Sashe 41
Mr Bello Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haruna yayi wata Dariyan kasaita kafin yace"Karka damu Mutumina,Kawai ka jira lokaci suna gama yawan kasashen zasu Hakura su Dawo Dashi gida nasan Daga Lokacin ko ita Aneesa bata Fara tunanin komai ba iyayenta Zasu Fara Tunanin Rabata Dashi,Domin zama da Nakashasshe sai Dole ko nace Gawa mai Rai.."Yafada yana Dariya Lokaci daya Suke Dariyan muguntan da Haruna kafin Kasim ya tsaigata da Dariyan yana Fadin"Zan so na ganshi fa..? Zan so naga idanuwan izza da takamar nashi naga yanzu yana dasu kokuwa.."
Haruna yace"Ina ai sai dai kaga Tarin kashi da Fitsari Daga Zaune mallam.."Kara saka Dariya Sukayi kamar Wasu mahaukata,sai da sukayi ya ishesu kana Kasim yace"zan Tura maka duka kudin aikin kaje ka kai mai kamika sakon godiyata garesa,saboda office yasa bazan samu zuwa ba.."
Haruna yace"No wahala karka wani Damu.."Daga Haka suka yanke Kiran Bisa Kujera Kasim ya Fada yana Sakin Dariya Lokaci Daya yana Jefar da gwangwanin maltinan Dake hannunsa Wanda yagama Shanyewa Dariya yake Cike da Nishadi kafin ya Saki Mirmishi yana Shafa Sajensa yana Fadin"Aneesa kin kusa Dawo gareni Dama ke din Tawa ce Ni kadai..",yake fada yana kara sakin Wani mirmishi mai cike da Ma"anoni.....
****
_New Delhi_
Kwanansu uku kenan da zuwa kasar ammh haryanzu Dr khabir khan bai musu wani bayani ba Kuma Har Tsawon Wadanan kwanakin Bello na Cikin Dakin gwaje gwaje ba'a fito dashi ba saboda abunda ya matukar basu mamaki yadda duk sakamakon gwaje gwajen Dake Fitowa,Normal babu mtsalan Komai Shine Abunda yake basu mamaki ga Bello yana nan Jiya iyau abinci ma sai Cikin Ruwan Alluran dasuke Sakamai ne yake samun Karfin Jiki.
Akwana na Hudu ne Dr kabir khan ya kira ya Muktar Da ya Sunusi Da ya Hashim Zuwa Cikin Offce dinsu yana kora musu jawabin Sakamakon gwajen gwajen da Suka ma Duk wasu kasusuwan Bello Dake da alhakin Tashinshi ko Tsayuwarshi Haka bangaren Mganarsa ma Hatta Hotoon kansa da kwakwalawarsa sai da Sukayi ammh komai Normal yake Nuna musu.
Bayani yake musu Lokaci Daya yana Nuna musu gwajen gwajen Hotunan,ya muktar Daya Shiga wani yanayi Cikin Harshen Turanci yace"Dr bawani Taimako da zaku mana ne ,?nan ne kadai Hop dinmu.."Shuru Dr khabir khan yayi kafin yace"agaskiya bazai iya cewa komai ba yanzu Ammh mganar gaskiya Wannan ne Karo na Farko da Suka samu Irin wannan case din sai dai zasu jaraba sanyashi cikin Wasu Injina Na Tsawon Wata Daya Sukagani in Har Bai tashi ba zasu koma bangaren kashi toh gaskiya indai Duk Hakan bai sa ya tashi ba Toh basu da wani Abunda zasu ma Bello.."Hankalinsu Duk ya Tashi Sosai Da jin wannan bayani Cikin Daukewar Hawaye Muktar yace"ajaraba agani Insha Allahu inaji ajikinsa Bello zai Tashi.."Da wannan Shawaran Suka Rufe Tattaunawansu,sai kuma Ranar ne aka Fito da Bello Daga dakin gwaji zuwa dakin matakin Farko,Ba"a barsu sun Shiga ba ammh daga bakin kofar suna iya Hangensa ta Cikin galisan Wajen,Aneesa Ranar da kuka Wiwi Suka koma Masauki Saboda yadda aka sanya Bello Cikin Wani Inji mai Jijjigar da Jikin Mutum,Daada kuwa ta koka ta koka kamar Ranta Zai Fita Duk ta Zabge ta rame kamar ba Ita ba Wani Abun Tsausayin ma Mai Rai kwance ba mgana ba motsi sai dai Numfashi,rai mai alfarma kawai ammh kowani bawa yaga Halin da Bello ke Ciki sai ya Koka mai.
Kullum sai dai suzo su lekasa su koma Aneesa sai tafi awa Daya Tsaye tana kallonsa tana Share kwallah Ranar da Suka Cika Sati da Zuwa Ya Sunusi da ya Hashim suka barsu anan suka koma Nageria cike da Fatan samun lafiya ga Bello,Ya muktar kuwa da Anty Rahila sai da Sukayi Sati Uku kana Suka koma Shida Yara saboda mkranta da kuma Aiki aka bar Daada da Aneesa Wajen Bello wanda sai yayi Wata Daya Cikin Wannan Na"uran injin din kana Za"a Fito dashi asake sabon Gwaje gwaje.
Shikanshi Ya Muktar din yana Nageria ne ammh Zuciyarsa gabadaya suna india kafin Tahowarasu ya Siyama Aneesa Waya saboda jin Halin da Suke Ciki kullun dai Jiya iyau Kullum Ya Muktar Cikin Waya Suke da Dr Khan Amsa Daya ne,Sai wa"adi ya cika Kana za su sake Gwaji suga ko ansamu Cigaba,Kullum baya barcin kirki Salloli yake da addu"an Allah ya Tashi kafadun Bello,mutane Dadama sunzo har gidan Yimai jajen Abunda ya Faru Duka iyalan Abba kabiru da na Abba garba mama Sahura da Umma Zulfa da Zubaida wanda kowacce Dataj lbrin Abunda ya Faru da Bello sai da ta girgiza Cikin Zuciyar iyayensu kuwa Hamdala Suke Da ba wacce Ya Auri yarta da yanzu an sakasu Acikin Wahala Umma Harda cema Anty Rahila Aneesa ne Abun Tsausayi Da kuruciyarta Zata kare da Aikin gaton kwance Anty Rahila dai bata tanka mata ba Saboda Ta gane inda ta Dosa,Hatta Inna Rukayyah Daga kano tazo,ta kwana biyu ta koma,Shikanshi Kasim ya kira Ya Muktar awaya yana mai jaje harda Nuna Tsausayi Kamar na Allah Nan ko yana kashe Wayar yayi ta Dariya.
Mutanen Borno Kuwa Ya Ali yazo Shida Anty Nafee,sunyi kwana Daya Suka koma,bayan suma Anty Yagana tazo gwanin ban Tsausayi ba wacce suke Tsausayamawa Irin Aneesa Tana karamar yarinya ta Hadu da Jarabta Rayuwa.,Kawayen Aneesa Kuwa B.kaita ce Taji Aneesa Shuru sai ta kira Wayar Anty Rahila nan taji lbri mara Dadi ita ta Kira S.jibiya take gayamata Dukkansu sun jajaantama Aneesa Tare da yin alkawarin saka Mr bello Cikin Addu"o'insu.
Uncle Aminu Ko Dake Kasar Spain bai da Lbrin Abunda ke Faruwa Domin Tunda yayi ta kiran Nombar Bello bai samu ya Hakura tunda bashi da Nombar ya Muktar ammh kullum sukayi mgana da Ammi sai ya Tambayeta ko Bello yazo.? Nan take gayamai Tun Zuwanshi lokacin Daya sanar da ita zai Fara Lecturing a Buk kano bai kara Dawowa ba,Aminu ya Shiga damuwa sosai ammh yana kokarin ya kamallah abun ke gabanshi ya Dawo domin Sauranshi Wata Biyar yagama komai ya Dawo gida.
Sani bai samu lbri ba Sai Daga baya Har Abuja yazo yama Ya Muktar Jajen Abunda ya Faru ya kuma ce in zasu koma India zai bisu yaga Halin da Bello ke Cikin,achan india kuwa Daada ta bama Muktar Shawaran yaje Adamawa ya Taho da Modibbo,Mtsayin Jika yake gareta Saurayi ne irin bai yi karatun Boko mai Zurfi ba iyakarsa Sakandiri sai na Addini,aikin Gyaran Motici yake agarin Adamawa tace ya Daukosa Su Taho tare koda An Fito da Bello Aneesa Tayi kankantan Iya kula da Bello itakuma ta Tsufa ga jikin Girma Nan da nan ya karbi Shawaranta yaje har Adamawa ya Taho da Modibbo iyaye da yan"uwa nata Faman addu'an samun Sauki ga Bello.
Ana saura kwana Uku Afito Da Bello Suka Dira Akaasar india Shida Sani da Modibbo,Daga modibbo har Sani Suna Tsaye Cikin Kofar Dakin da Bello yake suna Hangensa Kwance sambal cikin Na"ura mai amfani da Na"urorin Computer,Sani na Hawaye modibbo nayi suna Tunanin bawa mai Rai ne Cikin Wannan Abun Lalle Allah kadai ne Mai Nuna aya alokacin dayaso Shi kanshi Ya Muktar yanzu bashi da wani karfin gwiwa kamar mace zaki ga yana Share Hawaye Shar Shar kamar ba Soja ba wanda yasha gwagwamaryan Rayuwa...
Awannan Dawowar ne ya Razana da Ganin yadda Aneesa ta koma Dama ba Auki ba,ta kara ramewa duk tayi baki,nan Daada ke Fadamai bata cin abinci sai kuka zama yayi yana ta lallashinta Tare da Sanar da ita bayan anfito da Bello sun ji sakamako in zai koma Nageria zai Tafi da ita nan Aneesa Taka Rushewa da kuka Tana babu inda Zata ita zata Zauna anan kukan Datakeyi sai da ta saka Ya Muktar share kwallah Saboda Tsausayinta.
Ranar da za"a fito da Bello Daga Cikin Wannan Injinan Dukkansu ba Wanda ya Runtsa kwana Sukayi Addu",an Allah ya sa ansamu Nasara matakin Farko Da Sassafe suka yi ma Asibitin Tsinke Likitoci Sunfi Goma Suka Shiga Dakin sun Dauki Tsawon Awanni Aciki kafin Su Fito basu ma kowa bayani ba Illah Dr khabir khan dayace musu Suyi ta Addu"a yanzu za"a kara Tafiya dashi Dakin gwaji abunda sakamako ya Fitar Shine zasu yi Aiki Dashi.
Aneesa Sulalewa Tayi Jikin Daada Tana Kuma duk Addu"an da tazo bakinta Daga gida Nageria ma Duka ya muktar Duk ya Kira su yana Rokon atayasu da Addu"a Anty Rahila ma Tuni ta Kira borno ta sanar dasu Kowa dai Yana ta Addu"an Allah ya sa Anyi a Sa"a.
Agaban idonsu aka Fito da Bello Zuwa Dakin Gwaji kamar gawa ya yi Fari kasumba ta cikamai Fuska da jiki,Numfashi ne kadai zai sa kagane Bello yana Da Rai,Tsawon awa Hudu Suka kwashe Cikin Dakin gwaji kafin Likitocin Su Fito,Yadda ya muktar yaga Fuskar Dr Khan ne yasa Yaji gwiwansa Tayi sanyi Hawaye Sun Taru Acikin kwarmin idanuwansa Daga yadda Indiyanwan Likitocin ke mgana zaka san Abun ya basu mamaki basu samu ganin Dr khan ba sai da Suka Fito Daga Meeting din Da Suka Shiga Akan Cutar Bello.
Gabadayansu Suka D'uru Cikin Office din Dr khan Lokacin yana Tare da Dr Sunhat,suna kara Duba Duka Record din Bello Suna kara mamaki Dr Khan ya Zare gilashin Idanuwanshi yana kallon Ya Muktar kafin yace"Am Srry to say...Ammh wannan Gwajin matakin Farko bamu Samu Nasara ba,Munyi matukar mamaki ganin yadda ya Fito Daga cikin Wannan Na"uran ammh kuma Duka Sakamakon Farko gwajin ke Nuna mana Gabadaya kanmu ya Daure babu Wanda aka taba sakashi cikin Wannan matakin ba batare da Kaga An samu Naasara ba.."
Gabadayansu suka Dau Salati Ya Muktar ya Dafe kai yana Fadin"Ya Allah gareka muke...Kuma gareka zamu koma...Mun yarda mu musulmai ne Mun karbi Jarabawanka Hannun bibbiyu ina Fatan Dukkanmu Allah ka bamu ikon Cinye wannan Jarabawan.."Yake fada yana Kifa kanshi bisa Tuberun Gabanshi yana kuka,Sani ma Hawayen yake Shida Modibbo Daada ko kanta na kasa Tana Share kwallah Aneesa Fita Tayi Daga Office din Tana kuka.
Dr khan da Dr.sunhat ne keta basu baki Cikin Harshen Turanci Lokaci daya suna mai Sanar dasu Akwai wani Baturan Likita Daga Kasar babban Birnin America U.S Wato Dr Philphil,kwararan Likitane kan Harkan Gaashin kashi,Duk bayan wata Shida yake Zuwa Asibitin nan yana musu aiki na Wata Uku,Toh insha Allahu zai zo nan da Kwana goma Saboda Bello Domin Sun Turamai Duka Record din Gwajen gwajensa Suna Fatan Wannan karon ayi Nasara.
Haruna yace"Ina ai sai dai kaga Tarin kashi da Fitsari Daga Zaune mallam.."Kara saka Dariya Sukayi kamar Wasu mahaukata,sai da sukayi ya ishesu kana Kasim yace"zan Tura maka duka kudin aikin kaje ka kai mai kamika sakon godiyata garesa,saboda office yasa bazan samu zuwa ba.."
Haruna yace"No wahala karka wani Damu.."Daga Haka suka yanke Kiran Bisa Kujera Kasim ya Fada yana Sakin Dariya Lokaci Daya yana Jefar da gwangwanin maltinan Dake hannunsa Wanda yagama Shanyewa Dariya yake Cike da Nishadi kafin ya Saki Mirmishi yana Shafa Sajensa yana Fadin"Aneesa kin kusa Dawo gareni Dama ke din Tawa ce Ni kadai..",yake fada yana kara sakin Wani mirmishi mai cike da Ma"anoni.....
****
_New Delhi_
Kwanansu uku kenan da zuwa kasar ammh haryanzu Dr khabir khan bai musu wani bayani ba Kuma Har Tsawon Wadanan kwanakin Bello na Cikin Dakin gwaje gwaje ba'a fito dashi ba saboda abunda ya matukar basu mamaki yadda duk sakamakon gwaje gwajen Dake Fitowa,Normal babu mtsalan Komai Shine Abunda yake basu mamaki ga Bello yana nan Jiya iyau abinci ma sai Cikin Ruwan Alluran dasuke Sakamai ne yake samun Karfin Jiki.
Akwana na Hudu ne Dr kabir khan ya kira ya Muktar Da ya Sunusi Da ya Hashim Zuwa Cikin Offce dinsu yana kora musu jawabin Sakamakon gwajen gwajen da Suka ma Duk wasu kasusuwan Bello Dake da alhakin Tashinshi ko Tsayuwarshi Haka bangaren Mganarsa ma Hatta Hotoon kansa da kwakwalawarsa sai da Sukayi ammh komai Normal yake Nuna musu.
Bayani yake musu Lokaci Daya yana Nuna musu gwajen gwajen Hotunan,ya muktar Daya Shiga wani yanayi Cikin Harshen Turanci yace"Dr bawani Taimako da zaku mana ne ,?nan ne kadai Hop dinmu.."Shuru Dr khabir khan yayi kafin yace"agaskiya bazai iya cewa komai ba yanzu Ammh mganar gaskiya Wannan ne Karo na Farko da Suka samu Irin wannan case din sai dai zasu jaraba sanyashi cikin Wasu Injina Na Tsawon Wata Daya Sukagani in Har Bai tashi ba zasu koma bangaren kashi toh gaskiya indai Duk Hakan bai sa ya tashi ba Toh basu da wani Abunda zasu ma Bello.."Hankalinsu Duk ya Tashi Sosai Da jin wannan bayani Cikin Daukewar Hawaye Muktar yace"ajaraba agani Insha Allahu inaji ajikinsa Bello zai Tashi.."Da wannan Shawaran Suka Rufe Tattaunawansu,sai kuma Ranar ne aka Fito da Bello Daga dakin gwaji zuwa dakin matakin Farko,Ba"a barsu sun Shiga ba ammh daga bakin kofar suna iya Hangensa ta Cikin galisan Wajen,Aneesa Ranar da kuka Wiwi Suka koma Masauki Saboda yadda aka sanya Bello Cikin Wani Inji mai Jijjigar da Jikin Mutum,Daada kuwa ta koka ta koka kamar Ranta Zai Fita Duk ta Zabge ta rame kamar ba Ita ba Wani Abun Tsausayin ma Mai Rai kwance ba mgana ba motsi sai dai Numfashi,rai mai alfarma kawai ammh kowani bawa yaga Halin da Bello ke Ciki sai ya Koka mai.
Kullum sai dai suzo su lekasa su koma Aneesa sai tafi awa Daya Tsaye tana kallonsa tana Share kwallah Ranar da Suka Cika Sati da Zuwa Ya Sunusi da ya Hashim suka barsu anan suka koma Nageria cike da Fatan samun lafiya ga Bello,Ya muktar kuwa da Anty Rahila sai da Sukayi Sati Uku kana Suka koma Shida Yara saboda mkranta da kuma Aiki aka bar Daada da Aneesa Wajen Bello wanda sai yayi Wata Daya Cikin Wannan Na"uran injin din kana Za"a Fito dashi asake sabon Gwaje gwaje.
Shikanshi Ya Muktar din yana Nageria ne ammh Zuciyarsa gabadaya suna india kafin Tahowarasu ya Siyama Aneesa Waya saboda jin Halin da Suke Ciki kullun dai Jiya iyau Kullum Ya Muktar Cikin Waya Suke da Dr Khan Amsa Daya ne,Sai wa"adi ya cika Kana za su sake Gwaji suga ko ansamu Cigaba,Kullum baya barcin kirki Salloli yake da addu"an Allah ya Tashi kafadun Bello,mutane Dadama sunzo har gidan Yimai jajen Abunda ya Faru Duka iyalan Abba kabiru da na Abba garba mama Sahura da Umma Zulfa da Zubaida wanda kowacce Dataj lbrin Abunda ya Faru da Bello sai da ta girgiza Cikin Zuciyar iyayensu kuwa Hamdala Suke Da ba wacce Ya Auri yarta da yanzu an sakasu Acikin Wahala Umma Harda cema Anty Rahila Aneesa ne Abun Tsausayi Da kuruciyarta Zata kare da Aikin gaton kwance Anty Rahila dai bata tanka mata ba Saboda Ta gane inda ta Dosa,Hatta Inna Rukayyah Daga kano tazo,ta kwana biyu ta koma,Shikanshi Kasim ya kira Ya Muktar awaya yana mai jaje harda Nuna Tsausayi Kamar na Allah Nan ko yana kashe Wayar yayi ta Dariya.
Mutanen Borno Kuwa Ya Ali yazo Shida Anty Nafee,sunyi kwana Daya Suka koma,bayan suma Anty Yagana tazo gwanin ban Tsausayi ba wacce suke Tsausayamawa Irin Aneesa Tana karamar yarinya ta Hadu da Jarabta Rayuwa.,Kawayen Aneesa Kuwa B.kaita ce Taji Aneesa Shuru sai ta kira Wayar Anty Rahila nan taji lbri mara Dadi ita ta Kira S.jibiya take gayamata Dukkansu sun jajaantama Aneesa Tare da yin alkawarin saka Mr bello Cikin Addu"o'insu.
Uncle Aminu Ko Dake Kasar Spain bai da Lbrin Abunda ke Faruwa Domin Tunda yayi ta kiran Nombar Bello bai samu ya Hakura tunda bashi da Nombar ya Muktar ammh kullum sukayi mgana da Ammi sai ya Tambayeta ko Bello yazo.? Nan take gayamai Tun Zuwanshi lokacin Daya sanar da ita zai Fara Lecturing a Buk kano bai kara Dawowa ba,Aminu ya Shiga damuwa sosai ammh yana kokarin ya kamallah abun ke gabanshi ya Dawo domin Sauranshi Wata Biyar yagama komai ya Dawo gida.
Sani bai samu lbri ba Sai Daga baya Har Abuja yazo yama Ya Muktar Jajen Abunda ya Faru ya kuma ce in zasu koma India zai bisu yaga Halin da Bello ke Cikin,achan india kuwa Daada ta bama Muktar Shawaran yaje Adamawa ya Taho da Modibbo,Mtsayin Jika yake gareta Saurayi ne irin bai yi karatun Boko mai Zurfi ba iyakarsa Sakandiri sai na Addini,aikin Gyaran Motici yake agarin Adamawa tace ya Daukosa Su Taho tare koda An Fito da Bello Aneesa Tayi kankantan Iya kula da Bello itakuma ta Tsufa ga jikin Girma Nan da nan ya karbi Shawaranta yaje har Adamawa ya Taho da Modibbo iyaye da yan"uwa nata Faman addu'an samun Sauki ga Bello.
Ana saura kwana Uku Afito Da Bello Suka Dira Akaasar india Shida Sani da Modibbo,Daga modibbo har Sani Suna Tsaye Cikin Kofar Dakin da Bello yake suna Hangensa Kwance sambal cikin Na"ura mai amfani da Na"urorin Computer,Sani na Hawaye modibbo nayi suna Tunanin bawa mai Rai ne Cikin Wannan Abun Lalle Allah kadai ne Mai Nuna aya alokacin dayaso Shi kanshi Ya Muktar yanzu bashi da wani karfin gwiwa kamar mace zaki ga yana Share Hawaye Shar Shar kamar ba Soja ba wanda yasha gwagwamaryan Rayuwa...
Awannan Dawowar ne ya Razana da Ganin yadda Aneesa ta koma Dama ba Auki ba,ta kara ramewa duk tayi baki,nan Daada ke Fadamai bata cin abinci sai kuka zama yayi yana ta lallashinta Tare da Sanar da ita bayan anfito da Bello sun ji sakamako in zai koma Nageria zai Tafi da ita nan Aneesa Taka Rushewa da kuka Tana babu inda Zata ita zata Zauna anan kukan Datakeyi sai da ta saka Ya Muktar share kwallah Saboda Tsausayinta.
Ranar da za"a fito da Bello Daga Cikin Wannan Injinan Dukkansu ba Wanda ya Runtsa kwana Sukayi Addu",an Allah ya sa ansamu Nasara matakin Farko Da Sassafe suka yi ma Asibitin Tsinke Likitoci Sunfi Goma Suka Shiga Dakin sun Dauki Tsawon Awanni Aciki kafin Su Fito basu ma kowa bayani ba Illah Dr khabir khan dayace musu Suyi ta Addu"a yanzu za"a kara Tafiya dashi Dakin gwaji abunda sakamako ya Fitar Shine zasu yi Aiki Dashi.
Aneesa Sulalewa Tayi Jikin Daada Tana Kuma duk Addu"an da tazo bakinta Daga gida Nageria ma Duka ya muktar Duk ya Kira su yana Rokon atayasu da Addu"a Anty Rahila ma Tuni ta Kira borno ta sanar dasu Kowa dai Yana ta Addu"an Allah ya sa Anyi a Sa"a.
Agaban idonsu aka Fito da Bello Zuwa Dakin Gwaji kamar gawa ya yi Fari kasumba ta cikamai Fuska da jiki,Numfashi ne kadai zai sa kagane Bello yana Da Rai,Tsawon awa Hudu Suka kwashe Cikin Dakin gwaji kafin Likitocin Su Fito,Yadda ya muktar yaga Fuskar Dr Khan ne yasa Yaji gwiwansa Tayi sanyi Hawaye Sun Taru Acikin kwarmin idanuwansa Daga yadda Indiyanwan Likitocin ke mgana zaka san Abun ya basu mamaki basu samu ganin Dr khan ba sai da Suka Fito Daga Meeting din Da Suka Shiga Akan Cutar Bello.
Gabadayansu Suka D'uru Cikin Office din Dr khan Lokacin yana Tare da Dr Sunhat,suna kara Duba Duka Record din Bello Suna kara mamaki Dr Khan ya Zare gilashin Idanuwanshi yana kallon Ya Muktar kafin yace"Am Srry to say...Ammh wannan Gwajin matakin Farko bamu Samu Nasara ba,Munyi matukar mamaki ganin yadda ya Fito Daga cikin Wannan Na"uran ammh kuma Duka Sakamakon Farko gwajin ke Nuna mana Gabadaya kanmu ya Daure babu Wanda aka taba sakashi cikin Wannan matakin ba batare da Kaga An samu Naasara ba.."
Gabadayansu suka Dau Salati Ya Muktar ya Dafe kai yana Fadin"Ya Allah gareka muke...Kuma gareka zamu koma...Mun yarda mu musulmai ne Mun karbi Jarabawanka Hannun bibbiyu ina Fatan Dukkanmu Allah ka bamu ikon Cinye wannan Jarabawan.."Yake fada yana Kifa kanshi bisa Tuberun Gabanshi yana kuka,Sani ma Hawayen yake Shida Modibbo Daada ko kanta na kasa Tana Share kwallah Aneesa Fita Tayi Daga Office din Tana kuka.
Dr khan da Dr.sunhat ne keta basu baki Cikin Harshen Turanci Lokaci daya suna mai Sanar dasu Akwai wani Baturan Likita Daga Kasar babban Birnin America U.S Wato Dr Philphil,kwararan Likitane kan Harkan Gaashin kashi,Duk bayan wata Shida yake Zuwa Asibitin nan yana musu aiki na Wata Uku,Toh insha Allahu zai zo nan da Kwana goma Saboda Bello Domin Sun Turamai Duka Record din Gwajen gwajensa Suna Fatan Wannan karon ayi Nasara.