Sashe 9
Al'adun Wasu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Izzatu ta sakawa Khalifa da Junior kayansu. Rigace mai dogon hannu da dogon wando duk sun dame musu jiki ga kuma fuska wadda aka fitarwa hudar idanu da wurin numfashi. Kayan bakake ne. Idan daga nesa ka hangosu zaka rantse kwarangwal ne saboda zanen kayan da yanayinsu. Bayan ta shiryasu ta daukesu hoto ta turawa Hamza a waya. Daga nan taje ta dauko na Nana. Su kuma jajaye ne harda safar hannu mai alamar farata zako zako. Fuskar(mask) kuwa kamar ta aljanu harda kaho biyu a sama. Nana tana ta dariya Izzatu ta gama shiryata ta daukota zasu fito falo sai Nana tace Mummy poo. Izzatu ta san halin Nana bata kashi a pampers duk yadda za'ayi da ita. Dole ta cire mata ta zame mata wandon ta dorata a po ta tafi kitchen duba girki don shabiyun rana ta wuce. Junior da Khalifa suna falonsu suna kallon cartoon.
Tana kitchen taji sallamar su Mama. Da sauri ta fito tana musu sannu da zuwa. Duk su biyun rungume su tayi yadda ta saba. Hajiya sai dan yake take don wannan halin na Izzatu na bata kunya. Bayan sun zauna ta gaishesu Mama tace ina Khalifan? Ashe baiji dadi ba. Izzatu tace eh amma yau da sauki sosai. Zazzabi ne da mura. Hajiya tace to Allah Ya bashi lafiya. Mama tace kirawo shi mu ganshi. Dazu babansa yayi min waya da safe shine muka zo duba shi. Izzatu tace Tala ta dauko musu ruwa da lemo.
Tala na tashi Nana ta fara ihun Mummy na gama da dan gwarancinta. Izzatu tace jeki kiyi mata tsarki bari na kawo musu. Tashi tayi tana kiran su Junior su zo ga su Hajita ta shige kitchen.
Ba'a fi rabin minti da shigar Tala ciki ba ta fito falo tana ihu. Gabadaya jikinta rawa yake sosai tana kuka. Hajiya da Mama suka tashi a firgice suna tambayarta abinda ya faru. Cikin kuka tace mutanen boye sun bayyana. Mama tace su wa? Tala tace aljanun. Yau na gansu da idona ra'ayil aini har su biyu. Wallahi sai ga yarsu zaune akan po din Nana dayan kuma yana mata wasa. Na higa uku na lalace kwarankwatsa ko a kauyenmu ban taba gamo ba he yau. Izzatu ce ta fito da sauri daga kitchen tace ke Tala bana son rashin hankalin nan naki.
[9/25, 3:33 PM] ‪+234 803 040 6305‬: AL'ADUN WASU 🗿14
Batul Mamman(Mrs)💖
Tala ta zazzaro idanu tana kallon Izzatu. Na rantse ba karya nake ba. Hajiya da Mama sai kallonsu suke yi. Tala na maida zance suka ji kukan Nana tana kiran Izzatu. Tare duk suka yi hanyar inda suka ga Tala ta fito. Hajiya ce a gaba. Sai da cikinta yayi mugun kadawa saboda abinda ta gani zaune akan po yana miko hannu alamar ta dauke shi. Na kusa dashi kuma mai siffar kwarangwal ya rugo da gudu zai rungumeta. Da kyar ta iya cewa Hasbunallahu wa ni'imal wakil sannan tayi baya kamar zata fadi. Mama tayi saurin tareta itama a tsorace har ta fara tunanin kada aljanun su rufe kofar gidan su hanasu fita. Tala tace kun gani ko Hajiya ai na fada muku. Nana dai tasowa tayi ta nufo su shima Junior haka. Khalifa da yake kwance a daki shima ya fito saboda hayaniyar da yaji. Mama ta karewa aljanun uku kallo tace Hajiya gidan Yaya ba lafiya. Izzatu ce karshen shigowa tana ganin abinda ya kidima surukanta ta kyalkyale da dariya harda hawaye, karshe sai da ta kai kasa. Hajiya da Mama sai kallon kallo a zatonsu ma ko aljanun sun taba ta. Sai da tayi mai isarta suna kallonta sannan tace Hajiya su Nana ne fa. Kaya ne na saka musu yau halloween. A gabansu ta cire musu fuskar kayan tana mai cigaba da dariya.
Ransu Hajiya yayi matukar baci. Tala kuwa karasawa tayi gaban yaran tace Khalifa kaine tana tattaba musu jiki. Ta dago kai tace Hajiya ai kuwa su din ne. Mama ta dubi Izzatu, hallo...me kika ce? Izzatu tace halloween. 31st October ake yi. Lokacin da muna Canada muna yinsa sosai. Tsabar bacin rai Hajiya ta kasa magana ma. Karshen wulakanci da cin mutumci Izzatu tayi musu.
Mama tace Hajiya ai sai mu tafi ko, don banga dalilin zamanmu ba. Su Junior suna ta binsu suna cewa zasu bi su. Cikinsu babu wadda ta iya kula yaran saboda yadda zukatansu ke kuna. Izzatu tace muje falo ku sha ruwa don ita bata dauki shirunsu a matsayin bacin rai ba. Sun kai bakin kofa zasu fita idon Mama ya kai kan wani mutum mutumi mai siffar mutum kafarsa ta akuya ga kaho har a saman hanci. Shima duk cikin kayan kwalliyar gidan ne na halloween. Cikin Mama har murdawa yayi, gabanta ya fadi don abin ya bata tsoro har kafarta ta goce ta fadi kasa. Hajiya tayi saurin durkusawa ta taimaka mata ta tashi. Junior da Khalifa ma suna ta cewa sannu Grams. Ita kuwa Izzatu wata dariyar ce ta subuce mata. A ranta tace ko ba komai ta rama abinda suka yi mata na sa Hamza ya hana su party.
A fusace Hajiya ya dago kanta cikin zafin rai zata yiwa Izzatu magana Hamza yayi sallama. Ganin Mama na kokarin mikewa yayi saurin karasawa gabanta yana tambayar abinda ya faru. Dama zuciyar Hajiya a kusa take maimakon ta bashi amsa ta kwashe shi da mari. Falon a take yayi tsit Tala tayi saurin komawa dakin su Khalifa ta ga an mari ubangidanta. Falon yayi tsit Izzatu ta hadiye sauran dariyarta. Shi kuwa hannuwansa biyu yasa ya dafe kumatunsa ya dubi mahaifiyarsa a razane. Mama tace haba Hajiya ya zaki dauki hukunci kan wanda baiji ba bai gani ba. Murmushin takaici Hajiyan tayi tace tunda nake ban taba ganin wulakancin da yayi min ciwo irin wannan ba. HAMZA ka guji ranar da zanyi maka baki.....idanunsa sunyi jawur yana mamakin sunansa da ta fada da kuma dalilin bacin ranta. Yace da Izzatu me ya faru? Ta dan tabe baki babu komai. Don basu dade da zama ba suka tashi. Hajiya da Mama suka yi hanyar kofa yana ta basu hakuri da son jin abinda ya faru sunki sauraronsa. Har bakin mota ya biyo su. Sai da dreban ya tada motar sannan Hajiya tace wallahi in dai da raina da lafiyata Hamza bazan kara taka kafata nazo gidanka ba. Mama da yake tunanin zata bata hakuri ko kallon inda yake bata yi ba. Sai ma kwalla da yaga tayi saurin sharewa kafin motar ta fita daga harabar gidan.
Da sauri ya shiga gidan yana kwalawa Izzatu kira. Ta fito hankali kwance tace sweetheart abinci zaka fara ci ko wanka. Izzy kina da hankali kuwa? Ya dubi su Junior kai ku koma dakinku. Sai da yaran suka tafi yace idan naki iyayen ne suka fita haka zaki musu? Ki fada min gaskiya me akayiwa su Hajiya. Izzatu tace ni ban sani ba. Suna ganin su Khalifa suka kama hanyar fita. A daidai can ne mama ta dan fadi. Hamza yace ta fadi? Ya karasa yaga gunki a wurin ya dago shi..meye wannan kuma? Izzatu tayi yar dariya na halloween ne. Ka tuna sanda akeyi a Canada? Akwai da yawa naso gama jerasu kafin ka dawo. Ya ce wane irin hoto kika turo min dazu? Ni abinda ya dawo dani kenan. Izzatu ta riko hannunsa zo mu zauna babyna. Ta kira yaran sai a lokacin ya kula da kayan jikinsu. Na nana yafi tada hankali ya mike a fusace izzy dont tell me haka su Mama suka ga yaran nan. Tace haka suka gansu mana. So what? Dafe kansa kawai yayi yana karanta Innalillahi a zuci. A hankali yace Izzy don Allah ki ajiye al'adun wasu a gefe mu zauna lafiya. Yadda Hajiya ta rantse ta bar zuwa gidana na miki rantsuwa da Allah idan kika sake dauko min wani abu da bai dace da dabiar musulmi ba sai na bata miki rai. Bacin rai wanda sai kinyi nadamar aurena. Iya nasihar da zanyi miki nayi nima na gane rashin kyautuwar abinda muka yi a baya. Kina zaune lafiya da iyayenki baki isa ki rabani da nawa ba. This....ya nuna ta da dan yatsa is my last warning.
[9/25, 3:33 PM] ‪+234 803 040 6305‬: AL'ADUN WASU 🗿15
Batul Mamman(Mrs)💖
Yana gama magana ya tashi yana kwalawa Tala kira. Da yake tana labe a bayan kofa da gudu ta fito jiki na rawa yace jeki ki cire musu kayan nan ki kawo min mota ina jiranki. To kawai tace ta kwasa da gudu tayi ciki. Izzatu ta kalleshi itama rai a bace kudi fa nasa na sayi kayan nan. Me zakayi dasu?. Ya dan daga gira daya Allah ko? Tunda kudin nawa ne babu ruwanki da abinda zanyi. A iya zamansu basu taba samun sabani kamar yadda suke yi yan watannin nan ba. Kirikiri iyayensa ke nuna mata kiyayya amma zata yi maganin abin. Ta yanke shawarar bazata taba bari maganganunsu suyi tasiri a ranta ba har ta dena rayuwarta yadda ta saba. Ita tasan iyayenta sun bata tarbiyya irin wadda ta dace kuma ga yayarta da mijinta suna zamansu lafiya sai ita kadai ce zasu takurawa.
Horn Hamza ya rinka dannawa da karfi sai ga Tala kamar an jeho ta. Ta mika masa kayan. Har ya dan ja motar sai ya dawo ya sake kiranta. Ke fada min gaskiya me ya faru da su Hajiya suka zo dazu? Ai kamar jira take ta soma bayani dalla dalla. Dama banda tsoron da taji ba karamin mamakin Izzatu tayi ba da tayiwa surukanta dariya. Fuskar nan ta Hamza kamar bai taba dariya ba ya ja mota ya nufi gidan iyayensa.
Tana kitchen taji sallamar su Mama. Da sauri ta fito tana musu sannu da zuwa. Duk su biyun rungume su tayi yadda ta saba. Hajiya sai dan yake take don wannan halin na Izzatu na bata kunya. Bayan sun zauna ta gaishesu Mama tace ina Khalifan? Ashe baiji dadi ba. Izzatu tace eh amma yau da sauki sosai. Zazzabi ne da mura. Hajiya tace to Allah Ya bashi lafiya. Mama tace kirawo shi mu ganshi. Dazu babansa yayi min waya da safe shine muka zo duba shi. Izzatu tace Tala ta dauko musu ruwa da lemo.
Tala na tashi Nana ta fara ihun Mummy na gama da dan gwarancinta. Izzatu tace jeki kiyi mata tsarki bari na kawo musu. Tashi tayi tana kiran su Junior su zo ga su Hajita ta shige kitchen.
Ba'a fi rabin minti da shigar Tala ciki ba ta fito falo tana ihu. Gabadaya jikinta rawa yake sosai tana kuka. Hajiya da Mama suka tashi a firgice suna tambayarta abinda ya faru. Cikin kuka tace mutanen boye sun bayyana. Mama tace su wa? Tala tace aljanun. Yau na gansu da idona ra'ayil aini har su biyu. Wallahi sai ga yarsu zaune akan po din Nana dayan kuma yana mata wasa. Na higa uku na lalace kwarankwatsa ko a kauyenmu ban taba gamo ba he yau. Izzatu ce ta fito da sauri daga kitchen tace ke Tala bana son rashin hankalin nan naki.
[9/25, 3:33 PM] ‪+234 803 040 6305‬: AL'ADUN WASU 🗿14
Batul Mamman(Mrs)💖
Tala ta zazzaro idanu tana kallon Izzatu. Na rantse ba karya nake ba. Hajiya da Mama sai kallonsu suke yi. Tala na maida zance suka ji kukan Nana tana kiran Izzatu. Tare duk suka yi hanyar inda suka ga Tala ta fito. Hajiya ce a gaba. Sai da cikinta yayi mugun kadawa saboda abinda ta gani zaune akan po yana miko hannu alamar ta dauke shi. Na kusa dashi kuma mai siffar kwarangwal ya rugo da gudu zai rungumeta. Da kyar ta iya cewa Hasbunallahu wa ni'imal wakil sannan tayi baya kamar zata fadi. Mama tayi saurin tareta itama a tsorace har ta fara tunanin kada aljanun su rufe kofar gidan su hanasu fita. Tala tace kun gani ko Hajiya ai na fada muku. Nana dai tasowa tayi ta nufo su shima Junior haka. Khalifa da yake kwance a daki shima ya fito saboda hayaniyar da yaji. Mama ta karewa aljanun uku kallo tace Hajiya gidan Yaya ba lafiya. Izzatu ce karshen shigowa tana ganin abinda ya kidima surukanta ta kyalkyale da dariya harda hawaye, karshe sai da ta kai kasa. Hajiya da Mama sai kallon kallo a zatonsu ma ko aljanun sun taba ta. Sai da tayi mai isarta suna kallonta sannan tace Hajiya su Nana ne fa. Kaya ne na saka musu yau halloween. A gabansu ta cire musu fuskar kayan tana mai cigaba da dariya.
Ransu Hajiya yayi matukar baci. Tala kuwa karasawa tayi gaban yaran tace Khalifa kaine tana tattaba musu jiki. Ta dago kai tace Hajiya ai kuwa su din ne. Mama ta dubi Izzatu, hallo...me kika ce? Izzatu tace halloween. 31st October ake yi. Lokacin da muna Canada muna yinsa sosai. Tsabar bacin rai Hajiya ta kasa magana ma. Karshen wulakanci da cin mutumci Izzatu tayi musu.
Mama tace Hajiya ai sai mu tafi ko, don banga dalilin zamanmu ba. Su Junior suna ta binsu suna cewa zasu bi su. Cikinsu babu wadda ta iya kula yaran saboda yadda zukatansu ke kuna. Izzatu tace muje falo ku sha ruwa don ita bata dauki shirunsu a matsayin bacin rai ba. Sun kai bakin kofa zasu fita idon Mama ya kai kan wani mutum mutumi mai siffar mutum kafarsa ta akuya ga kaho har a saman hanci. Shima duk cikin kayan kwalliyar gidan ne na halloween. Cikin Mama har murdawa yayi, gabanta ya fadi don abin ya bata tsoro har kafarta ta goce ta fadi kasa. Hajiya tayi saurin durkusawa ta taimaka mata ta tashi. Junior da Khalifa ma suna ta cewa sannu Grams. Ita kuwa Izzatu wata dariyar ce ta subuce mata. A ranta tace ko ba komai ta rama abinda suka yi mata na sa Hamza ya hana su party.
A fusace Hajiya ya dago kanta cikin zafin rai zata yiwa Izzatu magana Hamza yayi sallama. Ganin Mama na kokarin mikewa yayi saurin karasawa gabanta yana tambayar abinda ya faru. Dama zuciyar Hajiya a kusa take maimakon ta bashi amsa ta kwashe shi da mari. Falon a take yayi tsit Tala tayi saurin komawa dakin su Khalifa ta ga an mari ubangidanta. Falon yayi tsit Izzatu ta hadiye sauran dariyarta. Shi kuwa hannuwansa biyu yasa ya dafe kumatunsa ya dubi mahaifiyarsa a razane. Mama tace haba Hajiya ya zaki dauki hukunci kan wanda baiji ba bai gani ba. Murmushin takaici Hajiyan tayi tace tunda nake ban taba ganin wulakancin da yayi min ciwo irin wannan ba. HAMZA ka guji ranar da zanyi maka baki.....idanunsa sunyi jawur yana mamakin sunansa da ta fada da kuma dalilin bacin ranta. Yace da Izzatu me ya faru? Ta dan tabe baki babu komai. Don basu dade da zama ba suka tashi. Hajiya da Mama suka yi hanyar kofa yana ta basu hakuri da son jin abinda ya faru sunki sauraronsa. Har bakin mota ya biyo su. Sai da dreban ya tada motar sannan Hajiya tace wallahi in dai da raina da lafiyata Hamza bazan kara taka kafata nazo gidanka ba. Mama da yake tunanin zata bata hakuri ko kallon inda yake bata yi ba. Sai ma kwalla da yaga tayi saurin sharewa kafin motar ta fita daga harabar gidan.
Da sauri ya shiga gidan yana kwalawa Izzatu kira. Ta fito hankali kwance tace sweetheart abinci zaka fara ci ko wanka. Izzy kina da hankali kuwa? Ya dubi su Junior kai ku koma dakinku. Sai da yaran suka tafi yace idan naki iyayen ne suka fita haka zaki musu? Ki fada min gaskiya me akayiwa su Hajiya. Izzatu tace ni ban sani ba. Suna ganin su Khalifa suka kama hanyar fita. A daidai can ne mama ta dan fadi. Hamza yace ta fadi? Ya karasa yaga gunki a wurin ya dago shi..meye wannan kuma? Izzatu tayi yar dariya na halloween ne. Ka tuna sanda akeyi a Canada? Akwai da yawa naso gama jerasu kafin ka dawo. Ya ce wane irin hoto kika turo min dazu? Ni abinda ya dawo dani kenan. Izzatu ta riko hannunsa zo mu zauna babyna. Ta kira yaran sai a lokacin ya kula da kayan jikinsu. Na nana yafi tada hankali ya mike a fusace izzy dont tell me haka su Mama suka ga yaran nan. Tace haka suka gansu mana. So what? Dafe kansa kawai yayi yana karanta Innalillahi a zuci. A hankali yace Izzy don Allah ki ajiye al'adun wasu a gefe mu zauna lafiya. Yadda Hajiya ta rantse ta bar zuwa gidana na miki rantsuwa da Allah idan kika sake dauko min wani abu da bai dace da dabiar musulmi ba sai na bata miki rai. Bacin rai wanda sai kinyi nadamar aurena. Iya nasihar da zanyi miki nayi nima na gane rashin kyautuwar abinda muka yi a baya. Kina zaune lafiya da iyayenki baki isa ki rabani da nawa ba. This....ya nuna ta da dan yatsa is my last warning.
[9/25, 3:33 PM] ‪+234 803 040 6305‬: AL'ADUN WASU 🗿15
Batul Mamman(Mrs)💖
Yana gama magana ya tashi yana kwalawa Tala kira. Da yake tana labe a bayan kofa da gudu ta fito jiki na rawa yace jeki ki cire musu kayan nan ki kawo min mota ina jiranki. To kawai tace ta kwasa da gudu tayi ciki. Izzatu ta kalleshi itama rai a bace kudi fa nasa na sayi kayan nan. Me zakayi dasu?. Ya dan daga gira daya Allah ko? Tunda kudin nawa ne babu ruwanki da abinda zanyi. A iya zamansu basu taba samun sabani kamar yadda suke yi yan watannin nan ba. Kirikiri iyayensa ke nuna mata kiyayya amma zata yi maganin abin. Ta yanke shawarar bazata taba bari maganganunsu suyi tasiri a ranta ba har ta dena rayuwarta yadda ta saba. Ita tasan iyayenta sun bata tarbiyya irin wadda ta dace kuma ga yayarta da mijinta suna zamansu lafiya sai ita kadai ce zasu takurawa.
Horn Hamza ya rinka dannawa da karfi sai ga Tala kamar an jeho ta. Ta mika masa kayan. Har ya dan ja motar sai ya dawo ya sake kiranta. Ke fada min gaskiya me ya faru da su Hajiya suka zo dazu? Ai kamar jira take ta soma bayani dalla dalla. Dama banda tsoron da taji ba karamin mamakin Izzatu tayi ba da tayiwa surukanta dariya. Fuskar nan ta Hamza kamar bai taba dariya ba ya ja mota ya nufi gidan iyayensa.