Sashe 57
Al'adun Wasu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk fitowa suka yi sojoji na tsayar dasu 'yan sandan suka taho suka fara yi musu bayanin report din da Ibrahim ya kai musu. Shaida suka nema domin gaskata zancen 'yan sandan. Nura ya duba wayarsa yayi sa'a akwai hoton ranar yinin Zuhra da suka je daukota daga Ajingi shine ya nuna musu. Duk da haka sai da suka bukaci washegari a kawo wani na'uin shaidar ko wacece Zuhra.
Alh Nasiru da kansa ya dauko hijab din da akayi wurgi dashi ya dora mata a kanta. Kasa tashi tayi ya dagata da kansa. Sai a lokacin ta kara sa kuka mai sauti. Ibrahim ya kalli sojojin yace mace mai hijab sunanta musulma ba 'yar ta'adda ba da zaku wulakanta ta haka.
A baya Alhaji ya zaunar da ita ya shiga gaba. Ibrahim ma binsu yayi a baya suka tafi gida.
Jugum jugum haka su Hajiya suka zauna a falo. Ana shigo da Zuhra Hajiya ta ajiye kunyarta taje ta rungumota. Zuhra ta kankameta tana kuka kamar mai ban tausayi. Cikin kuka tace Hajiya ai ba laifi bane idan ban yafewa Maman Khalifa ba ko? Kowa a wurin yaji tausayinta. Ga masu tayata kuka su Adabiyya suna yi.
Da kyar falon ya sami nutsuwa har ta fada musu abinda ya faru. Alhaji ya bata hakuri sannan yace ta kwantar da hankalinta zuwa gobe zasu san abin yi. Ruwa mai zafi Mama ta sa aka dafa mata tayi wanka amma taki cin komai. Dole suka kyaleta ta kwanta cike da tunani kala kala.
[10/22, 4:49 PM] +234 705 352 3457: AL'ADUN WASU 74
Batul Mamman(Mrs)
Gudu take yi a wani daji kafarta ko takalma babu ga gumi da ya wanke mata jiki. Sautin harbi take ji amma ta rasa daga ina yake fitowa. Tana cikin gudun ta hango wani gida a tsakiyar dajin ta tafi da sauri ta shiga ta rufe kofar harda saka kwado. Juyawar da zatayi idonta ya sauka akan sojoji da bata san iya adadinsu ba. Dariya suka fara yi mata kafin su saita ta da bindiga su fara harbi.
Hajiya tana idar da sallah ta juya gefen gado inda Zuhra ke kwance tana ta mutsu-mutsu duk ta hada gumi. Da sauri ta tashi ta tsaya a kanta ta fuskanci kowane irin mafarki take yi ba na lafiya bane. Kafadar Zuhra ta dafa da niyar tashinta Zuhran ta tashi a razane tare da kwalla kara. Ganin Hajiya yasa ta kankameta sai kuka ya kwace mata. Hajiyan tana rarrashinta tana kokarin mayar da hawayen da yake barazanar fitowa daga idonta. Tashin Zuhra na uku kenan tunda suka kwanta. Kamar ta sani ta hanata kwana dasu Hamida tace ta dawo dakinta. Sai da Zuhra tayi shiru sannan Hajiya tace...ki tashi kiyi sallah ba'a dade da kiran assalatu ba. Kuma ki yawaita addua nima zan cigaba da yi miki musamman na kwanciya saboda wannan mafarke mafarken da kike yi.
Jiki a mace Zuhra tace to Hajiya sannan ta tashi ta shiga toilet. Tun faruwar wannan al'amari 'yan awanni da suka wuce Zuhra da Hajiya suka manta da kunyar juna irin na surukai.
Bayan ta idar da sallah ne Mama ta shigo dakin da gani itama sallar tayi. Zuhra ta gaisheta ta amsa fuska a sake sannan ta tambayi Hajiya ya suka kwana...wallahi jiya Alhaji baiyi baccin kirki ba duk ya damu. Kusan a zaune muka kwana.
Hajiya tace to ai nima bamuyi baccin ba. Sau uku bacci na daukarta ta tashi a firgice. Allah Kaltume da sakin Izzatu a hannuna yake sai da yaron nan ya dawo ya tarar ta dade a gidansu.
Mama tayi murmushi, Hajiya Halima bata taba sanya kanta cikin lamuran 'ya'yanta musamman Hamza da ya kasance na fari. Wannan maganar tata ta kara tabbatar da cewa ba karamin bacin rai abinda Izzatu tayi ya sanyata ba. Haka suka zauna suna taba 'yar hira har gari ya karasa wayewa Mama ta tafi kitchen tare da Hamida wadda ita ce mai tayin abincin safe yau.
****
Dayake jirgin Emirate Hamza ya hau sun tsaya a Abu Dhabi canjin jirgin da hutun awa biyu. Wayar Zuhra ya rinka kira yanzu ko shiga ma bata yi. Hankalinsa yayi matukar tashi. Da ya kira Izzatu bayan sun gaisa lokacin karfe takwas na safe tace masa Zuhra bata fito daga daki ba. Hankalinsa gabadaya a tashe yake. Yace taje ta kwankwasa mata kofa tace yace ta kunna wayarta. Izzatu tace ita bazata je ba ta kashe wayarta ma a cewarta kada ya dameta ita babu ruwanta da matarsa. Haka ya hakura ya kira iyayensa suka amsa wayarsa kamar babu abinda ya faru. A hira ne ya sanar da Mama ya kasa samun Zuhra tun daren jiya bayan ya shiga jirgi. Mayar da zancen nasa wasa tayi har tana cewa ko zai biyata ne taje ta gano masa lafiyar amarya. Shi dai jikinsa duk babu dadi har ya sake shiga jirgin da zai kaisu Thailand wanda daga shi zasu shiga mai kaisu South Korea.
*****
Tunda Izzatu ta ajiye wayar Hamza jikinta yayi sanyi. Jiya dai lafiya kalau tayi bacci amma tunda ta fuskanci Zuhra bata dawo gida ba hankalinta ya kasa kwanciya. Ita fa a tata wautar ba niyarta wani mugun abin ya sami Zuhra ba. So tayi ta bata wahala karshe kila ta biyo motar haya a daren. Tunani tayi ko an saceta a hanya taji wani mugun tsoro ya shigeta. Sai yanzu take danasanin abinda tayi domin batan Zuhra ba karamin abu bane. Daga baya tayi tunanin ko gidansu Zuhran ta wuce sai tayi dariya. Karshen abin kenan kila ta koma gida ne tana son ta hadata da Hamza. Indai hakane kuwa ko a jikinta don tana da bakin kubutar da kanta. Tun daga wannan lokacin hankalinta ya kwanta.
Mama ce da kanta ta kira Tala wadda take ta hada kaya cikin kwanciyar hankali saboda Hamida ta tabbatar mata da anga Zuhra amma Alhaji yace kada ta kuskura ta fadawa kowa. Mama tace tasan yadda zatayi ta dauko wayar Zuhra a motar Hamza ta kawo mata gida. Wurin maigadi taje ta fada masa. Sai da rana ta fito yace Tala ta fada mata yace zai wanke mata motar yaga datti a ciki. Babu musu Izzatu ta leko ta tagar dakinta ta danna remote ta bude masa motar. Dama tana son zuwa shopping anjima.
Motar ya bude ya dauko wayar ya bawa Tala. Ita kuma bata dade ba tayi sallama da Izzatu ta dauki kayanta da sunan ta tafi kauye. Gidansu Hamza ta fara zuwa inda su Adabiyya suka labarta mata abinda ya sami Zuhra. Tala tayi kuka sosai sannan ta kawo wayar ta bawa Mama. Da aka kira Zuhra ta fito suka gaisa dukkansu sai da suka yi kuka. Tala tasan uwargidan nasu sai a hankali amma bata taba tsammanin abin nata yakai ta aikata wannan rashin imanin ba. Tayi musu sallama kuma su Hajiya suka kara mata guzuri ta tafi.
Wurin shabiyun rana Alhaji ya tara iyalinsa harda na gidan miji su Jidda da Mariya aka sake sanar dasu halin da ake ciki. A nan ya fada musu cewa bai yarda wata ta nuna tasan inda Zuhra take ba har Hamza ya dawo. Daga masu hawaye suna tausayin Zuhra sai masu zagin Izzatu da yi mata muguwar addua. Bayan sun tashi Alhaji ya wakilta Mama taje tasan da yadda zata yi ta daukowa Zuhra kayan sawa kafin ya dinka mata wasu. Bayan sun fita yace da Hajiya ta shirya ita da Zuhra zasu je unguwa.
Ibrahim ke jan motar har iya inda mota ke shiga a layin gidansu Zuhra. Yana tsayar da motar Zuhra ta fita da gudu ta shige gida.
Umma da Baba na zaune a falo suna jiran Safara'u ta gama girkin rana zasu je Ajingi barka maman Safara'un ta haihu.
Kamar an jehota Zuhra ta fada kan Baba tana kuka. Daga shi har Umma hankalinsu ya tashi suna tambayarta abinda ke faruwa ta kasa magana. Sallamar Hajiya ce ta katsesu Umma ta tashi ta tarota. Bayan sun gaisa ta fadawa Baba tare da Alhaji suke. Da kyar ya daga Zuhra daga jikinsa ya fita ya shigo dasu shi da Ibrahim.
Bayan sun zazzauna Hajiya ta kalli Zuhra da ta lafe jikin Umma, ita kuma Umman tana shafa mata baya tace...lallai Zuhra ke 'yar shagwaba ce ajin karshe. Umma taji kunya ta soma ture Zuhra. Baba yace dawo daga nan uwata nima ina da jikin da zaki tumurmusa. Kasa karasawa tayi ta sunkuyar da kanta saboda kunya. Ita ta manta ma da surukanta a wurin. Umma da Baba kuwa indai Zuhra zata yi kuka to basu da kwanciyar hankali.
Alh Nasiru yace nasan zakuyi mamakin zuwanmu a wannan lokacin kuma a irin wannan yanayin. Dole ce ta kawo haka domin bahaushe yace ranar wanka ba'a boyon cibi. Daga nan Alhaji ya warware musu gaskiyar lamari game da auren Hamza da Zuhra. Baba da Umma duk mamaki ya ishesu yadda Zuhra bata taba nuna musu ba auren soyayya tayi ba. Alhaji ya cigaba da cewa a yadda na fahimta Yaya da Zuhra suna son junansu yanzu duk da irin abinda ya faru kafin auren.
Baba ya rike hannun Zuhra yace kada ki cuci kanki kinfi karfin wulakanci muddin ina raye. Ki fada min gaskiya idan ba kya son auren sai a waraware. Kana ganin Baba kasan ba karamin bacin rai yaji ba game da labarin April fool da aka yiwa 'yarsa. Kanta a kasa Zuhra ta kasa magana sai kara rike hannun Baba da take yi. Hakan da tayi ya bashi tabbacin tana son mijinta. Da akasin haka ne kiri kiri zata masa da ido yadda tayi da ya taba cewa yaron shagonsa yana sonta. Ya dago kai ya kalli Alhaji...to yanzu menene yake faruwa kuka dawo da ita gida daga tafiyar Hamzan jiya?
Alh Nasiru da kansa ya dauko hijab din da akayi wurgi dashi ya dora mata a kanta. Kasa tashi tayi ya dagata da kansa. Sai a lokacin ta kara sa kuka mai sauti. Ibrahim ya kalli sojojin yace mace mai hijab sunanta musulma ba 'yar ta'adda ba da zaku wulakanta ta haka.
A baya Alhaji ya zaunar da ita ya shiga gaba. Ibrahim ma binsu yayi a baya suka tafi gida.
Jugum jugum haka su Hajiya suka zauna a falo. Ana shigo da Zuhra Hajiya ta ajiye kunyarta taje ta rungumota. Zuhra ta kankameta tana kuka kamar mai ban tausayi. Cikin kuka tace Hajiya ai ba laifi bane idan ban yafewa Maman Khalifa ba ko? Kowa a wurin yaji tausayinta. Ga masu tayata kuka su Adabiyya suna yi.
Da kyar falon ya sami nutsuwa har ta fada musu abinda ya faru. Alhaji ya bata hakuri sannan yace ta kwantar da hankalinta zuwa gobe zasu san abin yi. Ruwa mai zafi Mama ta sa aka dafa mata tayi wanka amma taki cin komai. Dole suka kyaleta ta kwanta cike da tunani kala kala.
[10/22, 4:49 PM] +234 705 352 3457: AL'ADUN WASU 74
Batul Mamman(Mrs)
Gudu take yi a wani daji kafarta ko takalma babu ga gumi da ya wanke mata jiki. Sautin harbi take ji amma ta rasa daga ina yake fitowa. Tana cikin gudun ta hango wani gida a tsakiyar dajin ta tafi da sauri ta shiga ta rufe kofar harda saka kwado. Juyawar da zatayi idonta ya sauka akan sojoji da bata san iya adadinsu ba. Dariya suka fara yi mata kafin su saita ta da bindiga su fara harbi.
Hajiya tana idar da sallah ta juya gefen gado inda Zuhra ke kwance tana ta mutsu-mutsu duk ta hada gumi. Da sauri ta tashi ta tsaya a kanta ta fuskanci kowane irin mafarki take yi ba na lafiya bane. Kafadar Zuhra ta dafa da niyar tashinta Zuhran ta tashi a razane tare da kwalla kara. Ganin Hajiya yasa ta kankameta sai kuka ya kwace mata. Hajiyan tana rarrashinta tana kokarin mayar da hawayen da yake barazanar fitowa daga idonta. Tashin Zuhra na uku kenan tunda suka kwanta. Kamar ta sani ta hanata kwana dasu Hamida tace ta dawo dakinta. Sai da Zuhra tayi shiru sannan Hajiya tace...ki tashi kiyi sallah ba'a dade da kiran assalatu ba. Kuma ki yawaita addua nima zan cigaba da yi miki musamman na kwanciya saboda wannan mafarke mafarken da kike yi.
Jiki a mace Zuhra tace to Hajiya sannan ta tashi ta shiga toilet. Tun faruwar wannan al'amari 'yan awanni da suka wuce Zuhra da Hajiya suka manta da kunyar juna irin na surukai.
Bayan ta idar da sallah ne Mama ta shigo dakin da gani itama sallar tayi. Zuhra ta gaisheta ta amsa fuska a sake sannan ta tambayi Hajiya ya suka kwana...wallahi jiya Alhaji baiyi baccin kirki ba duk ya damu. Kusan a zaune muka kwana.
Hajiya tace to ai nima bamuyi baccin ba. Sau uku bacci na daukarta ta tashi a firgice. Allah Kaltume da sakin Izzatu a hannuna yake sai da yaron nan ya dawo ya tarar ta dade a gidansu.
Mama tayi murmushi, Hajiya Halima bata taba sanya kanta cikin lamuran 'ya'yanta musamman Hamza da ya kasance na fari. Wannan maganar tata ta kara tabbatar da cewa ba karamin bacin rai abinda Izzatu tayi ya sanyata ba. Haka suka zauna suna taba 'yar hira har gari ya karasa wayewa Mama ta tafi kitchen tare da Hamida wadda ita ce mai tayin abincin safe yau.
****
Dayake jirgin Emirate Hamza ya hau sun tsaya a Abu Dhabi canjin jirgin da hutun awa biyu. Wayar Zuhra ya rinka kira yanzu ko shiga ma bata yi. Hankalinsa yayi matukar tashi. Da ya kira Izzatu bayan sun gaisa lokacin karfe takwas na safe tace masa Zuhra bata fito daga daki ba. Hankalinsa gabadaya a tashe yake. Yace taje ta kwankwasa mata kofa tace yace ta kunna wayarta. Izzatu tace ita bazata je ba ta kashe wayarta ma a cewarta kada ya dameta ita babu ruwanta da matarsa. Haka ya hakura ya kira iyayensa suka amsa wayarsa kamar babu abinda ya faru. A hira ne ya sanar da Mama ya kasa samun Zuhra tun daren jiya bayan ya shiga jirgi. Mayar da zancen nasa wasa tayi har tana cewa ko zai biyata ne taje ta gano masa lafiyar amarya. Shi dai jikinsa duk babu dadi har ya sake shiga jirgin da zai kaisu Thailand wanda daga shi zasu shiga mai kaisu South Korea.
*****
Tunda Izzatu ta ajiye wayar Hamza jikinta yayi sanyi. Jiya dai lafiya kalau tayi bacci amma tunda ta fuskanci Zuhra bata dawo gida ba hankalinta ya kasa kwanciya. Ita fa a tata wautar ba niyarta wani mugun abin ya sami Zuhra ba. So tayi ta bata wahala karshe kila ta biyo motar haya a daren. Tunani tayi ko an saceta a hanya taji wani mugun tsoro ya shigeta. Sai yanzu take danasanin abinda tayi domin batan Zuhra ba karamin abu bane. Daga baya tayi tunanin ko gidansu Zuhran ta wuce sai tayi dariya. Karshen abin kenan kila ta koma gida ne tana son ta hadata da Hamza. Indai hakane kuwa ko a jikinta don tana da bakin kubutar da kanta. Tun daga wannan lokacin hankalinta ya kwanta.
Mama ce da kanta ta kira Tala wadda take ta hada kaya cikin kwanciyar hankali saboda Hamida ta tabbatar mata da anga Zuhra amma Alhaji yace kada ta kuskura ta fadawa kowa. Mama tace tasan yadda zatayi ta dauko wayar Zuhra a motar Hamza ta kawo mata gida. Wurin maigadi taje ta fada masa. Sai da rana ta fito yace Tala ta fada mata yace zai wanke mata motar yaga datti a ciki. Babu musu Izzatu ta leko ta tagar dakinta ta danna remote ta bude masa motar. Dama tana son zuwa shopping anjima.
Motar ya bude ya dauko wayar ya bawa Tala. Ita kuma bata dade ba tayi sallama da Izzatu ta dauki kayanta da sunan ta tafi kauye. Gidansu Hamza ta fara zuwa inda su Adabiyya suka labarta mata abinda ya sami Zuhra. Tala tayi kuka sosai sannan ta kawo wayar ta bawa Mama. Da aka kira Zuhra ta fito suka gaisa dukkansu sai da suka yi kuka. Tala tasan uwargidan nasu sai a hankali amma bata taba tsammanin abin nata yakai ta aikata wannan rashin imanin ba. Tayi musu sallama kuma su Hajiya suka kara mata guzuri ta tafi.
Wurin shabiyun rana Alhaji ya tara iyalinsa harda na gidan miji su Jidda da Mariya aka sake sanar dasu halin da ake ciki. A nan ya fada musu cewa bai yarda wata ta nuna tasan inda Zuhra take ba har Hamza ya dawo. Daga masu hawaye suna tausayin Zuhra sai masu zagin Izzatu da yi mata muguwar addua. Bayan sun tashi Alhaji ya wakilta Mama taje tasan da yadda zata yi ta daukowa Zuhra kayan sawa kafin ya dinka mata wasu. Bayan sun fita yace da Hajiya ta shirya ita da Zuhra zasu je unguwa.
Ibrahim ke jan motar har iya inda mota ke shiga a layin gidansu Zuhra. Yana tsayar da motar Zuhra ta fita da gudu ta shige gida.
Umma da Baba na zaune a falo suna jiran Safara'u ta gama girkin rana zasu je Ajingi barka maman Safara'un ta haihu.
Kamar an jehota Zuhra ta fada kan Baba tana kuka. Daga shi har Umma hankalinsu ya tashi suna tambayarta abinda ke faruwa ta kasa magana. Sallamar Hajiya ce ta katsesu Umma ta tashi ta tarota. Bayan sun gaisa ta fadawa Baba tare da Alhaji suke. Da kyar ya daga Zuhra daga jikinsa ya fita ya shigo dasu shi da Ibrahim.
Bayan sun zazzauna Hajiya ta kalli Zuhra da ta lafe jikin Umma, ita kuma Umman tana shafa mata baya tace...lallai Zuhra ke 'yar shagwaba ce ajin karshe. Umma taji kunya ta soma ture Zuhra. Baba yace dawo daga nan uwata nima ina da jikin da zaki tumurmusa. Kasa karasawa tayi ta sunkuyar da kanta saboda kunya. Ita ta manta ma da surukanta a wurin. Umma da Baba kuwa indai Zuhra zata yi kuka to basu da kwanciyar hankali.
Alh Nasiru yace nasan zakuyi mamakin zuwanmu a wannan lokacin kuma a irin wannan yanayin. Dole ce ta kawo haka domin bahaushe yace ranar wanka ba'a boyon cibi. Daga nan Alhaji ya warware musu gaskiyar lamari game da auren Hamza da Zuhra. Baba da Umma duk mamaki ya ishesu yadda Zuhra bata taba nuna musu ba auren soyayya tayi ba. Alhaji ya cigaba da cewa a yadda na fahimta Yaya da Zuhra suna son junansu yanzu duk da irin abinda ya faru kafin auren.
Baba ya rike hannun Zuhra yace kada ki cuci kanki kinfi karfin wulakanci muddin ina raye. Ki fada min gaskiya idan ba kya son auren sai a waraware. Kana ganin Baba kasan ba karamin bacin rai yaji ba game da labarin April fool da aka yiwa 'yarsa. Kanta a kasa Zuhra ta kasa magana sai kara rike hannun Baba da take yi. Hakan da tayi ya bashi tabbacin tana son mijinta. Da akasin haka ne kiri kiri zata masa da ido yadda tayi da ya taba cewa yaron shagonsa yana sonta. Ya dago kai ya kalli Alhaji...to yanzu menene yake faruwa kuka dawo da ita gida daga tafiyar Hamzan jiya?