← Book details Mr Bello Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 55 OF 76

Sashe 55

Mr Bello Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da sauri na Bude ido ina kallon yadda na Rike rigansa da Sauri na Sakeshi na mike ina Jin Kunya Gira ya Dagamin yana Fadin"Kunyar me..? Bayan kin gama lafemin..."yafada yana kallon yanayinshi Ni kuwa ban Kula Dashi ba na Fada Tiolet Cikin Jin kunya,Har na gama wanka Fuskata tana cikin Mirmishi ina Daure da Towel na Fito ina ganinshi zaune inda na barshi muka hada ido na Turamai baki,na Wuce da Sauri na Dauki Hijabi,na saka da Kallo yabini kafin yace""Malama kizo ki taimakamin nayi wanka Tunda kin jamin.."Yafada kansa Tsaye.

Da Sauri na waigo ina kallonsa Kunu yasha Lokaci Daya yana Daga min gira,Kai na Sunkuyar ina Rufe Fuska na kariso kusa dashi na taimakamai na maida shi saman keken shi,ni na ciremai T.shirt din Jikinsa da Vest wando kadai na barmai na Turashi Zuwa Toilet ina Kauda kai bana son muna Hada ido,ina kaisa na Juyo da Gudu na Fito ina jinsa yana Kira na naki dawowa kunya kamar na Nutse wai Na sakashi wanka Lalle nema.

Ban bari ya fito ba nayi Saurin Shiryawa na Fice Zuwa Falon, Shikuwa da gaske sai da yayi wankan Tsarki kana yayi wanka ya Turo kanshi ya Fito dama yasan bazai ganni ba,na gudu yar dariya yayi,shi ya tura kanshi gaban Madubi ,ya Shafa mai ya tura kanshi Zuwa gaban Wardrope ya bude ya Dauko Riga da wando na wani Farin yadinsa,vest dinsa da boxers dinsa wanda suke Daga kasa na Jeramai,Shi ya shirya kanshi Tunda ko ya kirani bazan dawo ba,Ina Zaune afalo naga ya Turo kansa ya Fito,kallona yayi yana Fadin"Kin kyauta..Kin sakani aiki kuma kin gudu kin barni..."

Dariya na saka ina Boyewa kaina Cikin Cinyoyina Shi kuwa Cikin Kauna mai Tsanani yake bina da kallo Ranar Wuni yayi Tsokanata ko kuma da mun hada ido ya Dagamin gira yana Dariya Duk sai na Tsargu kunya ta hanani sakin Jiki.

******

Yau ta kama Asabar ne Tun Safe na tashi da aiki, Sakamakon Tun Jiya B.kaita ta kirani tana Tafe,Tunda tun satin Daya gabata tashigo kano,ita da Salamatu Jibiya sun zana jamb kuma sun samu Nasara B.kaita har ta samu Admssion,anan Buk zata karanci Microbiology,ita kuma Salamtu Jibiya Tana Federal University Dutse Dukkansu tun Wanchan Satin kowacce ta Wuto mkrta,B.kaita nan cikin Makaratan ta samu Hostel take Zaune

Girke girke kala nayi mata Ita da Anty Aisha wacce itama suka dawo Daga Benin inda Mijinta ke aiki,ta kira ni da safe tace min Zata zo anjuma ita da Megidanta,Raihana tazo Tun Safe ta taimakamin Bayan mun gama Girkin ita na Barma gyaran Kichen Din da kuma gyara Falon Duk da na gyara da Safe Daki na Koma na Shiga wanka ganin Bello na kwance bai tashi ba,har nayi wankana na Fito ban Lura dashi ba Ashe Tun Shigowata yatashi Daga barcin yana dai kwance ne yayi kamar yana barci.

Mai na Shafa agurguje Na Bude cikin Akwatunan da kasim yayi min na Dauko wata Shadda Doguwar Riga,mai ruwan kasa,cikin Wardrope dina na Dauko bra da pant na saka kafin na Zura Rigar,bai min mgana ba sai da na gama kwalliyata na Daura Dankwali na waigo kenan muka hada ido yana Daga kwance kokarin Tashi yake na Taimakamai bayan na sakamai Filo Ta bayanshi ina Fadin"ashe ka tashi..?

Nafada ina kallonsa cikin Lumsassun idanuwansa yace"Tun dazu ma.."Ido na waro ina kallonsa Gira ya Dagamin yana Fadin"Yes Tundaga Fitowarki Wanka har gama Shiryawanki.."Baki na Rike Lokaci Daya naja baya ina Buga kafa Cikin Shagwaba nake Fadin"Ni..ni wlh ban yarda ba..Koda yaushe kai ta ganemin jiki.."Dariya ta kamashi ya kanne yana Fadin"ah kajimin yarinya Ni bance kina min wayau ba sai ni..Tsaya Tun yaushe kike ganin nawa Jikin .? Yafada yana saka hannu cikin bakinsa alamun Tunani,

Zaro ido nayi ina Dariya nace"Ni fa Bana kallonka idona nake kullewa sai na gama.."Kafada ya make yana Fadin"ban yarda ba ko Yaya ne kin kalla dai.."Yafada yana Hade rai Baki na Tura ina Fadin"Shikenan Tunda ka rama Daga yau bazan kara wanka anan ba Dayan Dakin zan koma.."Zakuda kafada yayi yana Fadin"Bakomai..Nagama ganin komai.."Kamar zan saki kuka Haka na juya ina Tura baki cikin Amon Murya yace"Wannan kayan fa..?

Cikin Mamaki na waigo ina Fadin"Kaya kuma..? Kai ya Dagamin, bai yi mgana ba Cikin mamaki nace"Cikin wanda Kasim ya bar min ne.."Cikin Daure Fuska yace"Ki cire rigar nan yanzu ki sauya wata...Kuma kada ki kara saka min Kaya Daga Cikin kayansa ki tattarasu waje Daya malama...."Yafada yana Kauda kai.

Cikin mamaki nace"in cire fa kace.? Bani da wasu kaya anan Duk suna Abuja.."Harara ya sakarmin kafin yace"Nace ki cire ko..? Kuma karki kuskura ki sake amfani da ko Tsinke Cikin kayansa Nagama mgana.."Yafada Lokaci daya yana dafe kansa,Kallonsa nayi cikin mamakinsa na Bude baki zan Sake mgana kawai ya jefamin wani kallo yana Fadin"Karki karamin Mgana malama...juz do as i say.."Yafada yana kokarin Zura Hannu ya Matso da Kekensa da Sauri na karisa na tura mai,lokaci Daya na Saka Hannu na Riko kafadansa na tayasa ya Sauko Daga kan gadon,ya Zauna Bisa Keken hannu na saka ina Kokarin Taimakamai na Ciremai Rigar barcin Dake jikinsa kawai ya Ture Hannuna bai kalleni ba ya Tura kekensa ya saka Hannu ya Bude Kofar Tiolet ya Shige ya barni nan tsaye ina Binsa da kallo Tuni idanuwana suka kawo kwallah.

Rigar na cire na Sauya da Material Dingin Doguwaar Riga Itama Cikin Wanda Anty Rahila ta Dinkamine  gab da Bikina,Kwalliyar Fuska tawa ma gogeta nayi ina Tunanin Toh miye Abun Fushi kuma..? Na dade Ciikin Bedroom kafin na Fice bayan Kiran B. kaita ya Shigo cikin Wayata nan take Shaidamin Tana Buk raod din na mata kwatancen Gidan,nan nayi mata Dayake muna bakin Titi ne

Ko Minti Goma ba"ayi ba sai gata ta iso ita da Wata Cousin dinta Aliya wacce Suka samu Admission tare,Nan muka Rumgume Juna Cike da Farinciki,Dagoni tayi tana Fadin"Kai Anee kinganki kuwa..? Na mata far da ido ina Fadin"Allah na amarci ne..."Duka ta Dagamin kafin mu saki Dariya Lokaci Daya muna Tafawa,riko hannunta Nayi muka karisa Falon Lokaci daya muka Zauna.

Sai da muka gaisa da Aliya Raihana ma ta gaishesu kana na mike naje na kawo musu Ruwa,Raihana kuma ta Dauko Kololin Abinci nan muka baje afalon Tare muka ci abincin muna Hira B.kaita ta kalleni tana Fadin"Wai ina Uncle din namu ne..? Ko kin fara Boyemana Shi ne..?

Dariya na saki ina Fadin"Ah ko Daya na barshi cikin Daki ne Mu gama cin Abinci Tukunnah zaki ganshi.."Nafada ina Dariya Dariyar itama ta saka Haka dai muka gama cin Abicin Raihana ta kwashe komai ta maida kichen Dakina ada na kaisu sukayi sallar Azahar Ni kuma na Shiga Bedroom dinmu na Sameshi Zaune Bisa Wheelchair dinsa yana kararun Qur"ani Daga Nesa na Tsaya ina Fadin"Bilkisu fa tazo Tun dazu kuma tana ta tambayarka..."

In kun tanka ya Tankani sai ma Maida Qur"anin daya yi ma"ajiyarsa,ya Shiga Tura kansa ,Yana sanye yau ma Da Riga da wando kirar Armani Fuskarsa tayi haske sosai ina kallo ya Bude kofar Bedroom din da Hannunsa ya Fice ya barni nan tsaye,kuncina na kama ina mamakinsa inaji suna gaisawa da Su B.kaita Har yana tambayanta karatu tana amsamai da lafiya kalau ba wata mtsala,Kwallah suka kusa Kawomin nayi Saurin maidasu kafin na Fito ko barayin Dayake ban kallah ba na maida kaina gefe na Wuce kichen Ina Taku Daya Bayan Daya.

Da Kallo yabini kafin ya Kauda kai Shima Cikin fushi,Abunda ya batamai rai yace ta cire kaya ta Zauna tana jajjaya dashi wato Haryanzu kasim yana Cikin Ranta kenan..? Bai kara cewa komai ba yashiga Tura kansa Zuwa Falon Farko wajen Modibbo B.kaita ta bishi da kallon Tsausayi ta juya suna mgana da Aliya,nikuwa wanke wanken Karya na Shigayi Duk don Damuwar Dake Raina ta Ragu Jina Shuru yasa B.kaita ta Biyino ganin ina aiki ne yasa ta kwabe gyale tafara tayani,nayi nayi ta bari taki,sai na kyaketa Muka Fara Hirar yau gamo nan take fadamin tayi wani Saurayi Dan Bauchi Sunanshi Usman yana lecturing A Umaru Musa yaraduwa Univeestiy Katsina ammh yana da mata kuma ya nuna mata da gaske yake yana so yazo yaga iyayenta ammh taki bashi dama,kallonta nayi ina Fadin"Saboda mene...?..

Ta marairaice tana Fadin"Ina tsoron matarshi ne Anee Allah kuwa.."Tsaki naja ina Fadin"Dillah ina Ruwanki da wata matarshi kanta Zaki Zauna...Don Allah ki bashi dama ayi awuce wajen indai ba baki son shi bane.."Cikin Sanyi Jiki tace"Allah ada bana sonshi ammh yanzu na kamu da sonshi yana da Kyakyawan Dabi"a.."Jin Haka yasa na Zage ina ta bata wasu Shawarwari har muka gama wanke komai muka adana,muka Dawo Cikin Bedroom dina muka cigaba da Zantawa Inda muka bar su Raihana da Aliya suna hira suma Daga gani taso tazo Daya.

Sai bayan la"asar suka tafi,Modibbo na Roka ya kaisu,bai ma Dawo daga kaisu ba Anty Aisha tazo ita da Mijinta,na Rumgumeta ina Murnan ganinta Ita kuma tana Dariya ta Dunguremin kai tana Fadin"Ke kam ko"ina akaje aka dawo sai kin Nuna ke Auta ce.."Dariya na saki ina Fadin"Eh mana Auta dan gatan gida.."Dariya mijinta Ya saka Bello ko sai dai ya murmusa.

Sai bayan mangariba suka tafi bayan Anty Aisha ta kawomin Gumbar mata da Humra,ta kuma bani Shawawari Sosai wajen yadda Zan kula da kaina,Na kuma jita na kuma karu,Sai da Suka Tafi kana Modibbi yatafi maida Raihana gida wanda naso na bishi naje na gaida Ammi ammh gogan ya hade rai yace bazani ba Dole na Hakura Na Shige Daki ina Tura baki Ranar Tun 8 na kwanta na Juyamai abaya acikin Raina ina Fadin naga mai taimakamaka ka hau gadon...

Ki biya ki karanta cikin Salama.

*Anitha....*
8/19/20, 11:26 AM - Ummi Tandama: *MR BELLO..!*
_(The young Teacher)_

  
*Wattpad:Janafnancy13*

   *Littafina na kudi ne,kibiya ki karanta cikin salama,akan �200 kachal,Vips � 400 ne,kada ki karanta min littafi indai baki biyani ba,Domin neman karin bayani zaku iya nemana ta wannan Nombar 09069067488*

        *🅿�31*

Ina jinsu Suna Hira sama sama Shida Modibbo,Bansan sadda Barci mai Nauyi ya kwasheni ba Saboda Daura ma kai Fushi katon Hijabin Sallaana na Zumbuda na kwanta Dashi Ko Zafi banaji ni adole an batamin Rai ina Tura bakin da Fushin Da Komai barci yayi awon Gaba Dani.
Chapter 55 · 0% Book details