali ya ce ahankali canciki, "Kin san Allah idan har biki bar d'akin nan ba, na tashi,,,,, ". Habib ya k'arasa maganar da girgiza kai". Hassana aje abincin ta yi, tana mai k'ara gasgata maganarta ta Habib ya warke. Hakan yasa Hassana aje mai abincin ta juya ta fita. Hassana wayar da Hajiya Turai ta bata ta d'auka, ta kira Hajiya Turai, Allah ko ya tai maka, kira d'aya Hajiya Turai ta d'aga".

Hasssana cikin murna, ta gaida Hajiya Turai, bayan sun gama gaisawa ne, Hassana ta ce, "Mommy Wallahi Oga Habib ya warke,yanzu haka maganar da nake yi dake Oga Habib na magana". Hajiya Turai cikin tsantsar farinciki ta ce, "Daughter nasan ba kimin wasa, dan Allah da gaske Habib d'ina ya warke?, kuma har kinji maganar shi? ". "Mommy Oga Habib ya warke tabbas, kuma naji maganar shi". Cewar Hassana. "Tom me yace miki, daughter? ". Hassana shiru ta yi, dan sai yanzu ne ma taji zafin abinda Habib ya ce mata".

Hajiya Turai ko jin Hassana ta yi shiru ya sa, ta ce, "Hello daughter kina jina, kuwa, ba Habib d'in wayar". Hassana koma wa bedroom d'in Habib ta yi, har yanzu Habib na zaune kamar yadda ta bashshi. Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, "Oga Habib Mommy na magana a waya? ". Habib d'ago kai ya yi yana kallan Hassana, sannan jin ta ce, Mommy ya amshi wayar ya kanga a kunne, duk da yana jin kamar ba zai iya magana ba".

Hajiya Turai ko, cikin k'osawa ta ce, "Hello Habib kana jina? ". Habib cikin dauriya da jarumta da yadda ya ke ji, ya ce, "Eh Mommy inaji". Hajiya Turai cikin murya mai kama da ta kuka ta ce, "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! alhamdullah!!!, Allah nagode maka da kanuna min wannan rana, Habib kana jina? ". "Eh Mommy inaji". Habib magana ya ke so yima mahaifiyar tashi doguwa, amma ya kasa, tsabar ciwan kai".
Chapter 41 · 0% Book details