Sashe 43
Oga Habeeb Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Hassana ko haka taita juyinta kan caution, ita kanta bacin kayanta na side d'in Habib da wanka ta yi, amma tasan ko karan hauka ya cijeta ba zata iya zuwa ba ta d'akko ba. Hassana na nan kwance har aka kira sallar azahar, tashi ta yi tai alwallah ta tada sallah, Hassana na zaman tahiyar k'arshe Habib ya yi sallama ya shigo falon. Kan 2 seater Habib ya zauna yana jiran fitowar Hajiyarsa, dan a tunanin shi tana ciki tana sallah. Shiru-shiru Habib ya ji har yanzu Hajiya Turai bata fito ba, dan in sallah ta ke, yaci ace ta idar. Habib jin shirun ya yi yawa, yasa ya nufi bedroom d'in Hajiya Turai, kwance Habib ya isketa tana bacci Sosai, kamar karya ta data, amma ganin lokacin sallah ya yi yasa ya tada ta. Hajiya Turai kallan Habib ta yi ta tashi zaune tana mai ma mamakin ganin lokacin da ta d'auka tana bacci. Habib ma kallan Mahaifiyarsa ya yi, ya ce, "Mommy anyi sallah fa". "Subhallah!, wannan wana irin bacci nayi haka, da har akai sallah ban ji ba ". Hajiya Turai ta shi ta yi ta nufi toilet, saida ta kuma sama jikinta ruwa sannan ta yi alwallah ta fito, lokacinda ta fito Habib ya fita ya koma falo. Hajiya Turai sai da ta shirya ta yi sallah, sannan ta je falon, inda ta iske Hassana zaune kan sallaya, Habib kuma kwance kan 3 seater kan shi sama. Hassana da ke zaune tana jinta duk a takure ganin Habib a falon, cikin na tsuwa Hassana ta kalli Hajiya Turai ta ce, "Barka da fitowa Mommy ". "Yauwa daughter, Maimuna ta ko san da dawowa ta?, ko ta shigo da abinci ne?". "A'a Mommy bata shigo da abinci ba, ina jin bata san kin dawo ba". Cewar Hassana. Hajiya Turai waya ta ciro ta kira Maimuna, maimuna nad'agawa, Hajiya Turai ta ce, "Hello Maimuna ya naga har yanzu ba'a shigo da abinci ba". daga can b'angaran Maimuna tace, "Hajiya Wallahi ban san kin dawo ba, kuma yanzu ba girki akema Oga Habib ba, amma yanzu bari ayi da sauri, me za ayi Hajiya? ". " ki yi Simple food kawai". Cewar Hajiya Turai, sannan ta datse kiran".
Hajiya Turai zama ta yi, sannan ta kalli Hassana ta ce, "Daughter zo ki zauna nan mana". Hajiya Turai ta nuna ma Hassana kusa da ita". Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, "Mommy ina son zan yi wanka ne". "Tom ki je ki yi mana daughter, ki shiga toilet d'ina ki yi". Hassana tom ta ce, sannan ta ce, "Mommy kayana na can". Habib sai yanzu ya waigo ya kalli Hassana jin ta ce kayanta na can, wato ita ce ta sa kayanta cikin nashi".
Hajiya Turai sanyi ta yi itama , ganin yadda Hassana ta yi sanyi kamar a takure ta ke, dan ko yana yinda ta ke magana kasan takure ta ke. Hajiya Turai tashi ta yi tazo har inda Hassana ta ke tamo hannunta ta ce, "zo ki je ki yi wankan ki, kinada kayan sawa nazo muki da kaya bari in aika a d'akko miki, nabar jakar kayan wajan mai gadi, lokacinda na iso mai gadi d'aya ne awajan get d'in". Hajiya Turai na rik'e da hannun Hassan suka shiga bedroom d'in Hajiya Turai. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi ta ce, "Daughter ki saki jikinki mana, kinga ko yadda kike yi?, ko kina so Habib ya rainaki ne?, kina nufin Saboda Habib kike d'ari-d'arin nan?, tom banji dad'in ganinki haka ba, ina son in rik'a ganinki kamarda, in ma d'aurewrar Habib ce tom karki yi tunanin ko mai, nature na shi ne, haka Habib ya ke tun yana yaro, idan ba ni ba ko friend's d'in shi, tom zan iya ce miki babu wanda zakiga Habib ya zauna da shi suna fira, tun abin na damuna har ya ma daida damuna, kuma ak'idarsa ce ko nima bai cika min yawan magana ba idan yana ganin wani kusa, dan Allah daughter ki saki ranki ki dawo kamar da ". Bud'e baki Hassana ta yi za tai magana, Hajiya Turai ta rufe mata baki, ta sa mata d'an ya tsa abaki, ta ce, "ki shiga ki wanka daughter idan kin shirya sai muyi maganar da kike son yi". Hassana juyawa ta yi ta shiga toilet d'in, kamar yadda Hajiya Turai ta buk'ata. Ita kuma Hajiya Turai fita ta yi, ta sa aka d'akko mata jakar kayan da ta siyoma Hassana, ta kai ta bedroom d'in ta, ta ce, "Daughter ga kayan nan, naki ne duka kisa wanda kike so". Sanan Hajiya Turai ta fita ta koma falon. Hajiya Turai na zama Maimuna na shigowa ta ce, "Hajiya ko mai na dernin". "Ok, me kika dafa ne? ". Cewar Hajiya Turai. "Cous-cous". Maimuna taba Hajiya Turai amsa"..
B'angaran Hassana ko tana fitowa ta shafa lotion d'in da taga Hajiya Turai ta aje mata, sannan ta bud'e jakar kayan da Hajiya Turai ta ce tata ce duka, Sosai Hassana ta ya ba da kyan kayan, dogayan riguna ne kala-kala da riga da siket na kanti, da gyalilluwa da ta kallama na sawa masu kyan gaske, Hassana ganin kayan da yawa wata doguwar riga red color da ta ji adon stone ta d'akko ta sa, sannan ta d'akko d'an kwakin rigar da yake babba ne ta yafa ta samu gu ta zauna, dan tafi son lokacinda zata fita ace Habib baya nan ya tafi".
Can b'angaran Hajiya Turai ko jin Hassana shiru, tashi ta yi ta nufi bedroom d'in ta, zaune ta iske Hassana. Hajiya Turai girgiza kai kawai ta yi, sannan ta ce, "Daughter muje mu ci abinci, ke muke jira". Hassana bayan Hajiya Turai ta bi suka fita. Sai dai Hassana bata ji dad'i ba ganin Habib har yanzu yana falon. Hajiya Turai kallan Habib ta yi, ta ce, "Habib muje ga abinci can". Habib b'ata fuska ya yi ganin Hassana kusa da Hajiya kenan harda ita zasu ci, Habib sharewa kawai ya yi badan ya soba ya tashi ya nufi derning space d'in".
Hajiya Turai da kanta ta yi seven's d'in Hassana da Habib. Ba laifi Habib ya ci dadama amma Hassana tsakura kawai ta yi, Hajiya Turai dai na kule da Hassana, amma sai bata tanka mata ba. Bayan Habib ya gama cin abincin, kallan Hassana ya yi, ya ce, "Bamu gu zamu yi magana". Dama Hassana tun-tuni ta aje spoon d'in ta alamun ta k'oshi. Habib ko na cewa bamu gu, kamar jira ta ke ta tashi zata tafi. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi ta ce ,"daughter koma ki zauna". Hassana komawa ta yi ta zauna. Habib haka d'in da Hajiyarsa ta yi, shi kuma sai ya b'ata mai rai, acewar shi bazai magana gabanta ba, hakan yasa ya tashi ya ce, "Mommy please ina wayata zan yi amfani da ita ne? ". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter ina wayar shi? ". Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, "Mommy tana sip d'in k'ayan shi". "Ok jeki d'akko mai". Cewar Hajiya Turai. Hassana tashi ta yi ta fita".
Habib kuma ganin haka komawa ya yi ya zauna, ya kalli Mahaifiyarsa ya ce, "Mommy wai ita d'in Wacece?, kuma me ya kaita side d'ina da har zata aje kayanta anan?, wai Mommy taya haka ma ta faru bansani ba!? ". Habib ya fad'i maganar cikin damuwa. Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "Habib wato abu mai girma ya faru da kai, idan zaka iya tunawa lokacinda zan tafi London ka ce min kana fama da wani irin ciwan kai, ahaka dai na tafi nabarka, mu kai da kai zaka je hospital adubaka, tom Habib bayan tafiya ta akakirani ake sanar dani wai baka da lafiya yanzu haka baka san inda kanka ya ke ba, kuma abinda ya tada masu Bilya hankali da sauran ma'aikatan wajanku sai ciwan yazo maka da duka, dan duk wanda ka rik'e sai an kwace shi , Hassana ka d'ai ya rinyarda ke aiki a Sanad yoghurt, yarinyar da ke zaune gidan nan, da ita ka d'ai kake yarda da ita,dan Habib ko ni da na dawo ban isa in shiga inda kake ba. Hassana kad'ai ke baka abinci ka ci, ita kad'ai ke baka magani kasha, ita kad'ai ke shiga inda kake ta zauna, amma in ba itaba duk wanda ya shiga sai an k'wace shi a hannunka, wannan da lilinne yasa na had'a ka aure da Hassana, dan ba zai yuwuba tana shiga inda kake har ta kwana a matsayinta na mace wadda ba muharramarka ba". Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "Tom kaji abinda ya faru Habib, amma abinda baka gane ba zaka iya min tambaya".
Hajiya Turai zama ta yi, sannan ta kalli Hassana ta ce, "Daughter zo ki zauna nan mana". Hajiya Turai ta nuna ma Hassana kusa da ita". Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, "Mommy ina son zan yi wanka ne". "Tom ki je ki yi mana daughter, ki shiga toilet d'ina ki yi". Hassana tom ta ce, sannan ta ce, "Mommy kayana na can". Habib sai yanzu ya waigo ya kalli Hassana jin ta ce kayanta na can, wato ita ce ta sa kayanta cikin nashi".
Hajiya Turai sanyi ta yi itama , ganin yadda Hassana ta yi sanyi kamar a takure ta ke, dan ko yana yinda ta ke magana kasan takure ta ke. Hajiya Turai tashi ta yi tazo har inda Hassana ta ke tamo hannunta ta ce, "zo ki je ki yi wankan ki, kinada kayan sawa nazo muki da kaya bari in aika a d'akko miki, nabar jakar kayan wajan mai gadi, lokacinda na iso mai gadi d'aya ne awajan get d'in". Hajiya Turai na rik'e da hannun Hassan suka shiga bedroom d'in Hajiya Turai. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi ta ce, "Daughter ki saki jikinki mana, kinga ko yadda kike yi?, ko kina so Habib ya rainaki ne?, kina nufin Saboda Habib kike d'ari-d'arin nan?, tom banji dad'in ganinki haka ba, ina son in rik'a ganinki kamarda, in ma d'aurewrar Habib ce tom karki yi tunanin ko mai, nature na shi ne, haka Habib ya ke tun yana yaro, idan ba ni ba ko friend's d'in shi, tom zan iya ce miki babu wanda zakiga Habib ya zauna da shi suna fira, tun abin na damuna har ya ma daida damuna, kuma ak'idarsa ce ko nima bai cika min yawan magana ba idan yana ganin wani kusa, dan Allah daughter ki saki ranki ki dawo kamar da ". Bud'e baki Hassana ta yi za tai magana, Hajiya Turai ta rufe mata baki, ta sa mata d'an ya tsa abaki, ta ce, "ki shiga ki wanka daughter idan kin shirya sai muyi maganar da kike son yi". Hassana juyawa ta yi ta shiga toilet d'in, kamar yadda Hajiya Turai ta buk'ata. Ita kuma Hajiya Turai fita ta yi, ta sa aka d'akko mata jakar kayan da ta siyoma Hassana, ta kai ta bedroom d'in ta, ta ce, "Daughter ga kayan nan, naki ne duka kisa wanda kike so". Sanan Hajiya Turai ta fita ta koma falon. Hajiya Turai na zama Maimuna na shigowa ta ce, "Hajiya ko mai na dernin". "Ok, me kika dafa ne? ". Cewar Hajiya Turai. "Cous-cous". Maimuna taba Hajiya Turai amsa"..
B'angaran Hassana ko tana fitowa ta shafa lotion d'in da taga Hajiya Turai ta aje mata, sannan ta bud'e jakar kayan da Hajiya Turai ta ce tata ce duka, Sosai Hassana ta ya ba da kyan kayan, dogayan riguna ne kala-kala da riga da siket na kanti, da gyalilluwa da ta kallama na sawa masu kyan gaske, Hassana ganin kayan da yawa wata doguwar riga red color da ta ji adon stone ta d'akko ta sa, sannan ta d'akko d'an kwakin rigar da yake babba ne ta yafa ta samu gu ta zauna, dan tafi son lokacinda zata fita ace Habib baya nan ya tafi".
Can b'angaran Hajiya Turai ko jin Hassana shiru, tashi ta yi ta nufi bedroom d'in ta, zaune ta iske Hassana. Hajiya Turai girgiza kai kawai ta yi, sannan ta ce, "Daughter muje mu ci abinci, ke muke jira". Hassana bayan Hajiya Turai ta bi suka fita. Sai dai Hassana bata ji dad'i ba ganin Habib har yanzu yana falon. Hajiya Turai kallan Habib ta yi, ta ce, "Habib muje ga abinci can". Habib b'ata fuska ya yi ganin Hassana kusa da Hajiya kenan harda ita zasu ci, Habib sharewa kawai ya yi badan ya soba ya tashi ya nufi derning space d'in".
Hajiya Turai da kanta ta yi seven's d'in Hassana da Habib. Ba laifi Habib ya ci dadama amma Hassana tsakura kawai ta yi, Hajiya Turai dai na kule da Hassana, amma sai bata tanka mata ba. Bayan Habib ya gama cin abincin, kallan Hassana ya yi, ya ce, "Bamu gu zamu yi magana". Dama Hassana tun-tuni ta aje spoon d'in ta alamun ta k'oshi. Habib ko na cewa bamu gu, kamar jira ta ke ta tashi zata tafi. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi ta ce ,"daughter koma ki zauna". Hassana komawa ta yi ta zauna. Habib haka d'in da Hajiyarsa ta yi, shi kuma sai ya b'ata mai rai, acewar shi bazai magana gabanta ba, hakan yasa ya tashi ya ce, "Mommy please ina wayata zan yi amfani da ita ne? ". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter ina wayar shi? ". Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, "Mommy tana sip d'in k'ayan shi". "Ok jeki d'akko mai". Cewar Hajiya Turai. Hassana tashi ta yi ta fita".
Habib kuma ganin haka komawa ya yi ya zauna, ya kalli Mahaifiyarsa ya ce, "Mommy wai ita d'in Wacece?, kuma me ya kaita side d'ina da har zata aje kayanta anan?, wai Mommy taya haka ma ta faru bansani ba!? ". Habib ya fad'i maganar cikin damuwa. Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "Habib wato abu mai girma ya faru da kai, idan zaka iya tunawa lokacinda zan tafi London ka ce min kana fama da wani irin ciwan kai, ahaka dai na tafi nabarka, mu kai da kai zaka je hospital adubaka, tom Habib bayan tafiya ta akakirani ake sanar dani wai baka da lafiya yanzu haka baka san inda kanka ya ke ba, kuma abinda ya tada masu Bilya hankali da sauran ma'aikatan wajanku sai ciwan yazo maka da duka, dan duk wanda ka rik'e sai an kwace shi , Hassana ka d'ai ya rinyarda ke aiki a Sanad yoghurt, yarinyar da ke zaune gidan nan, da ita ka d'ai kake yarda da ita,dan Habib ko ni da na dawo ban isa in shiga inda kake ba. Hassana kad'ai ke baka abinci ka ci, ita kad'ai ke baka magani kasha, ita kad'ai ke shiga inda kake ta zauna, amma in ba itaba duk wanda ya shiga sai an k'wace shi a hannunka, wannan da lilinne yasa na had'a ka aure da Hassana, dan ba zai yuwuba tana shiga inda kake har ta kwana a matsayinta na mace wadda ba muharramarka ba". Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "Tom kaji abinda ya faru Habib, amma abinda baka gane ba zaka iya min tambaya".