← Book details Oga Habeeb Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 40 OF 78

Sashe 40

Oga Habeeb Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hajiya Turai ko tana ganin kiran Farida da gangan tak'i d'agawa, dan ta tsani Farida Sosai, kawai dai ita Allah ya yo ta mai kawai cice sai kai ta cutarta ta. Hajiya Turai ganin Farida tak'i daina kiranta, kashe wayar ta yi gaba d'aya ".

Farida ko koda ta k'ara kiran Hajiya Turai ta ji wayar kashe ba tai tunanin komai ba, dan atunaninta suna wani programs d'in ne, kamar yadda ta tab'a fad'a mata, in dai kakira kaga bata d'aga ba tom suna bakin aiki ne. Hakan yasa Farida ba tai tunanin komai ba, tunaninta ya bata kawai Hajiya Turai na bakin aiki ne".

Farida Mahaifiyarta ta sake kira ta shaida mata ta kira Hajiya Turai bata d'aga ba, dan haka ta bata wata shawar". Hajiya Murya cema Farida ta yi,"Farida ki yi hak'uri zuwa anjima sai ki kuma kiran Hajiya Turai awaya, kin san in tana kan aiki bata amsa kira".

Farida tom kawai ta ce ma Mahaifiyarya ta kashe kiran, Farida d'akinta ta shiga ta kwanta tana ta malele kuwa , dan jinta ta ke indai ba Hassana ta bar gidan ba, tom bata da sauran na tsuwa, bakamar yau ba da Hassana ta kuma in gizata, dan ta yi ran tsuwar sai ta nuna ma Hassana ruwa ba tsaran kwando bane. Farida da ke kwance da sauri ta ta shi Saboda wani tunanin da yazo mata, hakan yasa ta tashi da sauri ta nufi site d'in worker's d'in gidan"..

Farida tsaye ta yi tana Waige-waige, tana nai man wadda tazo gani, cikin sa'a Farida ta hangota tana shanya. Farida da sauri ta k'arasa inda ta ke, cikin sakin fuska, Farida ta kalleta ta ce, Sannu ko? ". "Yauwa Aunty Farida Sannu". Farida cikin sakin fuska ba irin yadda ta saba yima worker's d'in magana ba, ta ce, "Yauwa dan Allah ya sunan ki". Jimmai da mamaki ya cika ta, tun zuwan Farida gurinta, ta ce, "Sunana Jummai". Farida cikin yaudara irin na wayayyun mata ta ce, "Wow nice name, tom dan Allah Jimmai wani tai mako zaki min, zan biyaki konawa ne, na zab'eki kimin wannan aikin ne, Saboda na lura duk gidan nan babu wadda ta fi kusanci da Hassana kamar ke, tom dan Allah Jimmai zaki min wani taimako ne, ba mai wani wuya ba ne".Farida maganin da ke jikin zaninta ta ciro ta mik'ama Jimmai ta ce, "Jimmai dan Allah zaki barbad'amin maganin nan ne, a part d'in Oga Habib". Jimmai ta ke tsoro ya kamata ta ja da baya tana mai mak'e hannunta ta k'i amsar maganin, dan sosai ta tsorata da jin abinda Farida ta ce".

Farida ko ganin Jimmai ta tsorata da maganin da ta ke mik'o mata, murmushi ta yi, ta ce, "Malama Jimmai karkiji komai ba maganin cutarwa bane, na san dai kin san ina son Oga Habib, dan nasan duk wanda yake agidan nan yasani, tom maganin nan da kike gani Jimmai bana cutarwa bane, idan ma k'awarki kike ji, itama ba cutar da ita maganin zai yi ba, ni nai miki alk'awari babu abinda zai samu k'awarki, na naimi kimin hakane dan nasan ke kad'ai ce agidan nan ayanzu zaki iya shiga part d'in Oga Habib kai tsaye, dan Allah ki tai makamin ki amsa".

Jimmai da ke tsaye al'ajabi ya isheta, amsar maganin ta yi tana ma jin tsoran karna cutarwa ne ya fara aiki akanta".

Dubu goma Farida taba Jimmai , ta ce, "Wannan ba biyanki nai ba, sai kin cika aiki sannan nima zan cika ki da abin arzik'i kala-kala".

Jimmai godiya taima Farida, ta amshi kud'in , Farida kuma ta wuce tana mai jin dad'in burinta ya kusa cika".

Jimmai ko tana ganin Farida ta wuce ta yi sauri ta shiga toilet ta jefa maganin, dan acewarta idan na zutarwa ne k'ilama ita zai fara cutarwa ita da take rik'e da shi. Jimmai sai da ta jefar da maganin sannan ta ji hankalinta ya kwanta. Murmushi ta yi, ta ce, "Aunty Farida baki da arzik'in da zaki ban kisa in zutar da Oga Habib bare kuma Hassana, ya Allah na godema da ka ba ma wannan baiwar taka zuwa guna, bata je inda zata bata ba burinta ya cika, Allah kaika san mai take nema da yarinyar nan, Allah kakareta daga shairinta, duk abinda zata mata Allah ka mai da mata aniyarta". Jimmai zama ta yi gun tana sake yima Hassana addu'a, akan Allah ya kareta daga shairin Farida."

WASHE GARI:
Farida da wuri ta yi sammakon zuwa gun Jimmai jin shiru bata ga Hassana ba, dan acewar in dai magani ya yi Habib ya kusanci Hassana ai ya isa ace ta ji alamun motsin Hassana. In da in dai akan yadda Malam mai biyan buk'ata dole ya ce musu ne, Hassana da kanta zata bar gidan, wata zuciyar kuma sai ta ce mata" tom koma Hassana ta bar gidan baki sani ba ne bama". Hakan yasa Farida zuwa ta tambayi Jimmai. Farida har cikin d'akin su Jimmai ta shiga ta kira Jimmai".

Farida kallan Jimmai ta yi, ta ce, "Jimmai na ce kin ko zubamusu maganin? ". "Eh Aunty Farida na zuba". Farida cikin jin dad'i ta juya ta nufi part d'in Habib, Farida na zuwa ta yi nocking d'in k'ofar, ta ji shiru ta kuma yi nan ma shiru".

Hassana ko lokacin ko tashi basu yi ba, dan takan dad'e tana addu'ar in ta idar da sallar asuba, hakan yasa idan ta koma baccin safe ta ke jimawa. Hassana cikin bacci ta ji bugun k'ofa, da saurinta ta tazo dan jin waye. Hassana na zuwa cikin murya mai kama da ta bacci ta ce, "Waye? ". Farida sumar tsaye ta yi, tana tunanin tom idan rannan ance Mommy ta ce ci Hassana yau kuma fa, yau dai daga ita sai Oga Habib, "anya ko maganin mutumin nan nayi?".Farida ta tambayi kanta, dan acewarta ba zai yuwu ba, ace haka na faruwa, sai dai in ko Malamin k'arya ne". Farida shiru ta yi bata amsa ma Hassana ba tabar gurin, tana zuwa ta kira Mahaifiyarta awaya ta ce, ta shirya gata nan zuwa kuma Wallahi yau babu abinda zai hanata zuwa Nijar, dama tun farko Mommy na ce miki bana son aiki irin wannan k'ila wa k'ala, tom gashi nan dai Oga Habib bai kusanci 'yar iskar yarinyar nan ba, dan haka gani nan yanzu ki shirya Wallahi bazan bari Hajiya ta dawo ta isketa a gidan nan ba". Hajiya Murja ko da bata da abin cewa wanda ya wuce ta yi biyayya da abinda Farida ta ce , ta ce, "Shikenan Farida ki zo tom dan nasan kona ce miki ki bari sai gobe ba bari zaki ba".

Farida na zuwa ta iske Hajiya Murja ta shirya ita taje jira, direct suka nufi airport sai dai inda suka je sai dai jirgin da zai kai su Katsina suka samu. Cikin isshan lokaci suka isa katsina, tun a airport d'in Katsina suka samu maimotar da zata kai su Nijar ".

Kasan cewar ba cancikin Nijar za su shiga ba , farko-farko ne yasa k'arfe hud'u na yamma suka isa gidan friend d'in Hajiya Murja wanda zata tai masu jagora zuwa gun bokan da zasu, in da dama ita ce ta tab'a yima Hajiya Murja hanyar shi".

Kasan cewar friend d'in Hajiya Murja ta sanda zuwan su Hajiya Murja yasa a ready ta ke, suna isa babu hutawa babu komai, danma sunci abinci akan hanya"..

Hajiya Bilki k'awar Hajiya Murja a motarta ta d'auki su Hajiya Murja ta kaisu har k'auyan da bokan ya ke".

Koda suka isa sun iske layi dan har sai da suka jira, sannan suka shiga. suna zuwa ya dakatar dasu ya ce, cikin muryar shi mara dad'in sauraro, "mai buk'ata kad'ai muke son gani, bama son 'yan rakiya, ku jirata a waje".

Hajiya Murja da Hajiya Bilki komawa sukai suka bar Farida kad'ai."..

K'urama Farida ido ya yi yana kallanta, dan har sai da Farida ta fara tsorata da kallan da bokan ya ke mata, sai zuwa wani d'an lokaci, ya ce, " me kike so ai miki, auran za'araba?, koko yarinyar ce kike so a kora daga gidan baki d'aya? ". Farida cikin zuciyarta ta ce, "Alhamdulillah kaji aiki". Sannan ta yi sauri cikin jin dad'i ta ce, "So nake araba auran kuma a kori yarinyar daga gidan baki d'aya, sannan ina son a dawo mai da hankalin shi ad'ora mai sona mu yi aure yana cikin hankalin shi ". Batare da bokan ya kuma cewa komai ba, wani magani ya d'akko yaba Farida, ya ce, "wannan zaki tauna shine ahaka zaki cinye shi, wannan kuma zaki wanke fuskarki da shi, wannan kuma zaki yarfa mai ajikine , ai dama ke ce kika haukata shi". Shiru bokan ya yi sannan ya ci gaba da cewa, "Magani na farko da nace miki zaki tauna, duk abinda kika ce, kina so agurinsa zai yi, zai ji maganarki fiye da ta Uwar da ta haifaima, a haka ne zaki bashi umarnin ya kuri ita yarinyar kuma ya saketa, magani na biyu da nace zaki wanke fuska da shi, shi kuma duk wani abun k'i da yake gani wanda ya hana shi sonki tom kamar shine kika wanke, magani na uku kuma wanda nace ki yayyafame, shine wanda zai dawo da shi hayyacinsa". Yana kaiwa nan ya ce, "mungama miki aiki, saura kud'in aiki zaki biya".

Farida kud'i ta ciro masuyawa ta ajema bokan, sannan ta ce, "Amma abinda yake ban tsoro ta yadda zanga Oga Habib d'in, dan yarinyar bata barina shiga wajan shi? ". Wani magani ya d'akko ya ce, kikira sunanta sau uku, sannan ki sha wannan, harta bar gidan sai abinda kika ce zata rik'a yi, dan haka daga kince ta ta bud'e miki da sauri zata bud'e". Farida da d'i ya ishsheta , kud'i ta kuma d'ebowa ta ba bokan, sannan ta tafi tana mai farincin nasara"..
Chapter 40 · 0% Book details