Sashe 34
Al'adun Wasu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da ta shiga falon gani kawai tace ta dan durkusa a gefen kujera. Lallai ya tabo Cutie dole ya bata hakuri. Yi yayi kamar bai gane tana fushi ba yace tashi ki zubo mana abinci yunwa nake ji. Ni naci da su Hamida ta bashi amsa a takaice. Sai ya dan kashingida to shikenan ki barshi na fasa ci nima. Kallonsa tayi da mamaki a fuskarta ba yanzu kace kana jin yunwa ba. Ya kada kai tunda kinci ba tare da kin jirani ba shikenan, am not hungry anymore. Duk sai bata ji dadi ba. A hankali ta dan matsa kusa dashi, Ya Hamza nayi maka laifi ne? Yadda take maganar yasan kuka take shirin yi masa. Yace a'a naga kema kina ta bata rai shiyasa na dena jin yunwar. Sunkuyar da kanta tayi sai hawaye...hankalin Hamza ya tashi ya sauko kasan ya matso kusa da ita. Yanzu Cutie me nayi miki kike kuka....cikin kukan tace ba kaine kace sai na saka wannan kayan ba dazu, kuma da nayi fushi baka rarrasheni ka bani hakuri ba. Tasa hannu ta share hawayenta kuma shine yanzu kake fushi dani don Mala'iku su rubuta min zunubi. Zama yayi yana kallonta har ta gama bayanin sannan ya soma murmushi yi hakuri my cute baby ashe fushin duk laifina ne. Kiyi hakuri dazun ma wasa nake miki. A take ta washe baki kamar ba ita take kuka ba...da gaske ka yarda nasa rigar mutumci? Ya dafe kai wato wadancan ba na mutumci bane. To ki saka duk wanda kike so kinji. Yanzu dai bani abinci sai muyi shirin bacci. Tana tashi yayi ajiyar zuciya Zuhra akwai iya rigima. Ji yadda take masa kuka lokaci daya kuma ta dena kamar ba ita ba.
Bayan yaci abinci ta koma suka zauna kallo ita da su Adabiyya. Shiru shiru Hamza na jiranta a dakinsa taki hawowa har shadaya da rabi. Duk sai ya damu so yake kawai ya ganta. Gajiya yayi da jira ya sauko ya tashe su suje su kwanta dare yayi. Zuhra na ganin ya tafi tace akwai TV a dakina muje muga karshen film din. Adabiyya tace wane karshen film kuma ki tafi ki kwanta Anti Zuhra kada kisa Yaya ya kora mu gida da sassafe.
Suna shiga dakinta taga Hamida ta shiga wanka Adabiyya ta cire kaya ta daura tawul tana jiranta. A ranta Zuhra tace ashe kowa na wankan dare banda ni. 'Yan sauran kayan bukatarta ta dauka tayi musu sai da safe. Tana sallama falon nasa ta ganshi zaune ga laptop a gabansa ya zurfafa yana aiki, TV kuma a kunne ana news a BBC. Zama tayi a wata kujerar tace masa sannu da aiki. Hannu ya daga alamar amsawa ya cigaba da abinda yake yi. Remote ta dauka ta canja tashar zuwa film din da suke kallo kafin ya tashe su. Wurin minti shabiyar tana zaune, idonsa yana kan aikin gabansa yace Cutie tashi kije kiyi wanka. 'Yar shagwaba ta soma yi masa ka bari a gama don Allah. Dago kai yayi yana kallonta to babu komai bari na gama aikin gabana sai nayi miki. Bata jira ya kare zancen ba ta shige cikin dakinsa harda murda key. Girgiza kai yayi yana dariya. Tunda tare zasu kwana ai bashi da damuwa.
Sai da ta gama gyara jikinta tsaf ta tuna bata dauko wasu kayan baccin ba. Wadanda ya dauko ta gani akan gadon ta dauk tasa. Kayan sunyi mata kyau sosai ta saka hula sannan ta dauki hijab dinta mai hannu dogo har kasa ta dora a kai. A haka zata kwana a can gefen gadon idan yaki yarda ta koma falo. Tsoro take kada ya sake rungumarta irin na daren jiya ko ma yayi mata kiss irin yadda yayi da safe. Lips dinta ta dan shafa tana murmushi ashe kiss dinma ba kazanta bane. Ji tayi Ya Hamza ya kara shiga ranta sosai. Tunanin me kike yi haka harda murmushi Hamza ya fada yana rufe kofar dakin da mukulli. Hantar cikinta ce ta kada saboda tsoro murya a sarke tace bari na koma falo na kwana. Dan hararta yayi kina son muyi fada ne? Ta girgiza kai yace to sami wuri ki kwanta ni sallah zanyi. Kafin ya fito daga alwala ta shimfida abin sallah biyu a inda take tunanin nan ne gabas. Kallonta yayi tayi masa murmushi nima nayi alwala ai. Zuhra batasan komai tayi kara shiga ransa take yi ba. Dadi yaji mara misaltuwa da yaga ta tsaya akan abin sallah tana jira ya tayar. Da Izzy ce sai dai ta kwanta yayi ya idar da nafilarsa ko ta bijiro masa da bukatarta a lokacin. Sunyi kusan minti arbain da biyar suna sallah sannan ya idar yayi musu addua. Zuhra na ninke abin sallan tace Ya Hamza karatunka dadi wallahi. Yace nagode kinyi min addua kuwa? Yana kallo da hijab din ta kwanta tace sosai ma. Sai da ya kashe fitila suka kwanta kowa na nasa gefen Zuhra tace Ya Hamza ina son tambayarka amma kada kaji haushi na. Idan na bata maka rai kayi hakuri. In sha Allah raina bazai baci ba yi tambayarki. Sauke numfashi tayi da karfi...na kula tun satin da ya wuce wani lokacin sai ka zauna kayi ta tunani. Har ina tsoron ko duk saboda ni ne sai naga kuma kamar abin yafi karfin matsalar aurena da kayi ba'ason ranka ba. Idan bazaka iya fada min ba ma babu komai zan tayaka addua kullum. Amma kasan wani lokacin idan ka dan fadawa wani matsalarka sai kaji nauyinta ya ragu. Ko jibi idan su Khalifa suka dawo sai ka fadawa mamansu. Tunda ta fara magana yake kallon inda take kwance. Zuhra daban ce shine kawai abinda yake tunani. Har tana lura da damuwarsa duk yadda yake kokarin boyewa. Shiru yayi ya kasa magana saboda yadda ta tsaya masa a rai. A hankali ya fara yarda da cewa bazai iya rabuwa da Zuhra ba. Ji tayi yayi shiru tace Ya Hamza nayi maka laifi ko? Ka yafe min. Babana ne yace ana son mata da miji su rinka yiwa juna addua. Naga ko dai a yaya muka yi aure kai mijina ne yanzu shine nake son yi maka addua. Har yanzu bai yi magana ba sai ma haushin kansa da yake ji saboda yadda ya kuntata mata harda sa ranar saki. Hankalin Zuhra ya tashi da lalube take mika hannu saboda dakin yayi duhu sosai sai sautin AC, Ya Hamza kayi magana mana, Ya Ham....hannunta ne ya kai jikinsa ya janyota ya rungumeta sosai suka kwanta. Kanta akan kirjinsa da yake a bude bai balle maballan ba yaji saukar hawayenta. Saurin dagata yayi duk ta dukunkune jiki da hijab yace Cutie kukan me kike yi? Har da sheshsheka tace ba kaine kayi shiru ba na zata wani abu ne ya sameka. Hijab din jikinta yake kokarin cirewa tana rikewa a raunane yace Cutie kin damu dani ne haka. Da muryar shagwabarta tace kaifa Yayana ne yanzu wanda yake min kirki bana so muyi fada har mu rabu. Ta rike hijab din a jikinta don Allah kada ka cire min kunya nake ji. Kyaleta yayi ya rungumta a haka. A hankali ya bata labarin da babu wanda ya sani sai kalilan a kamfaninsa. Amma bai fada mata duk Izzatu ce take yin sanadiyar faruwarsu ba. Har mamakin kansa yake yadda ya iya budewa Zuhra kazamar yarinyar nan mara kunya cikinsa. Muryarta a kasa saboda labarinsa yasa ta kara yin kuka tace Ya Hamza ka godewa Allah da duk wata jarabawar rayuwa. Kaga ni bana sonka aka yi mana aure amma dana hakura na barwa Allah sai gashi ka zama mai kirki har ina sonka sosai a matsayinka na Yayana. Allah baya dorawa mumini abinda yafi karfinsa. Kuma yarda da qaddara yana karawa mutum imani da kusanci da Allah. Kada ka taba jin tsoron talauci Allah shine mai azurtawa. Zan rinka tayaka addua har Allah Ya kawo karshen komai. Hawaye ne suka cika masa ido ba na komai ba sai na karin imani da maganganun Zuhra suka saka masa. Abu daya ya kudurce a ransa zaiyi iya kokarinsa ya koya mata sonsa domin a halin yanzu baiga wanda ya isa ya rabashi da ita ba sai Allah. Idan abin nan da yake ji soyayya ce da bai taba tunanin zai yiwa wata ba bayan Izzatu to lallai ya amince har ransa yana son Zuhra. Ita kuwa duk da kunyar da take ji saboda yanayin kwanciyarsu ta hakura saboda yadda take jin tausayin Ya Hamza.
[10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: [10/2, 9:57 AM] +234 803 220 0468: AL'ADUN WASU 54
Batul Mamman(Mrs)
A hankali ta dan bude idonta sai taga haske a cikin dakin. Bude idanun tayi gabadaya ta kalli agogo. Karfe bakwai harda minti tara. Subhanallah ta fada tana kokarin tashi daga kan gadon. Rabin jikin Hamza duk ya danne mata hijab tayi kokarin janyewa ta kasa. Tana son taba shi ta tashe shi amma haka kawai take jin wata irin kunyarsa. Baccinsa yake hankali kwance. Karewa fuskarsa kallo tayi tana ayyana irin kamaninnsa da dukkan kannensa. Duk Alhaji Nasiru suka biyo shiyasa kana ganinsu kaga 'yan gida daya. Sajensa yafi komai daukar hankalinta kuma yana karawa fuskarsa kyau da kwarjini. Ga wani tausayinsa da yake ratsata saboda labarin da ya bata da daddare. Shagala tayi da kallon mijinta tana tunanin yadda zata ji ranar da zasu rabu. Idonsa a rufe yace irin wannan kallo Cutie sai na zata irin son nan kike yi min, in ba ni ba sai rijiya. Saurin tashi tayi zata gudu saboda kunyar da taji ya kamata tana kallonsa hijab dinta ya shake mata wuya. Tashi yayi yana mata sannu. Kinga maganin masu kwana da miji da hijab kenan. Kan Zuhra dai yana kasa ta kasa kallonsa ya tashi ya shige toilet yayi alwala. Bayan ya fito itama tayi suka yi sallar asuba tare da salatul duha tunda gari ya waye.
Bayan yaci abinci ta koma suka zauna kallo ita da su Adabiyya. Shiru shiru Hamza na jiranta a dakinsa taki hawowa har shadaya da rabi. Duk sai ya damu so yake kawai ya ganta. Gajiya yayi da jira ya sauko ya tashe su suje su kwanta dare yayi. Zuhra na ganin ya tafi tace akwai TV a dakina muje muga karshen film din. Adabiyya tace wane karshen film kuma ki tafi ki kwanta Anti Zuhra kada kisa Yaya ya kora mu gida da sassafe.
Suna shiga dakinta taga Hamida ta shiga wanka Adabiyya ta cire kaya ta daura tawul tana jiranta. A ranta Zuhra tace ashe kowa na wankan dare banda ni. 'Yan sauran kayan bukatarta ta dauka tayi musu sai da safe. Tana sallama falon nasa ta ganshi zaune ga laptop a gabansa ya zurfafa yana aiki, TV kuma a kunne ana news a BBC. Zama tayi a wata kujerar tace masa sannu da aiki. Hannu ya daga alamar amsawa ya cigaba da abinda yake yi. Remote ta dauka ta canja tashar zuwa film din da suke kallo kafin ya tashe su. Wurin minti shabiyar tana zaune, idonsa yana kan aikin gabansa yace Cutie tashi kije kiyi wanka. 'Yar shagwaba ta soma yi masa ka bari a gama don Allah. Dago kai yayi yana kallonta to babu komai bari na gama aikin gabana sai nayi miki. Bata jira ya kare zancen ba ta shige cikin dakinsa harda murda key. Girgiza kai yayi yana dariya. Tunda tare zasu kwana ai bashi da damuwa.
Sai da ta gama gyara jikinta tsaf ta tuna bata dauko wasu kayan baccin ba. Wadanda ya dauko ta gani akan gadon ta dauk tasa. Kayan sunyi mata kyau sosai ta saka hula sannan ta dauki hijab dinta mai hannu dogo har kasa ta dora a kai. A haka zata kwana a can gefen gadon idan yaki yarda ta koma falo. Tsoro take kada ya sake rungumarta irin na daren jiya ko ma yayi mata kiss irin yadda yayi da safe. Lips dinta ta dan shafa tana murmushi ashe kiss dinma ba kazanta bane. Ji tayi Ya Hamza ya kara shiga ranta sosai. Tunanin me kike yi haka harda murmushi Hamza ya fada yana rufe kofar dakin da mukulli. Hantar cikinta ce ta kada saboda tsoro murya a sarke tace bari na koma falo na kwana. Dan hararta yayi kina son muyi fada ne? Ta girgiza kai yace to sami wuri ki kwanta ni sallah zanyi. Kafin ya fito daga alwala ta shimfida abin sallah biyu a inda take tunanin nan ne gabas. Kallonta yayi tayi masa murmushi nima nayi alwala ai. Zuhra batasan komai tayi kara shiga ransa take yi ba. Dadi yaji mara misaltuwa da yaga ta tsaya akan abin sallah tana jira ya tayar. Da Izzy ce sai dai ta kwanta yayi ya idar da nafilarsa ko ta bijiro masa da bukatarta a lokacin. Sunyi kusan minti arbain da biyar suna sallah sannan ya idar yayi musu addua. Zuhra na ninke abin sallan tace Ya Hamza karatunka dadi wallahi. Yace nagode kinyi min addua kuwa? Yana kallo da hijab din ta kwanta tace sosai ma. Sai da ya kashe fitila suka kwanta kowa na nasa gefen Zuhra tace Ya Hamza ina son tambayarka amma kada kaji haushi na. Idan na bata maka rai kayi hakuri. In sha Allah raina bazai baci ba yi tambayarki. Sauke numfashi tayi da karfi...na kula tun satin da ya wuce wani lokacin sai ka zauna kayi ta tunani. Har ina tsoron ko duk saboda ni ne sai naga kuma kamar abin yafi karfin matsalar aurena da kayi ba'ason ranka ba. Idan bazaka iya fada min ba ma babu komai zan tayaka addua kullum. Amma kasan wani lokacin idan ka dan fadawa wani matsalarka sai kaji nauyinta ya ragu. Ko jibi idan su Khalifa suka dawo sai ka fadawa mamansu. Tunda ta fara magana yake kallon inda take kwance. Zuhra daban ce shine kawai abinda yake tunani. Har tana lura da damuwarsa duk yadda yake kokarin boyewa. Shiru yayi ya kasa magana saboda yadda ta tsaya masa a rai. A hankali ya fara yarda da cewa bazai iya rabuwa da Zuhra ba. Ji tayi yayi shiru tace Ya Hamza nayi maka laifi ko? Ka yafe min. Babana ne yace ana son mata da miji su rinka yiwa juna addua. Naga ko dai a yaya muka yi aure kai mijina ne yanzu shine nake son yi maka addua. Har yanzu bai yi magana ba sai ma haushin kansa da yake ji saboda yadda ya kuntata mata harda sa ranar saki. Hankalin Zuhra ya tashi da lalube take mika hannu saboda dakin yayi duhu sosai sai sautin AC, Ya Hamza kayi magana mana, Ya Ham....hannunta ne ya kai jikinsa ya janyota ya rungumeta sosai suka kwanta. Kanta akan kirjinsa da yake a bude bai balle maballan ba yaji saukar hawayenta. Saurin dagata yayi duk ta dukunkune jiki da hijab yace Cutie kukan me kike yi? Har da sheshsheka tace ba kaine kayi shiru ba na zata wani abu ne ya sameka. Hijab din jikinta yake kokarin cirewa tana rikewa a raunane yace Cutie kin damu dani ne haka. Da muryar shagwabarta tace kaifa Yayana ne yanzu wanda yake min kirki bana so muyi fada har mu rabu. Ta rike hijab din a jikinta don Allah kada ka cire min kunya nake ji. Kyaleta yayi ya rungumta a haka. A hankali ya bata labarin da babu wanda ya sani sai kalilan a kamfaninsa. Amma bai fada mata duk Izzatu ce take yin sanadiyar faruwarsu ba. Har mamakin kansa yake yadda ya iya budewa Zuhra kazamar yarinyar nan mara kunya cikinsa. Muryarta a kasa saboda labarinsa yasa ta kara yin kuka tace Ya Hamza ka godewa Allah da duk wata jarabawar rayuwa. Kaga ni bana sonka aka yi mana aure amma dana hakura na barwa Allah sai gashi ka zama mai kirki har ina sonka sosai a matsayinka na Yayana. Allah baya dorawa mumini abinda yafi karfinsa. Kuma yarda da qaddara yana karawa mutum imani da kusanci da Allah. Kada ka taba jin tsoron talauci Allah shine mai azurtawa. Zan rinka tayaka addua har Allah Ya kawo karshen komai. Hawaye ne suka cika masa ido ba na komai ba sai na karin imani da maganganun Zuhra suka saka masa. Abu daya ya kudurce a ransa zaiyi iya kokarinsa ya koya mata sonsa domin a halin yanzu baiga wanda ya isa ya rabashi da ita ba sai Allah. Idan abin nan da yake ji soyayya ce da bai taba tunanin zai yiwa wata ba bayan Izzatu to lallai ya amince har ransa yana son Zuhra. Ita kuwa duk da kunyar da take ji saboda yanayin kwanciyarsu ta hakura saboda yadda take jin tausayin Ya Hamza.
[10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: [10/2, 9:57 AM] +234 803 220 0468: AL'ADUN WASU 54
Batul Mamman(Mrs)
A hankali ta dan bude idonta sai taga haske a cikin dakin. Bude idanun tayi gabadaya ta kalli agogo. Karfe bakwai harda minti tara. Subhanallah ta fada tana kokarin tashi daga kan gadon. Rabin jikin Hamza duk ya danne mata hijab tayi kokarin janyewa ta kasa. Tana son taba shi ta tashe shi amma haka kawai take jin wata irin kunyarsa. Baccinsa yake hankali kwance. Karewa fuskarsa kallo tayi tana ayyana irin kamaninnsa da dukkan kannensa. Duk Alhaji Nasiru suka biyo shiyasa kana ganinsu kaga 'yan gida daya. Sajensa yafi komai daukar hankalinta kuma yana karawa fuskarsa kyau da kwarjini. Ga wani tausayinsa da yake ratsata saboda labarin da ya bata da daddare. Shagala tayi da kallon mijinta tana tunanin yadda zata ji ranar da zasu rabu. Idonsa a rufe yace irin wannan kallo Cutie sai na zata irin son nan kike yi min, in ba ni ba sai rijiya. Saurin tashi tayi zata gudu saboda kunyar da taji ya kamata tana kallonsa hijab dinta ya shake mata wuya. Tashi yayi yana mata sannu. Kinga maganin masu kwana da miji da hijab kenan. Kan Zuhra dai yana kasa ta kasa kallonsa ya tashi ya shige toilet yayi alwala. Bayan ya fito itama tayi suka yi sallar asuba tare da salatul duha tunda gari ya waye.