← Book details Oga Habeeb Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 42 OF 78

Sashe 42

Oga Habeeb Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hajiya Turai cikin Sanyi ta ce, "Sannu Habib Allah ya baka lafiya baki d'aya, ina nan da wowa gobe insha Allah, yanzu ba daughter wayar". Habib daughter ya mai-mai ta azuciyar shi, yana mamakin ita d'in wacece.Habib mik'ama Hassana wayar ya yi, yana mai nuna mata hanyar fita, alamun ta amshi wayar ta fita. Hassana amsar wayar ta yi ta fita, tana mai sauraran Hajiya Turai. Hajiya Turai ko ta ci gaba da cewa, "Daughter naji har yanzu bashi da lafiya, tom nasan Habib da gaddama mare in kira Family doctor mu ya duba shi, amma insha Allah gobe da wuri zan shigo". "Tom mommy Allah ya kawoki lafiya, mommy ki kira idan da akwai Wanda Oga Habib zai yarda ya kwana da shi". Cewar Hassana. Hajiya Turai cikin sauri ta ce, "Daughter ke fa? ". "Mommy wallahi ya ce in dai ya tashi ya ganni a d'akin zan sani, ni dai Mommy dan Allah part d'in ki zani in kwana". Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "Tom shikenan daughter amma dan Allah da safe ki yi k'ok'ari kizo da wuri ki duba shii, dama Bilya na nan ne, tom kinga Bilya na zaria, amma zan kira shi yanzu in ce mai yadawo gobe". Hajiya Turai kashe wayar ta yi".

Hassana ko juyawa ta yi ta fita , ta nufi part d'in Hajiya Turai".

B'angaran Habib ko da kyar ya iya tashi ya d'auki abincin da Hassana ta kawo mai ya ci. Habib na gama cin abincin wani wahalallan bacci ya d'auke shi.
Shine fa Habib bashi ya farka ba, sai washe gari, dalilin Farida".

Farida na shiga gidansu Oga Habib, tsayawa ta yi dai-dai k'ofar Falon Habib d'in, ta ciro maganin da boka ya bata ya ce, ta tauna duk abinda ta ce ma Habib zai yi. Aiko haka Farida ta ciro maganin ta tauna, sannan ta ciro wanda ya bata ya ce duk abinda tasa Hassana ba za ta yi mata gadda ma ba, shima ta tauna, sannan ta d'akko na wanke fuskar ta wanke fuskarta, shi kuma wanda ya ce, duk wani aibunta da ya hana Habib d'in ya so ta, tom kamar shine ta wanke. Farida nagama magungunan ta, ta fara nocking d'in k'ofar falon Habib da k'arfi".

Habib da tun baccin jiya da ya kwanta bai tashi ba, bayan ya gama cin abincin da Hassana ta kawo mai. Habib cikin bacci ya jiyo yadda ake bun k'ofar, cikin mamaki da al'ajabi Habib ya tashi, Alhamdulillah yau sosai yaji k'arfin jikin shi, sai abinda ba'arasa ba, Habib cikin sauri yanu fa k'ofar dan ganin mara hankalin da yake mai nocking haka. Habib na zuwa cikin fad'a-fad'a ya ce, "Wa ye? ". Farida da k'osawa ta sa ta kasa fahimtar muryar waye, ta ce, cikin k'osawa, kuma ita ma cikin fad'a-fad'an dan ta zaci Hassana ce, ta ce, "Bud'e ki gani mana, 'yar rainin hankali, daga yau ne dai". Habib cikin b'acin rai ya bud'e k'ofar, yana kallan Farida fuska d'aure babu alamun fara'a ya ce, "Farida dama nafara wasa da ke? ". Farida cikin al'abi da mamaki ta ke kallan Habib, kai ko dai maganin da boka ya bani ne ya warkar da shi, tun kafin in sa mai, Farida kallan Habib ta yi tana sosa k'eya ta ce, "Oga Habib dama wata magana ce nake so muyi dan Allah ". Habib ko da mamaki ya kalli Farida, amma ganin sammakon da tayi, da kuma yana son tambayarta dan yana buk'atar amsar tambayar shi kafin Hajiya Turai ta dawo. Habib cema Farida ya yi, "Ok, inajinki? ". Farida ko najin haka ta kuma tabbatar da maganinta ya yi wato yana jinta, Lallai wata sabon gani, hakan yasa Farida dan k'ara tabbatarwa ta ce, "Uhm Oga Habib dan Allah mu shiga daga ciki mana? ". Habib batare da yayi ma Farida musu ba, yashiga, Farida kuma tabi bayan Habib tana mai tabbatar da aiki yagama yi".

Habib kallan Farida ya yi, alamun inajinki. Farida cikin bada umarni, ta ce, "Oga Habib so nake ka saki Hassana yau-yau d'innan ". Habib da mamaki ya ke kallan Farida. Farida kuma ganin Habib na kallata ta ce, "Ko ba zaka iya bane? ". Habib shiru ya yi, na farko abinda ya bashi mamaki ganin yadda Farida ke mai magana cikin bada Umarni, na biyu kuma, tabbas yarinyar da yagani jiya ita ce Hassanar, idan ita ce, tom meye dangan takar shi da ita? ".

Farida ko ganin Habib ya shiga kogon tunanin, ya sa ta kuma cewa, "Oga Habib dan Allah kai nake jira, kace ka saki Hassana saki Uku, idan Mommy ta tambaye ka kace mata kai bazaka iya zaman aure da ita ba, kai ni kake so".
Habib dafe ganshi ya yi, dan tabbas ko a yadda ya ke jin jikin shi ya tabbatar mai akwai abinda ke faruwa dashi, jiya ya farka yaga wata atare dashi ad'akin shi, yau kuma wannan ma haukaciyar tazo tana mai wasu maganganu marasa ma'ana, Habib kallan Farida ta yi, ya ce, " Tom jeki zanyi". Habib ya ce ma Farida haka ne kawai dan baya son ya kuma jin wata maganar da zata k'ara mai wani tunanin, hakan yasa ya ce ma Farida, tom ta je zai yi".Farida fita tayi tana mai jin dad'in furicin Habib, dan tabbas aiki ya yi, dan idan ba haka ba, tasan Habib sare da yazun ya yi maganin ta".

Habib ko zama ya yi shi kad'ai yama rasa kalar tunanin da zai yi, wai meke faruwa da shine?, me Farida ke nufi ne?".

Habib wayar shi ya fara naima ya kira Bilya dan samun amsoshin tambayoyin shi. Babu inda Habib be duba ba, amma ba wayar shi. Toilet ya shiga ya yi wanka, bayan ya fito ne ya shafa lotion ajikin shi, sannan ya bud'e sip d'in kayan shi, amma abinda ya bashi mamaki kayan mace agefan kayan shi, Habib cikin al'ajabi da mamaki ya ke bin kayan Hassana da kallo. Habib daurewa ya yi ya kauda komai, ya ciro kayan shi ya sa, ya adana tambayoyin shi sai Hajiya Turai ta dawo, amma tabbas ya san akwai babban al'amari da ke faruwa da shi, ko kuma ya faru da shi, dan ko yana yin yadda yake jin jikin shi yana kuma tabbatar mai da hakan.
Bayan Habib ya gama shiryawa, kitchen ya shiga, nanma yasha mamaki, nan ma dai haka ya kauda mamakin shi gefe ya had'a ma kanshi tea ya fito".

K'arfe goma sha d'aya na safiya jirgin su Hajiya Turai ya sauka. Kasan cewar Hajiya Turai ta san Bilya baya nan, yasa ta d'au drop d'in mota ta kawota gida".

Hajiya Turai direct part d'in Habib ta nufa. Habib na kwance ya ji nocking , ya zo sai dai sosai abin yazo mai a ba zata, dan bai yi tunanin dadowar Hajiya Turai yau ba , dan bata cewa gata nan tazo sai tai sati tana sa rana".

Hajiya Turai cikin tsantsar farincin da ta kasa b'oyewa ta rungume Habib tana mai cewa, "Alhamdulillah, tabbas duk abinda ya yi farko zai yi k'arshe, kuma babu abinda ya gagari Allah, Sannu Habib Allah yasa wannan ce k'arshen wahalarka a duniya da lahira"."Ameen Mommyna, mu shiga ciki ki futa".

Hajiya Turai tana rik'e da hannun Habib suka shiga ciki, Hajiya Turai zata zauna kenan, Habib ya ce, "Mommy karki zauna zoki ga wani abu". Hajiya Turai tashi ta yi ta bi Habib".

Habib ko wajan sip d'in kayan shi ya kai Hajiya Turai, bud'e sip d'in ya yi, sannan ya ce, yana mai nuna kayan Hassana ya ce, "Mommy kayan Waye nan?". Hajiya Turai kallan Kayan Hassana ta yi, dake jere kusa da na Habib. Hajiya Turai kama hannun Habib ta yi, ta ce,............ ✍️.

In kin karanta daure ki yi Comment sister 🤝.

Share
&
Comment please 🙏.

💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*

https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl

_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_

*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*
TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby).

https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7

https://m.facebook.com/groups/565235401564189/

Shafi na 50&51.

Hajiya Turai kama hannun Habib ta yi, ta ce" Habib ka yi hak'uri in nasamu natsuwa zuwa anjima sai mu yi magana". Habib da tom ya amsa ma ma haifiyar shi ba dan ya so ba, so ya yi ta bashi amsa yanzu. Hajiya Turai kallan Habib ta yi ta ce, "Bari in shiga ciki, zuwa anjima sai kazo muyi maganar inda naga ka matsu". "A'a Mommy ba wai na matsu bane, kawai dai ina mamakin yadda kayan mace ya had'u da kayana ne waje d'aya, kuma na farka naganta anan, tom shine abin ke ban mamaki, kuma duk bansan ta yadda hakan ta faruba, sannan yau Farida ta zo mun da wata magana wadda ta kuma tabbatar min da akwai wani b'oyayye al'amari da ke faruwa". Habib ya idasa maganar cikin damuwa. Hajiya Turai kallan Habib ta yi, sannan ta ce, "Shikenan ni zan shiga ciki, kasaman anjima kamar yadda na ce ma, sai muyi maganar".

Hajiya Turai fita ta yi daga side d'in Habib ta nufi nata part d'in. Hassana na kwance tun da ta tashi da safe ta ke kwance kan caution, haka nan Hassana ke jinta wani iri duk ba dad'i, kamar a mafarki Hassana ta ji sallamar Hajiya Turai. Hassana cikin nuna murnarta naganin Hajiya Turai ta tashi ta zauna tana, "Oyoyo Mommy". Hajiya Turai murmushi ta yi tace, "Oyoyo daughter". Hassana cikin fad'ad'a fara'ar fuskarta suka gaisa da Hajiya Turai. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter ya k'ok'ari na tafi na barki da mara lafiya, ikon Allah yau satina biyu kenan da tafiya". "Kai Mommy har kin yi sati biyu? ". Cewar Hassana. "Eh daughter, bari in shiga ciki in watsa ruwa in kwanta ". Hajiya Turai bedroom d'in ta ta shiga ta watsa ruwa sannan ta kwanta".
Chapter 42 · 0% Book details