Sashe 46
Oga Habeeb Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
B'angaran Farida ko tana isa gidan Hajiya Murja, ta wurga ma Hajiya Murja letter da Hajiya Turai ta ba Hassana, ta ce, "Mommy nikam nagaji!, sai yaushe zan zama mai sa'ane, kince muje wajan wancan wai shi mai biyan buk'ata dole, ya ce sai Oga Habib ya yi hauka zan samu in aure hankali kwance, ya yi haukarshi ya gama k'arshe mai-mai kon a had'a auran da ni da wata aka had'a, yanzu munyi takakkiya munje gun wannan shima kinga shirman da yabamu, nifa nagaji zan yanke hukuncin da zai min dai-dai in huta da rayuwar bak'incikin nan da nake, Mommy koda yaushe ina fad'a miki Oga Habib shine cikar farincikina, duk wani farinciki indai ba ina tare da shiba tom jabu ne, dan haka ni yau d'in nan zan yanke hukuncina na k'arshe! ". Hajiya Murja sosai hankalinta ya tashi da furincin Farida dan ta san Farida babu wani hukuncin da zata yanke wanda ya wuce ta ce zata tafi ta barta".
Hajiya Murja hannun Farida ta kama ta ce, "Farida ki yi hak'uri kinji, bari in kira Hajiya Zaliha in mata bayanin halinda nake ciki nasan zata tai maka min da wani abun".
Hajiya Murja wayrta ta d'auka ta kira Hajiya Zaliha kamar yadda ta ce. Hajiya Zaliha na d'aga Kiran Hajiya Murja tai mata bayanin halinda ta ke ciki. Hajiya Zaliha cewa ta yi ta bari anjima zata shigo unguwar zata biyo".
Hajiya Murja kallan Farida ta yi ta ce, "Farida ki yi hak'uri kamar yadda kika ji nace miki, indai kika sa hak'uri aure zakaninki da Habib babu fashi, kinga ma dai shi Habib ba son yarinyar ya ke ba, son Hajiya Turai ko ai na banza ne inda ba ita zata zauna mai da ita ba, dan haka ke dai ki yi hak'uri ki ban nan da isowar Hajiya Zaliha". Hajiya Murja na nan sai aikin ba Farida baki take, sunanan zaune Hajiya Zaliha ta iso.
Bayan sun gaggaisa ne Hajiya Zaliha ta kalli Hajiya Murja ta ce, "Hajiya naji duk ba yaninki, amma yanzu zamu gwada da basirar da Allah ya bamu ne, dama ai k'issar baka tafi ta malam, dan haka inda Malaman sun kasa sai mu yi da k'isssar mu ta mata". Hajiya Zaliha kallan Farida ta yi, ta ce, " Haba Daughter kina so kiban kunya sai kace wata 'yar kyauye, yanzu ke baza ki iya yaudarar namiji da kalaman bakinki ba ya soki, sai kin had'ashi da Malam, Tom ni Wallahi a zamanina da kallo nake yaudarar d'a namiji, bare ke da kike da dama kina zaune gidansu. Yanzu dai ki bud'e kunnanki da kyau ji ji abinda zan fad'amiki, amma fa sai kin jure, dan shi dama mai nema sai ya jure indai kika sa juriya tom zakiga ribar abin. Yanzu dai da farko zakina yawan tusa kanki aduk abinda ya shafi Habib agidan, amma zaki yi abin a Sannu, dan karki kuskura kina nuna zak'ewa wajan tusa kanki,duk wani abu da ya dan ganci Habib ki yi k'ok'ari ya kasance ke zaki mai, ke idan zai yuwuma duk wani abu nashi ya dawo hannunki, ita kuma yarinyar dama kunce ba sonta ya ke ba, zakina nuna rashin iyawarta duk abinda tai a gabanshi, ko da ya yi kinuna mata ba haka ake ba. Shi kuma Habib d'in kina nuna mai kina jin tausan shi na had'a shi da yarinyar da akai , dan kwata-kwata ba ajinshi ba ce". Hajiya Zaliha kallan Farida ta yi ta ce, "Daughter ina fatan kina fahim tata?, yawan kwalliya ko ki dage da saka kayan da zaija hankalinshi, ita ko yarinyar in ma mai son kwalliya ce ki sanyadda zaki kina hanata".
Farida cikin jin dad'i ta rungume Hajiya Zaliha, ta ce, "Wayyo Mommy, dama nasan hakane ai da tuntuni gunki nazo da yanzu na auri Oga Habib anwuce gun".Dariya Hajiya Zaliha ta yi, ta ce, "Banni da shi daughter, k'aryar muskilanci yake. Sannan kina yawan kirana awaya ina k'ara miki wasu darisan".
Hajiya Zaliha ta dad'e tana kuma koyama Hassana dabarun da zata ja hankalin Habib, batare da ta had'a shi da boka ba ko malam".
Farida ko nagama jin k'issoshin da Hajiya Zaliha ta koya mata, ta tashi ta ce, "Ai tafiyama za tai".
B'angaran Habib ko bayan sun isa Sanat yughurt, kallan Bilya ya yi, ya ce, "Bilya ka tabbatar da yarinyar nan gobe tazo aiki! ". Magana Bilya ya ke son yima Habib amma baiga fuska ba, sai dai cewa ya yi, "Tom insha Allah Oga Habib".
B'angaran Hassana ko tsabar kukan da ta yi ne ya saukar mata da ciwan kai, hakan yasa ta kwanta, ba ita ta farka ba sai azahar, bayan ta yi sallah ne ta je derning space ta ci abinci, duk da bawani na kirki ta ci ba, danma yunwa ta ke ji inda tun jiya rabon ta da abinci".
Gaf da magriba Farida ta shigo gidan. Sai dai ko da tazo Falon bataga Hassana ba, hakan yasa ta zarce room d'in ta, wanka Farida ta yi sannan ta zauna ta rangad'a kwalliya kamar mai shirin zuwa gasar kyau. Falo Farida ta dawo ta zauna, duk da tana mai fargabar kar Habib yak'i ganin wannan wankan, inda in Hajiya Turai bata nan Habib ba ya dawowa da wuri. Farida na nan zaune Hassana ta fi to ta nufi kitchen tana son had'a tea dan shi kawai ta ke jin zata iya sha".
Hassana wucewa ta zo yi zata shiga kitchen, Farida ta ce, "Ke! ". Hassana juyowa ta yi tana kallan Farida, amma harga zuciyarta bata jin dad'in ke d'in da Farida ke ce mata ba".
Farida kallan Hassana ta yi, ta ce, "Ki taho min da abinda zanci". "Tom". Hassana ta ce, ta juya ta shiga kitchen ta had'a tea d'in ta, sanann ta d'iboma Farida abincin ta kai mata . Hassana mik'ama Farida abincin ta yi ta tafi, Farida kallan Hassana ta yi, ta ce, "Da hannunki zan ci? ". Hassana batare da ta tanta mata ba, ta koma kitchen ta d'akko mata spoon ta kawo mata".
Washe gari da wuri Bilya ya shigo falon Hajiya Turai yana sallama. Hassana da taji yo sallamar Bilya , fitowa ta yi, bayan sun gaisa ne Bilya ya kalli Hassana ya ce, "Dama Oga Habib ne ya aikoni ya ce, "Yau ki je aiki". Bilya na fad'ima Hassana haka ya juya ya fita".
Hassana dama ta yi wankanta, cikin kayan da Hajiya Turai ta sai mata, ta d'akko wata abaya da yake duk kusan dogayan riguma ne, tasa. Sannan ta d'auki ma yafin rigar da yake yana da girma ta yafa, takama hanya zata tafi.
Farida da fitowarta kenan, kallan Hassana ta yi damamaki ta ce, " Ke ina zaki? ". Hassana batare da ta kalli Farida ba ta ce, "Aiki". Hassana na fad'in haka ta juya ta tafi abinta. Tabar Farida gun tsaye, ko ba komai taji dad'in hakan dan hakan ya tabbatar mata Habib bai damu da Hassana ba".
Hassana ko kasan cewar babu kud'i a hannunta wajan Jimmai ta je. Jimmai da murnarta ta rungume Hassana ta ce, "Dama talaka irin mu na ganinki!, Wallahi bacin sanin da naimi ba d'an ka d'an bane da babu yadda za ai in gane ki. Hassana kinganki ko yadda kika dawo, kinyi fari kinyi k'iba.. ". Hassana murmushi ta yi, ta ce, "Uhm Sister Jimmai kenan, ni wata k'iba zan wani yi, ni dai yanzu sauri nake ban 1k a kud'innan,". Shiru Jimmai ta yi tana kallan Hassana, sannan ta kauda tunanin da ta ke yi, ta ce, "Wai Hassana ina zaki ne haka? ". "Aiki zani". Cewar Hassana ".
Jimmai kallan Hassana ta yi da alamun mamaki a tattare da ita, ta ce, "Aiki kuma?". "Sister Jimmai ban dan Allah, Allah akwai damuwa idan na je late". Cewar Hassana ".
Jimmai kallan Hassana ta yi da alamun tuhuma, ta ce, "Hassana ni na san jin sauk'in Oga Habib zaki fuskanci abubuwa da yawa agun Oga Habib, sannan zaki fuskanta agun Aunty Farida ma. Hassana ya auranki da Oga Habib yana nan ko ba ya nan?". "Bayanan". Hassana ta ba jimmai amsa. Jimmai kallan Hassana ta yi ta ce, "Bana son maganar wasa dan Allah, Hajiya ta raba auran ne koko? ".
Hassana shiru ta yi sannan ta kalli Jimmai ta ce, "Sister Jmmai dan Allah kiban in tafi, idan nadawo zanzo muyi magana". Jimmai shiga ta yi ta d'akkoma Hassana 1k kamar yadda ta ce, ta ba ta. Sannan Hassana ta tafi".
Hassana ba ita ta je Sanat yughurt ba sai 11:15PM. Abinda Hassana ko bata sani ba tuni Billy ta canza wata madadin Hassana. Hassana ko da ta je Sanat yughurt stuff's d'in gurin wa inda suka saba da da ita, da murnarsu suka tarbi Hassana suna tambayarta lafiya tabar zuwa shiru haka? ".
Duk wanda ya tambayi Hassana sai ta ce mai batada lafiya ne. Dariya sosai sukayi sannan Amina wadda tasu tafi zuwa d'aya da Hassana, ta kalli Hassana ta ce, "Sister ki canza wata k'aryar, amma wannan bata amsu ba, kallakki fa, yadda ki kai kyau, kika wani canza kamanni, da kyar muka iya gane ki, bacin ma wannan voice d'in taki da bazamu shaidaki ba, amma shine zaki wani ce mana kinyi ciwo ne ".ita dai Hassana murmushi kawai tai masu, sannan ta ce, "Ni yanzu tunanina d'aya yadda zamu k'arke da supervisor". Amina dariya ta yi, ta ce, "kuma kinsan rashin mutuncinta sai abinda ya yi gaba, dan Wallahi muna ganin mulkin mallaka".
Hassana kallan Amina ta yi, ta ce, "Sister Amina yanzu ya zanyi?, in da kince ta maida wata a mazaunina? ". "Zuwa zakiyi ki sa me ta sai ki mata bayanin rashin zuwaniki, amma fa karki ce mata ciwo kikai kamar yadda kika ce mana, dan Wallahi ba zata yarda ba, garama kice mata tafiya ce ta kamaki lokaci guda, k'ila idan kikaci sa'a ta yadda ki ci gaba da aiki".
Hajiya Murja hannun Farida ta kama ta ce, "Farida ki yi hak'uri kinji, bari in kira Hajiya Zaliha in mata bayanin halinda nake ciki nasan zata tai maka min da wani abun".
Hajiya Murja wayrta ta d'auka ta kira Hajiya Zaliha kamar yadda ta ce. Hajiya Zaliha na d'aga Kiran Hajiya Murja tai mata bayanin halinda ta ke ciki. Hajiya Zaliha cewa ta yi ta bari anjima zata shigo unguwar zata biyo".
Hajiya Murja kallan Farida ta yi ta ce, "Farida ki yi hak'uri kamar yadda kika ji nace miki, indai kika sa hak'uri aure zakaninki da Habib babu fashi, kinga ma dai shi Habib ba son yarinyar ya ke ba, son Hajiya Turai ko ai na banza ne inda ba ita zata zauna mai da ita ba, dan haka ke dai ki yi hak'uri ki ban nan da isowar Hajiya Zaliha". Hajiya Murja na nan sai aikin ba Farida baki take, sunanan zaune Hajiya Zaliha ta iso.
Bayan sun gaggaisa ne Hajiya Zaliha ta kalli Hajiya Murja ta ce, "Hajiya naji duk ba yaninki, amma yanzu zamu gwada da basirar da Allah ya bamu ne, dama ai k'issar baka tafi ta malam, dan haka inda Malaman sun kasa sai mu yi da k'isssar mu ta mata". Hajiya Zaliha kallan Farida ta yi, ta ce, " Haba Daughter kina so kiban kunya sai kace wata 'yar kyauye, yanzu ke baza ki iya yaudarar namiji da kalaman bakinki ba ya soki, sai kin had'ashi da Malam, Tom ni Wallahi a zamanina da kallo nake yaudarar d'a namiji, bare ke da kike da dama kina zaune gidansu. Yanzu dai ki bud'e kunnanki da kyau ji ji abinda zan fad'amiki, amma fa sai kin jure, dan shi dama mai nema sai ya jure indai kika sa juriya tom zakiga ribar abin. Yanzu dai da farko zakina yawan tusa kanki aduk abinda ya shafi Habib agidan, amma zaki yi abin a Sannu, dan karki kuskura kina nuna zak'ewa wajan tusa kanki,duk wani abu da ya dan ganci Habib ki yi k'ok'ari ya kasance ke zaki mai, ke idan zai yuwuma duk wani abu nashi ya dawo hannunki, ita kuma yarinyar dama kunce ba sonta ya ke ba, zakina nuna rashin iyawarta duk abinda tai a gabanshi, ko da ya yi kinuna mata ba haka ake ba. Shi kuma Habib d'in kina nuna mai kina jin tausan shi na had'a shi da yarinyar da akai , dan kwata-kwata ba ajinshi ba ce". Hajiya Zaliha kallan Farida ta yi ta ce, "Daughter ina fatan kina fahim tata?, yawan kwalliya ko ki dage da saka kayan da zaija hankalinshi, ita ko yarinyar in ma mai son kwalliya ce ki sanyadda zaki kina hanata".
Farida cikin jin dad'i ta rungume Hajiya Zaliha, ta ce, "Wayyo Mommy, dama nasan hakane ai da tuntuni gunki nazo da yanzu na auri Oga Habib anwuce gun".Dariya Hajiya Zaliha ta yi, ta ce, "Banni da shi daughter, k'aryar muskilanci yake. Sannan kina yawan kirana awaya ina k'ara miki wasu darisan".
Hajiya Zaliha ta dad'e tana kuma koyama Hassana dabarun da zata ja hankalin Habib, batare da ta had'a shi da boka ba ko malam".
Farida ko nagama jin k'issoshin da Hajiya Zaliha ta koya mata, ta tashi ta ce, "Ai tafiyama za tai".
B'angaran Habib ko bayan sun isa Sanat yughurt, kallan Bilya ya yi, ya ce, "Bilya ka tabbatar da yarinyar nan gobe tazo aiki! ". Magana Bilya ya ke son yima Habib amma baiga fuska ba, sai dai cewa ya yi, "Tom insha Allah Oga Habib".
B'angaran Hassana ko tsabar kukan da ta yi ne ya saukar mata da ciwan kai, hakan yasa ta kwanta, ba ita ta farka ba sai azahar, bayan ta yi sallah ne ta je derning space ta ci abinci, duk da bawani na kirki ta ci ba, danma yunwa ta ke ji inda tun jiya rabon ta da abinci".
Gaf da magriba Farida ta shigo gidan. Sai dai ko da tazo Falon bataga Hassana ba, hakan yasa ta zarce room d'in ta, wanka Farida ta yi sannan ta zauna ta rangad'a kwalliya kamar mai shirin zuwa gasar kyau. Falo Farida ta dawo ta zauna, duk da tana mai fargabar kar Habib yak'i ganin wannan wankan, inda in Hajiya Turai bata nan Habib ba ya dawowa da wuri. Farida na nan zaune Hassana ta fi to ta nufi kitchen tana son had'a tea dan shi kawai ta ke jin zata iya sha".
Hassana wucewa ta zo yi zata shiga kitchen, Farida ta ce, "Ke! ". Hassana juyowa ta yi tana kallan Farida, amma harga zuciyarta bata jin dad'in ke d'in da Farida ke ce mata ba".
Farida kallan Hassana ta yi, ta ce, "Ki taho min da abinda zanci". "Tom". Hassana ta ce, ta juya ta shiga kitchen ta had'a tea d'in ta, sanann ta d'iboma Farida abincin ta kai mata . Hassana mik'ama Farida abincin ta yi ta tafi, Farida kallan Hassana ta yi, ta ce, "Da hannunki zan ci? ". Hassana batare da ta tanta mata ba, ta koma kitchen ta d'akko mata spoon ta kawo mata".
Washe gari da wuri Bilya ya shigo falon Hajiya Turai yana sallama. Hassana da taji yo sallamar Bilya , fitowa ta yi, bayan sun gaisa ne Bilya ya kalli Hassana ya ce, "Dama Oga Habib ne ya aikoni ya ce, "Yau ki je aiki". Bilya na fad'ima Hassana haka ya juya ya fita".
Hassana dama ta yi wankanta, cikin kayan da Hajiya Turai ta sai mata, ta d'akko wata abaya da yake duk kusan dogayan riguma ne, tasa. Sannan ta d'auki ma yafin rigar da yake yana da girma ta yafa, takama hanya zata tafi.
Farida da fitowarta kenan, kallan Hassana ta yi damamaki ta ce, " Ke ina zaki? ". Hassana batare da ta kalli Farida ba ta ce, "Aiki". Hassana na fad'in haka ta juya ta tafi abinta. Tabar Farida gun tsaye, ko ba komai taji dad'in hakan dan hakan ya tabbatar mata Habib bai damu da Hassana ba".
Hassana ko kasan cewar babu kud'i a hannunta wajan Jimmai ta je. Jimmai da murnarta ta rungume Hassana ta ce, "Dama talaka irin mu na ganinki!, Wallahi bacin sanin da naimi ba d'an ka d'an bane da babu yadda za ai in gane ki. Hassana kinganki ko yadda kika dawo, kinyi fari kinyi k'iba.. ". Hassana murmushi ta yi, ta ce, "Uhm Sister Jimmai kenan, ni wata k'iba zan wani yi, ni dai yanzu sauri nake ban 1k a kud'innan,". Shiru Jimmai ta yi tana kallan Hassana, sannan ta kauda tunanin da ta ke yi, ta ce, "Wai Hassana ina zaki ne haka? ". "Aiki zani". Cewar Hassana ".
Jimmai kallan Hassana ta yi da alamun mamaki a tattare da ita, ta ce, "Aiki kuma?". "Sister Jimmai ban dan Allah, Allah akwai damuwa idan na je late". Cewar Hassana ".
Jimmai kallan Hassana ta yi da alamun tuhuma, ta ce, "Hassana ni na san jin sauk'in Oga Habib zaki fuskanci abubuwa da yawa agun Oga Habib, sannan zaki fuskanta agun Aunty Farida ma. Hassana ya auranki da Oga Habib yana nan ko ba ya nan?". "Bayanan". Hassana ta ba jimmai amsa. Jimmai kallan Hassana ta yi ta ce, "Bana son maganar wasa dan Allah, Hajiya ta raba auran ne koko? ".
Hassana shiru ta yi sannan ta kalli Jimmai ta ce, "Sister Jmmai dan Allah kiban in tafi, idan nadawo zanzo muyi magana". Jimmai shiga ta yi ta d'akkoma Hassana 1k kamar yadda ta ce, ta ba ta. Sannan Hassana ta tafi".
Hassana ba ita ta je Sanat yughurt ba sai 11:15PM. Abinda Hassana ko bata sani ba tuni Billy ta canza wata madadin Hassana. Hassana ko da ta je Sanat yughurt stuff's d'in gurin wa inda suka saba da da ita, da murnarsu suka tarbi Hassana suna tambayarta lafiya tabar zuwa shiru haka? ".
Duk wanda ya tambayi Hassana sai ta ce mai batada lafiya ne. Dariya sosai sukayi sannan Amina wadda tasu tafi zuwa d'aya da Hassana, ta kalli Hassana ta ce, "Sister ki canza wata k'aryar, amma wannan bata amsu ba, kallakki fa, yadda ki kai kyau, kika wani canza kamanni, da kyar muka iya gane ki, bacin ma wannan voice d'in taki da bazamu shaidaki ba, amma shine zaki wani ce mana kinyi ciwo ne ".ita dai Hassana murmushi kawai tai masu, sannan ta ce, "Ni yanzu tunanina d'aya yadda zamu k'arke da supervisor". Amina dariya ta yi, ta ce, "kuma kinsan rashin mutuncinta sai abinda ya yi gaba, dan Wallahi muna ganin mulkin mallaka".
Hassana kallan Amina ta yi, ta ce, "Sister Amina yanzu ya zanyi?, in da kince ta maida wata a mazaunina? ". "Zuwa zakiyi ki sa me ta sai ki mata bayanin rashin zuwaniki, amma fa karki ce mata ciwo kikai kamar yadda kika ce mana, dan Wallahi ba zata yarda ba, garama kice mata tafiya ce ta kamaki lokaci guda, k'ila idan kikaci sa'a ta yadda ki ci gaba da aiki".