Sashe 19
Al'adun Wasu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Hakkinta ne na ciyar da ita" yana fadin haka ya hau saman.
Ya kusa minti biyu kafin ya murda kofar ya shiga. Akwai kamshi dai saboda dakin amarya ne sai dai zafi sosai duk da tagar a bude take. Ko meyasa bata kunna AC ba oho.
A tsaye take tana jera kayanta a wardrobe har ta kusa gamawa taji an taba kofar. Cikinta sai da ya bada sauti saboda tsoro. Ko da ya shigo duk rashin kunyar da taso yi masa sai ta fasa saboda yadda ya cika mata ido. Bata taba kare masa kallo ba sai yau. Da ace zaman lafiya suke yi da ta fada masa yadda yayi kyau. Shima ita yake kallo. Riga da skirt tasa na atampa fuskar nan tasha farar hoda. Kana ganinta ita daban fuskar ma daban. Ga hannun breziya ya fito ta kowane gefen hannun rigarta. Ya dan tabe baki....kai kuma irin taka jarabawar kenan Hamza.
"Ke baki iya gaisuwa bane?"
Saurin durkusawa tayi tare da jin kunya.
"Ina kwana, an tashi lafiya"?
Bai amsa ba ya juya"ki sauko muyi breakfast".
Kafin ya kai kofa ta biyo bayan shi. Yunwa take ji sosai. Ace yau har shadaya saura bata ci abinci ba. Ita kanta tasan tayi abinda zaa jinjina mata.
A baya ta rinka binsa har suka sauko. Izzatu ta kai karshe wurin bacin rai, sai kawai ta danne. Kujera ta samu kusa da yaran ta zauna tare da yin sallama. Khalifa ne kawai ya amsa. Ya kalli Mamansa.
"Mummy wannan ma mai aiki ce?"
Hamza ya ce masa yayi shiru kawai yaci abinci. Zuhra tana sane bata ji ya gyara masa yace ita ba mai aiki bace ko da bai kirata matarsa ba.
Izzatu ko daga kai batayi ba bare ta bashi amsa. Itama Zuhra taki kallonta. Yadda take jin haushin Izzatu ko kallo bata isheta ba. A dalilinta tazo gidan nan da bata da wata kima a idon mazauna cikinsa. Muryar Hamza ce ta katse mata tunani.
"Wai ba kya gaishe da mutane ne?"
Ta dago fuska suka hada ido. "Na gaisheka a daki"
Da kansa yayi mata alamar bata gaishe da Izzatu ba. Amma lallai ya rainata da yawa. Su basu ce 'ya'yansu su gaisheta ba sai ita zata gaishe da matarsa. Kamar bazata yi ba sai kuma tace "ina kwana"
Maimakon ta amsa sai kawai ta tashi ta koma dakinta. Hamza ya bi bayanta. Yaran ma suka gama suka tashi. Suna tafiya Zuhra ta janyo flask ta bubbude sannan ta debi abinda zata ci ta hada tea. Sai da taci ta koshi sannan ta tashi daga dinning area din ta koma wurin yaran inda suke zaune suna kallo. Tambayarsu sunayensu tayi suka bata amsa. Junior yace "ke kuma ya sunanki?".
Murmushi tayi "sunana Zuhra". Khalifa yace "nice name, will you be my friend?"
Ido ta dan zaro "tohhh kun iya turanci tun yanzu..." da haka suka rinka hira da ita tana jansu da wasa. Hatta Nana mai kyuya ta yarda da Zuhra.
Hamza ya dauko laptop zai fara aiki sai kuma ya rufe. "Izzy kirawo yarinyar nan, I need to talk to both of you"
Wani irin kallo tayi masa. " sweety nice zani dakin Zuhra? Allah Ya kiyaye. Kuma ai bai kamata ta shigo mana bedroom ba. As far as am concerned ni ban dauketa matarka ba."
"Gashi kuma na biya sadaki" yadda yayi maganar tasan har yanzu yana ganin laifinta a matsayin wadda ta jawo masa auren.
Tana fitowa ta jiyo muryar Junior yana cewa Zuhra ta yi masa tatsuniya. Daga saman ta leka ta kirawo Khalifa. Shi ta fadawa ya rako Zuhra dakin daddysu yana jiranta.
Rike da hannun Khalifa suka shiga dakin. Wata irin niima taji. Ita nata dakin sai zafi. Falo ne a farko sannan kofar dakin daga ciki. Wurin ya tsaru sosai ta tsaya tana kallo. Izzatu tace da Khalifa yaje wurinsu Junior.
Babu wadda ta kula yar uwarta har Hamza ya fito. Kusa da Izzatu ya zauna. Ita Zuhra kasa ta zauna kan kafet saboda gudun kada ace tayi laifi. Gyara zamansa yayi fuskarsa ta nuna alamun ba wasa. Sannan ya soma magana
"Kamar yadda kuka sani dukkaninku matana ne duk da cewa circumstances behind auren kowacce is different......
Zuhra anzo wurin...gabadaya jumlar karshe bata fahimta ba.
.....bana son tashin hankali a gidan nan. Izzy kece babba ina so kija girmanki. Ke kuma ya juya ga Zuhra ki bata girmanta. Tun farko na gargadeki akan auren nan kika ki ji. So duk abinda kika gani sai kiyi hakuri. Sannan a yanzu baki da kitchen don sai an gyara miki daki a kasa. For now idan Izzy tayi girki zata baki. Saboda haka babu zancen rabon kwana sai an gama kitchen din." Ya kallesu duk su biyu. "Ko akwai mai magana?"
Izzatu tana ta kumbure kumbure tace " ka fada mata ta fita harkar yarana".
Bai ce mata komai ba yace da Zuhra tana iya tafiya. Tunda ya soma magana bata daga kai ba. Yayi tsammanin zata nuna bacin rai amma sai yaga tayi shiru. Kanta a kasa ta fita daga dakin ta koma nata. Tana rufe kofar ta suma kuka duk yadda taso daurewa ta kasa....ba son Hamza take ba amma babu macen da zata so a nuna mata ita ba komai bace a gaban kishiya.
[9/25, 3:50 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 31
Batul Mamman(Mrs)
Sai karfe uku da rabi Tala ta kwankwasa mata kofa. Ko da ta bude abinci ne a plate an rufe da wani sai ruwa roba daya mai sanyi da cup. Godiya tayi mata ta karba. Gara a rinka kawo mata don ita bata jin zata iya jurar zama tare da mutanen da basa kaunarta su ci abinci.
Dama tuni ta soma jin yunwa. Tana budewa taliya ce da miya sai coleslaw a gefe. Kare masa kallo tayi tana mamaki. Abin kuma harda rowar abinci? Abincin dan kukut a plate kamar zaa bawa Khalifa. Tas ta cinye ta sha ruwa rabin robar. In ba haka tayi ba tasan bazata koshi ba.
Hamza tun bayan azahar suka fita da wani abokinsa. Gidansu Zuhra suka je yi musu ban gajiya. Su Umma sunji dadi sosai. Har ta cire kunyarta ta tambayeshi ya Zuhra ta kwana. Murmushi yayi sannan yace mata lafiya kalau. Tana gaishe su. Da zasu tafi Baba ya bawa Hamza wayar Zuhra. A jakar Hajara ta manta ta daren jiya. Juya wayar ya rinka yi, banda tsufa ta dade da fita yayi.
Da daddare ma har daki aka biyota da abincin. Macaroni ce da vegetable soup. Sai dai Zuhra ta tsani macaroni. Duk yunwar da take ji dole ta hakura. Gudun kada aga kwadayinta ma ko naman dake cikin miyar bata ci ba ta dauki tray din ta sauka kasa dashi. Tana tafiya Hamza da Izzatu dake zaune a dinning table na binta da ido. Bata ko tanka musu ba ta wuce ta ajiye abincin a kitchen. Ta fito kenan Tala ta biyota da sauri.
"Naga baki ci abincin ba"
Dan murmushi tayi "na koshi ne".
Tana wucewa idonta ya kai kan nasu abincin. Shinkafa suke ci, wato ita suka hada da macaroni. Hamza na lura da irin kallon da take musu har ta wuce.
Wurin karfe goma da rabi Zuhra tana zaune tunani duk ya isheta gashi ta manta wayarta a gida. Ga uwa uba yunwa. Turo kofar taji anyi tayi saurin tashi zaune ta saka hijab. Daga ita sai daurin kirji saboda zafi ya dameta.
Kafin ta rufe jikinta ya kula da daurin kirjin. Ba karamin tsanar sa yayi ba. Bai tsaya jan zance da ita ba yace..
" kina jindadin cin abincin ke kadai ko zaki rinka ci tare damu?"
Tasan har ransa ba so yake taci dasu din ba." Zanci ni kadai"
"Fine, sai ki rinka fada da wuri idan bazaki ci ba saboda a dena wasting. An kawo miki kin mayar batare da kin taba ba".
Idan kika yi shiru zaki kwari kanki shine abinda zuciyarta ke raya mata. Ta dan rage murya "bana cin macaroni ne"
"Macaroni kuma? Mtsw ke bana son karya."
Turo baki tayi "ni ba karya nake ba. Abinda aka kawo min kenan."
Dafa kansa yayi yadda yake idan yana cikin damuwa." Me yasa bakiyi magana ba. Anyway nasan shinkafar bata kare ba idan kina so kije ki ci."
Tana kallo ya karaso cikin dakin ya kunna wani abu. Da yake tana setin AC din tuni ta fara jin iska. Yana gani tayi murmushi. Sannan tace.
"Don Allah ina ka kunna? Jiya zafi ya isheni na zata da sankarau zan tashi da safe"
Ta kusa sashi dariya sai ya gimtse. Idan ya sakar mata fuska zata yi tunanin ta sami karbuwa ne. Remote din AC din ya nuna mata sannan ya miko mata wayarta da chaja a cikin leda. Murna tayi sosai tayi masa godiya.
Sai da ya kama hannun kofar ta sake magana tana sosa keya.
"uhmmm"
Ya tsaya yana kallonta
"yes" ganin taki magana.
"Dama, dama famfon bandakin ne naga kamar sun lalace."
"Kin lalata su dai" ya fada yana shiga ciki. Ya duba duka komai lafiya kalau. Ya fito "wai ni abokin wasanki ne? Babu famfon da ya lalace"
Bata ce komai ba tayi saurin shiga. Hannu ta tara a famfon sink da baho duk ruwa ya fito da kansa. Sai da ya tsorata ta duk da ta gani jiya. " ka gani ko, yau tun sallar asuba da shaya nake yin alwala."
Wannan karon murmushi yayi. Sannan yayi mata bayanin yadda kan famfon yake. Tun kafin ya fita ta rinka bi tana tara hannu ruwa na zuba. Dariya take yi don abin ya burgeta. Yace to kada ki karar mana da ruwan gidan. Kunya taji tayi saurin cire hannunta ta fito. Shi kuwa tuni ya fice ya tafi nasa dakin.
[9/25, 3:51 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 32
Batul Mamman(Mrs)
Ya kusa minti biyu kafin ya murda kofar ya shiga. Akwai kamshi dai saboda dakin amarya ne sai dai zafi sosai duk da tagar a bude take. Ko meyasa bata kunna AC ba oho.
A tsaye take tana jera kayanta a wardrobe har ta kusa gamawa taji an taba kofar. Cikinta sai da ya bada sauti saboda tsoro. Ko da ya shigo duk rashin kunyar da taso yi masa sai ta fasa saboda yadda ya cika mata ido. Bata taba kare masa kallo ba sai yau. Da ace zaman lafiya suke yi da ta fada masa yadda yayi kyau. Shima ita yake kallo. Riga da skirt tasa na atampa fuskar nan tasha farar hoda. Kana ganinta ita daban fuskar ma daban. Ga hannun breziya ya fito ta kowane gefen hannun rigarta. Ya dan tabe baki....kai kuma irin taka jarabawar kenan Hamza.
"Ke baki iya gaisuwa bane?"
Saurin durkusawa tayi tare da jin kunya.
"Ina kwana, an tashi lafiya"?
Bai amsa ba ya juya"ki sauko muyi breakfast".
Kafin ya kai kofa ta biyo bayan shi. Yunwa take ji sosai. Ace yau har shadaya saura bata ci abinci ba. Ita kanta tasan tayi abinda zaa jinjina mata.
A baya ta rinka binsa har suka sauko. Izzatu ta kai karshe wurin bacin rai, sai kawai ta danne. Kujera ta samu kusa da yaran ta zauna tare da yin sallama. Khalifa ne kawai ya amsa. Ya kalli Mamansa.
"Mummy wannan ma mai aiki ce?"
Hamza ya ce masa yayi shiru kawai yaci abinci. Zuhra tana sane bata ji ya gyara masa yace ita ba mai aiki bace ko da bai kirata matarsa ba.
Izzatu ko daga kai batayi ba bare ta bashi amsa. Itama Zuhra taki kallonta. Yadda take jin haushin Izzatu ko kallo bata isheta ba. A dalilinta tazo gidan nan da bata da wata kima a idon mazauna cikinsa. Muryar Hamza ce ta katse mata tunani.
"Wai ba kya gaishe da mutane ne?"
Ta dago fuska suka hada ido. "Na gaisheka a daki"
Da kansa yayi mata alamar bata gaishe da Izzatu ba. Amma lallai ya rainata da yawa. Su basu ce 'ya'yansu su gaisheta ba sai ita zata gaishe da matarsa. Kamar bazata yi ba sai kuma tace "ina kwana"
Maimakon ta amsa sai kawai ta tashi ta koma dakinta. Hamza ya bi bayanta. Yaran ma suka gama suka tashi. Suna tafiya Zuhra ta janyo flask ta bubbude sannan ta debi abinda zata ci ta hada tea. Sai da taci ta koshi sannan ta tashi daga dinning area din ta koma wurin yaran inda suke zaune suna kallo. Tambayarsu sunayensu tayi suka bata amsa. Junior yace "ke kuma ya sunanki?".
Murmushi tayi "sunana Zuhra". Khalifa yace "nice name, will you be my friend?"
Ido ta dan zaro "tohhh kun iya turanci tun yanzu..." da haka suka rinka hira da ita tana jansu da wasa. Hatta Nana mai kyuya ta yarda da Zuhra.
Hamza ya dauko laptop zai fara aiki sai kuma ya rufe. "Izzy kirawo yarinyar nan, I need to talk to both of you"
Wani irin kallo tayi masa. " sweety nice zani dakin Zuhra? Allah Ya kiyaye. Kuma ai bai kamata ta shigo mana bedroom ba. As far as am concerned ni ban dauketa matarka ba."
"Gashi kuma na biya sadaki" yadda yayi maganar tasan har yanzu yana ganin laifinta a matsayin wadda ta jawo masa auren.
Tana fitowa ta jiyo muryar Junior yana cewa Zuhra ta yi masa tatsuniya. Daga saman ta leka ta kirawo Khalifa. Shi ta fadawa ya rako Zuhra dakin daddysu yana jiranta.
Rike da hannun Khalifa suka shiga dakin. Wata irin niima taji. Ita nata dakin sai zafi. Falo ne a farko sannan kofar dakin daga ciki. Wurin ya tsaru sosai ta tsaya tana kallo. Izzatu tace da Khalifa yaje wurinsu Junior.
Babu wadda ta kula yar uwarta har Hamza ya fito. Kusa da Izzatu ya zauna. Ita Zuhra kasa ta zauna kan kafet saboda gudun kada ace tayi laifi. Gyara zamansa yayi fuskarsa ta nuna alamun ba wasa. Sannan ya soma magana
"Kamar yadda kuka sani dukkaninku matana ne duk da cewa circumstances behind auren kowacce is different......
Zuhra anzo wurin...gabadaya jumlar karshe bata fahimta ba.
.....bana son tashin hankali a gidan nan. Izzy kece babba ina so kija girmanki. Ke kuma ya juya ga Zuhra ki bata girmanta. Tun farko na gargadeki akan auren nan kika ki ji. So duk abinda kika gani sai kiyi hakuri. Sannan a yanzu baki da kitchen don sai an gyara miki daki a kasa. For now idan Izzy tayi girki zata baki. Saboda haka babu zancen rabon kwana sai an gama kitchen din." Ya kallesu duk su biyu. "Ko akwai mai magana?"
Izzatu tana ta kumbure kumbure tace " ka fada mata ta fita harkar yarana".
Bai ce mata komai ba yace da Zuhra tana iya tafiya. Tunda ya soma magana bata daga kai ba. Yayi tsammanin zata nuna bacin rai amma sai yaga tayi shiru. Kanta a kasa ta fita daga dakin ta koma nata. Tana rufe kofar ta suma kuka duk yadda taso daurewa ta kasa....ba son Hamza take ba amma babu macen da zata so a nuna mata ita ba komai bace a gaban kishiya.
[9/25, 3:50 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 31
Batul Mamman(Mrs)
Sai karfe uku da rabi Tala ta kwankwasa mata kofa. Ko da ta bude abinci ne a plate an rufe da wani sai ruwa roba daya mai sanyi da cup. Godiya tayi mata ta karba. Gara a rinka kawo mata don ita bata jin zata iya jurar zama tare da mutanen da basa kaunarta su ci abinci.
Dama tuni ta soma jin yunwa. Tana budewa taliya ce da miya sai coleslaw a gefe. Kare masa kallo tayi tana mamaki. Abin kuma harda rowar abinci? Abincin dan kukut a plate kamar zaa bawa Khalifa. Tas ta cinye ta sha ruwa rabin robar. In ba haka tayi ba tasan bazata koshi ba.
Hamza tun bayan azahar suka fita da wani abokinsa. Gidansu Zuhra suka je yi musu ban gajiya. Su Umma sunji dadi sosai. Har ta cire kunyarta ta tambayeshi ya Zuhra ta kwana. Murmushi yayi sannan yace mata lafiya kalau. Tana gaishe su. Da zasu tafi Baba ya bawa Hamza wayar Zuhra. A jakar Hajara ta manta ta daren jiya. Juya wayar ya rinka yi, banda tsufa ta dade da fita yayi.
Da daddare ma har daki aka biyota da abincin. Macaroni ce da vegetable soup. Sai dai Zuhra ta tsani macaroni. Duk yunwar da take ji dole ta hakura. Gudun kada aga kwadayinta ma ko naman dake cikin miyar bata ci ba ta dauki tray din ta sauka kasa dashi. Tana tafiya Hamza da Izzatu dake zaune a dinning table na binta da ido. Bata ko tanka musu ba ta wuce ta ajiye abincin a kitchen. Ta fito kenan Tala ta biyota da sauri.
"Naga baki ci abincin ba"
Dan murmushi tayi "na koshi ne".
Tana wucewa idonta ya kai kan nasu abincin. Shinkafa suke ci, wato ita suka hada da macaroni. Hamza na lura da irin kallon da take musu har ta wuce.
Wurin karfe goma da rabi Zuhra tana zaune tunani duk ya isheta gashi ta manta wayarta a gida. Ga uwa uba yunwa. Turo kofar taji anyi tayi saurin tashi zaune ta saka hijab. Daga ita sai daurin kirji saboda zafi ya dameta.
Kafin ta rufe jikinta ya kula da daurin kirjin. Ba karamin tsanar sa yayi ba. Bai tsaya jan zance da ita ba yace..
" kina jindadin cin abincin ke kadai ko zaki rinka ci tare damu?"
Tasan har ransa ba so yake taci dasu din ba." Zanci ni kadai"
"Fine, sai ki rinka fada da wuri idan bazaki ci ba saboda a dena wasting. An kawo miki kin mayar batare da kin taba ba".
Idan kika yi shiru zaki kwari kanki shine abinda zuciyarta ke raya mata. Ta dan rage murya "bana cin macaroni ne"
"Macaroni kuma? Mtsw ke bana son karya."
Turo baki tayi "ni ba karya nake ba. Abinda aka kawo min kenan."
Dafa kansa yayi yadda yake idan yana cikin damuwa." Me yasa bakiyi magana ba. Anyway nasan shinkafar bata kare ba idan kina so kije ki ci."
Tana kallo ya karaso cikin dakin ya kunna wani abu. Da yake tana setin AC din tuni ta fara jin iska. Yana gani tayi murmushi. Sannan tace.
"Don Allah ina ka kunna? Jiya zafi ya isheni na zata da sankarau zan tashi da safe"
Ta kusa sashi dariya sai ya gimtse. Idan ya sakar mata fuska zata yi tunanin ta sami karbuwa ne. Remote din AC din ya nuna mata sannan ya miko mata wayarta da chaja a cikin leda. Murna tayi sosai tayi masa godiya.
Sai da ya kama hannun kofar ta sake magana tana sosa keya.
"uhmmm"
Ya tsaya yana kallonta
"yes" ganin taki magana.
"Dama, dama famfon bandakin ne naga kamar sun lalace."
"Kin lalata su dai" ya fada yana shiga ciki. Ya duba duka komai lafiya kalau. Ya fito "wai ni abokin wasanki ne? Babu famfon da ya lalace"
Bata ce komai ba tayi saurin shiga. Hannu ta tara a famfon sink da baho duk ruwa ya fito da kansa. Sai da ya tsorata ta duk da ta gani jiya. " ka gani ko, yau tun sallar asuba da shaya nake yin alwala."
Wannan karon murmushi yayi. Sannan yayi mata bayanin yadda kan famfon yake. Tun kafin ya fita ta rinka bi tana tara hannu ruwa na zuba. Dariya take yi don abin ya burgeta. Yace to kada ki karar mana da ruwan gidan. Kunya taji tayi saurin cire hannunta ta fito. Shi kuwa tuni ya fice ya tafi nasa dakin.
[9/25, 3:51 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 32
Batul Mamman(Mrs)