Sashe 54
Al'adun Wasu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Girgiza kai yayi yana mamakin yadda take daga masa murya. Ban fada miki ba saboda gudun kada kizo ki tayar min da rigima kice sai kinje. Amma naga alama hakan ya zama kuskure. Ki zauna a gida ki karasa jinyar jikinki lafin mu dawo. Kuma bana son cigaba da maganar nan don banyi niya ba saboda haka idan wata tafiyarar tazo sai nayi dake idan naga dama.
Ficewa tayi daga dakin ta tafi dakin Zuhra rai a bace ta buga kofar da karfi tana masifa....Zuhra ki kiyayeni wallahi. Ki bar ganin na kyaleki lokaci na baki kafin na koreki daga gidan nan.
Hamza da yake bayanta yace tunda ki kike auranta ba. To kema ki kiyayeni wallahi ko gobe mu tafi airport tare ki koma gidanku. Kada ki kaini bango Izzy darajar 'ya'ya kawai kike ci kema kuma kin sani.
Zuhra dai kallonsu take daya bayan daya ta kasa magana. Tana kallo Hamza yaja hannun Izzatu suka fita. Ranar basuyi baccin arziki ba saboda yadda take ta fada. Sai da Hamza yace idan ta saki bude baki a bakin igiyar aurenta. Cikin masifa tace guda nawa? Yace sai kinyi maganar zan sanar dake ko nawa kika tsinke. Ba arziki ta yi shiru amma ta gama sikewa da Zuhra. Dole tasan yadda zata yi da ita kafin tayi sanadiyar kashe mata aure.
Tun bayan asuba Zuhra tayi wanka ta gama shiri saboda Hamza ya fada mata jirginsu karfe bakwai zai tashi.
Shima da wuri ya shirya ya shiga dakinta. Sai kai kawo take yi a tsakar daki. Tana ganinshi ta gaishe shi yace wannan tafiyar ta meye? Kinci abinci kuwa? Zuhra tace wane irin abinci Ya Hamza? Cikina sai kullewa yake saboda fargaba. Anya zan iya shiga jirgin kuwa. Yayi dariya idan bazaki iya ba sai na tafi da yayarki.
Jin haka Zuhra ta fita daga dakin da sauri har tana tuntube. Shi ya dauko mata akwatin kayanta yabi bayanta.
Da kyar ya samu tasha tea duk hankalinta baya jikinta. A tsorace kawai take da maganar shiga jirgi. Basu dade ba Nura yazo daukarsu shi zai kai su airport din. Har suka fita Izzatu ko kofar daki bata fito ba.
Ana shiga airport Zuhra na kara razana. Gabadaya a tsorace take. Hamza kuwa sai dariya yace yau ga 'yar kauye ga jirgi. Kamar tayi kuka tace Ya Hamza ko dai mu tafi tasha ne mu sami mota. Ya kama hannunta ya rike....Cutie kada ki damu babu inda zanje in barki kinji ko. A hankali ta gyada kai.
Cikin dan lokaci ya karbar mata ticket suka fita inda jirgin yake. Layi suka bi tare da wasu masu tafiyar. Zuhra sai kallo wai ita ce yau zata shiga jirgin sama. Ga wasu manyan jiragen da suka fi wanda zasu shiga ma. Tana rike da hannun Hamza tace kuma yanzu a iska dreban jirgin yake gane hanya ko akwai alama da ake sakawa yadda bazasu bata ba? Yace wurin tukin nasu ne yake aiki da na'ura mai kwakwalwa tana nuna musu hanya sannan daga can airport dinma ana yi musu bayani... Suna shiga ciki har suka zauna ya daura mata seat belt yana mata bayanin yadda jirgi ke tafiya a sama. Kusa da taga ya zaunar da ita shi kuma yana gefe. Sai da ya gama bayaninsa tace ni dai duk bangane ba. Hamza ya ja mata kunne,amma shine kika barni ina ta surutu ko?
A hankali jirgin ya fara tafiya a kasa cikin Zuhra ya murda don tsoro ta kankame Hamza. Ihu taso yi lokacin da ya fara tashi har ta bude baki yayi saurin rufe shi da nasa. Bai kyaleta ba sai da yaji sun daidaita a sama.
Da sauri da sauri take fitar da numfashi ta dan bata fuska Ya Hamza muna cikin wannan yanayin wa yake ta soyayya? Sai da ya ja hancinta sannan yace ai magana ta kare tunda soyayyar ta hana ki cikawa mutane kunne da ihu. Harda wani kara lafewa a jikina,kai wannan yarinya kin zama abinda kika zama. Kunya taji da kawar da kanta tana kallon waje.
Daga nan hirar ta koma ta abubuwan da take gani. Suna haka aka kawo abinci. Zuhra tace kaji fitina har mutum yana da nutsuwar cin abinci a nan. Hamza yayi dariya yau yaga shirme wurin Cutie kala kala. Har dan bacci tayi wanda ta farka lokacin da jirgin ya fara sauka kasa.
Taxi suka samu zuwa hotel din da aka ce suje ana ya hadu da wasu mutum biyu da suma basu dade da zuwa ba suka gaisa. Mukullan dakunansu aka basu sannan mutumin da aka turo wurinsu ya sanar dasu karfe goma mota zata zo daukarsu saboda a yau zasu fara abinda ya kawosu.
Sai da Hamza ya tabbatar Zuhra ta sami nutsuwa sannan yayi wanka ya shirya. Kashedi yayi mata kada ta bude kofar sai karfe daya lokacin da yayi magana da receptionist za'a kawo mata abincin rana. Kamar kada su rabu lokacin da zai fita. Tayi ta masa addua sannan suka yi sallama.
Hajiya Izzatu har karfe uku bata fito daga daki ba. Tala ce tayi komai. Wayar kawarta wata baturiya Laura ta kira ta sanar da ita halin kuncin da Hamza ya sakata a ciki.
. AL'ADUN WASU 72
Batul Mamman(Mrs)
Laura ta gama jin korafin Izzatu tayi tsaki tace....
Duk laifinku ne 'yan Nigeria. Kuna bawa iyayenku mahimmanci fiye da yadda ya kamata. Na tabbata duk abinda mijinki yake miki yanzu don ya faranta musu ne.
Izzatu tace hakane amma kinsan mu addininmu da al'ada duk basu yarda da rashin biyayya ga iyaye ba.
To ai kuwa bazaki dena ganin bacin rai ba Izzy...Laura ta fada tana kara jin haushin al'ada irin ta hausawa....idan baki manta ba sai da nace kada ki yarda kuyi aure. Ku zauna tare ku haihu kamar yadda nayi. Duk lokacin da kika gaji dashi ki tattara ki bar masa gidan amma kika ki. Shawara daya zan baki shine kice ya zaba ko ke ko iyayensa da wannan matar da ya auro. Ni kinga mahaifiyata ce bata son Phil kinga tuni na yakiceta. Sai karshen shekara muke haduwa a wurin anniversary din mutuwar babana.
Izzatu tayi kasake tana jin gurguwar shawarar Laura. A ranta tace duk ranar da ta bawa Hamza wannan zabin to ko minti biyar tasan bazata kara a gidan ba. Su turawa basu san al'adunmu akwai bambanci ba. A gurguje tayi sallama da Laura domin ta fuskanci shawararta tamkar ta kama kafar wala ne. Dole ta sake sabuwar shawara amma zaman Zuhra a gidan nan bazarana yake ga igiyar aurenta.
******
Kullum karfe goma Hamza yake fita sai takwas na dare yake dawowa. Kafin ya dawo Zuhra zata wuni bacci amma yana dawowa to fa sai a bude soyayya. Zamansu suke lafiya cike da kwanciyar hankali. Basu da wata damuwa sai ta junansu. Kullum dai zai kira Izzatu kuma zai gaisa da 'ya'yansa. Rashin lokaci yasa bai sami damar kai Zuhra ko'ina ba. Amma ita kasancewarsu tare ya isheta shiyasa bata damunsa da su fita.
Ranar da zasuyi jarabawa Zuhra tayi ta masa addua. Karfe uku ya dawo ranar ya dauketa suka sami taxi suka fita gari. Shine har bakin ruwa(beach)ya kaita. Suka dan zagaya kasuwa ya siyawa Zuhra kananan kaya masu kyau don yaga bata dasu sosai. Wata rigar idan ya dauko sai taji kunya.
Asabar da lahadi ma duk yawo ya kaita sai ranar litinin suka biyo jirgin safe suka koma Kano. Wannan karon kauyancin Zuhra ya ragu. Nura ne ya sake zuwa daukarsu amma sai da ya biya gida ya gaisa da iyayensa sannan suka wuce nasu gidan.
Tun asuba Izzatu tasa Tala guaran gida ita kuma aka shige kitchen girkin tarar maigida. Tana jin tsayuwar mota tun daga bakin kofa ta taresu ta kankame Hamza tana murna. Kiss take zuba masa ko ta ina a fuska ga Nura a bayansa dauke da jaka sai kawar da kai yake sannan ga Zuhra da ta hade rai. Izzatu tayi dariyar keta, ko babu komai tasan Zuhra bazata iya yin abinda tayi ba. Shi kanshi Hamzan yanzu sai da yaji kunya sabanin da da suke abinsu hankali kwance.
Ko zama baiyi ba taja hannunsa suka tafi daki tana fada masa yadda tayi missing dinsa. Zancen yaya aikin da ya kaishi kuwa ko a waya bata yi. Bata da zance sai na korafin ya tafi ya barta.
Haka rayuwa ta kasance musu kowacce ranar girkinta tana kokarin farantawa mijinta rai. Kwanansu biyar da dawowa Hamza ya sami sako cewa yayi na uku a jarabawarsu ana bukatar ya kai passport dinsa Abuja ofishin minister domin neman visa. Da farincikinsa ya sanar da Izzatu saboda ranar girkinta ne. Tana jin haka ta tashi ta nufi dakinta.
Hamza ya bi bayanta da sauri don ya zata wani abin ne ya faru...Izzy saurin me kike yi haka ko gama sauraron abinda nace bakiyi ba?
Wardrobe ta bude ta janyo wata jaka sannan ta fuskance shi...naji abinda kace mana. Sai dai Sweety nasan ba abin mamaki bane idan kayi nasara saboda I believe in you my darling. Kayana zan hada na tafiyarmu Abujan....ta daga jakar sama, kana ganin wannan zata isa ko tayi kankanta?
Rasa bakin magana yayi sai binta yake da ido kamar lokacin ya fara ganinta. Babu godewa Allah, babu taya shi murna sai jaka da ta dauko zata hada kaya bayan shi kanshi bai sami cikakken bayani game da tafiyar ba. A kalla jakar zata dauki kaya bakwai zuwa goma idan an cusa su sosai. Ko ya fada mata a Abuja zasu yi course din ne bai sani ba. Haka ya fita ya barta ba tare da ya bata amsa ba ya tafi dakin Zuhra.
Kulu ne tumuli guda a gabanta tana warewa saboda ya samar mata wata makarantar sun bada kwangilar sakar rigunan sanyin makaranta.
Da murmushi ta tarbe shi tace Ya Hamza ba na hanaka satar kwana ba? Shima murmushin yayi ai kece satar kwanan. Ace mutum bashi da ikon ganin matarsa sai ranar girkinta.
Kusa da ita yaje ya zauna ya kama hannunta ya rike.
Cutie albishirinki? Idonta a kan fuskarsa tace goro Ya Hamzana.
Me zaki bani idan na fada miki?
Duk abinda kake so indai baifi karfina ba.
Ficewa tayi daga dakin ta tafi dakin Zuhra rai a bace ta buga kofar da karfi tana masifa....Zuhra ki kiyayeni wallahi. Ki bar ganin na kyaleki lokaci na baki kafin na koreki daga gidan nan.
Hamza da yake bayanta yace tunda ki kike auranta ba. To kema ki kiyayeni wallahi ko gobe mu tafi airport tare ki koma gidanku. Kada ki kaini bango Izzy darajar 'ya'ya kawai kike ci kema kuma kin sani.
Zuhra dai kallonsu take daya bayan daya ta kasa magana. Tana kallo Hamza yaja hannun Izzatu suka fita. Ranar basuyi baccin arziki ba saboda yadda take ta fada. Sai da Hamza yace idan ta saki bude baki a bakin igiyar aurenta. Cikin masifa tace guda nawa? Yace sai kinyi maganar zan sanar dake ko nawa kika tsinke. Ba arziki ta yi shiru amma ta gama sikewa da Zuhra. Dole tasan yadda zata yi da ita kafin tayi sanadiyar kashe mata aure.
Tun bayan asuba Zuhra tayi wanka ta gama shiri saboda Hamza ya fada mata jirginsu karfe bakwai zai tashi.
Shima da wuri ya shirya ya shiga dakinta. Sai kai kawo take yi a tsakar daki. Tana ganinshi ta gaishe shi yace wannan tafiyar ta meye? Kinci abinci kuwa? Zuhra tace wane irin abinci Ya Hamza? Cikina sai kullewa yake saboda fargaba. Anya zan iya shiga jirgin kuwa. Yayi dariya idan bazaki iya ba sai na tafi da yayarki.
Jin haka Zuhra ta fita daga dakin da sauri har tana tuntube. Shi ya dauko mata akwatin kayanta yabi bayanta.
Da kyar ya samu tasha tea duk hankalinta baya jikinta. A tsorace kawai take da maganar shiga jirgi. Basu dade ba Nura yazo daukarsu shi zai kai su airport din. Har suka fita Izzatu ko kofar daki bata fito ba.
Ana shiga airport Zuhra na kara razana. Gabadaya a tsorace take. Hamza kuwa sai dariya yace yau ga 'yar kauye ga jirgi. Kamar tayi kuka tace Ya Hamza ko dai mu tafi tasha ne mu sami mota. Ya kama hannunta ya rike....Cutie kada ki damu babu inda zanje in barki kinji ko. A hankali ta gyada kai.
Cikin dan lokaci ya karbar mata ticket suka fita inda jirgin yake. Layi suka bi tare da wasu masu tafiyar. Zuhra sai kallo wai ita ce yau zata shiga jirgin sama. Ga wasu manyan jiragen da suka fi wanda zasu shiga ma. Tana rike da hannun Hamza tace kuma yanzu a iska dreban jirgin yake gane hanya ko akwai alama da ake sakawa yadda bazasu bata ba? Yace wurin tukin nasu ne yake aiki da na'ura mai kwakwalwa tana nuna musu hanya sannan daga can airport dinma ana yi musu bayani... Suna shiga ciki har suka zauna ya daura mata seat belt yana mata bayanin yadda jirgi ke tafiya a sama. Kusa da taga ya zaunar da ita shi kuma yana gefe. Sai da ya gama bayaninsa tace ni dai duk bangane ba. Hamza ya ja mata kunne,amma shine kika barni ina ta surutu ko?
A hankali jirgin ya fara tafiya a kasa cikin Zuhra ya murda don tsoro ta kankame Hamza. Ihu taso yi lokacin da ya fara tashi har ta bude baki yayi saurin rufe shi da nasa. Bai kyaleta ba sai da yaji sun daidaita a sama.
Da sauri da sauri take fitar da numfashi ta dan bata fuska Ya Hamza muna cikin wannan yanayin wa yake ta soyayya? Sai da ya ja hancinta sannan yace ai magana ta kare tunda soyayyar ta hana ki cikawa mutane kunne da ihu. Harda wani kara lafewa a jikina,kai wannan yarinya kin zama abinda kika zama. Kunya taji da kawar da kanta tana kallon waje.
Daga nan hirar ta koma ta abubuwan da take gani. Suna haka aka kawo abinci. Zuhra tace kaji fitina har mutum yana da nutsuwar cin abinci a nan. Hamza yayi dariya yau yaga shirme wurin Cutie kala kala. Har dan bacci tayi wanda ta farka lokacin da jirgin ya fara sauka kasa.
Taxi suka samu zuwa hotel din da aka ce suje ana ya hadu da wasu mutum biyu da suma basu dade da zuwa ba suka gaisa. Mukullan dakunansu aka basu sannan mutumin da aka turo wurinsu ya sanar dasu karfe goma mota zata zo daukarsu saboda a yau zasu fara abinda ya kawosu.
Sai da Hamza ya tabbatar Zuhra ta sami nutsuwa sannan yayi wanka ya shirya. Kashedi yayi mata kada ta bude kofar sai karfe daya lokacin da yayi magana da receptionist za'a kawo mata abincin rana. Kamar kada su rabu lokacin da zai fita. Tayi ta masa addua sannan suka yi sallama.
Hajiya Izzatu har karfe uku bata fito daga daki ba. Tala ce tayi komai. Wayar kawarta wata baturiya Laura ta kira ta sanar da ita halin kuncin da Hamza ya sakata a ciki.
. AL'ADUN WASU 72
Batul Mamman(Mrs)
Laura ta gama jin korafin Izzatu tayi tsaki tace....
Duk laifinku ne 'yan Nigeria. Kuna bawa iyayenku mahimmanci fiye da yadda ya kamata. Na tabbata duk abinda mijinki yake miki yanzu don ya faranta musu ne.
Izzatu tace hakane amma kinsan mu addininmu da al'ada duk basu yarda da rashin biyayya ga iyaye ba.
To ai kuwa bazaki dena ganin bacin rai ba Izzy...Laura ta fada tana kara jin haushin al'ada irin ta hausawa....idan baki manta ba sai da nace kada ki yarda kuyi aure. Ku zauna tare ku haihu kamar yadda nayi. Duk lokacin da kika gaji dashi ki tattara ki bar masa gidan amma kika ki. Shawara daya zan baki shine kice ya zaba ko ke ko iyayensa da wannan matar da ya auro. Ni kinga mahaifiyata ce bata son Phil kinga tuni na yakiceta. Sai karshen shekara muke haduwa a wurin anniversary din mutuwar babana.
Izzatu tayi kasake tana jin gurguwar shawarar Laura. A ranta tace duk ranar da ta bawa Hamza wannan zabin to ko minti biyar tasan bazata kara a gidan ba. Su turawa basu san al'adunmu akwai bambanci ba. A gurguje tayi sallama da Laura domin ta fuskanci shawararta tamkar ta kama kafar wala ne. Dole ta sake sabuwar shawara amma zaman Zuhra a gidan nan bazarana yake ga igiyar aurenta.
******
Kullum karfe goma Hamza yake fita sai takwas na dare yake dawowa. Kafin ya dawo Zuhra zata wuni bacci amma yana dawowa to fa sai a bude soyayya. Zamansu suke lafiya cike da kwanciyar hankali. Basu da wata damuwa sai ta junansu. Kullum dai zai kira Izzatu kuma zai gaisa da 'ya'yansa. Rashin lokaci yasa bai sami damar kai Zuhra ko'ina ba. Amma ita kasancewarsu tare ya isheta shiyasa bata damunsa da su fita.
Ranar da zasuyi jarabawa Zuhra tayi ta masa addua. Karfe uku ya dawo ranar ya dauketa suka sami taxi suka fita gari. Shine har bakin ruwa(beach)ya kaita. Suka dan zagaya kasuwa ya siyawa Zuhra kananan kaya masu kyau don yaga bata dasu sosai. Wata rigar idan ya dauko sai taji kunya.
Asabar da lahadi ma duk yawo ya kaita sai ranar litinin suka biyo jirgin safe suka koma Kano. Wannan karon kauyancin Zuhra ya ragu. Nura ne ya sake zuwa daukarsu amma sai da ya biya gida ya gaisa da iyayensa sannan suka wuce nasu gidan.
Tun asuba Izzatu tasa Tala guaran gida ita kuma aka shige kitchen girkin tarar maigida. Tana jin tsayuwar mota tun daga bakin kofa ta taresu ta kankame Hamza tana murna. Kiss take zuba masa ko ta ina a fuska ga Nura a bayansa dauke da jaka sai kawar da kai yake sannan ga Zuhra da ta hade rai. Izzatu tayi dariyar keta, ko babu komai tasan Zuhra bazata iya yin abinda tayi ba. Shi kanshi Hamzan yanzu sai da yaji kunya sabanin da da suke abinsu hankali kwance.
Ko zama baiyi ba taja hannunsa suka tafi daki tana fada masa yadda tayi missing dinsa. Zancen yaya aikin da ya kaishi kuwa ko a waya bata yi. Bata da zance sai na korafin ya tafi ya barta.
Haka rayuwa ta kasance musu kowacce ranar girkinta tana kokarin farantawa mijinta rai. Kwanansu biyar da dawowa Hamza ya sami sako cewa yayi na uku a jarabawarsu ana bukatar ya kai passport dinsa Abuja ofishin minister domin neman visa. Da farincikinsa ya sanar da Izzatu saboda ranar girkinta ne. Tana jin haka ta tashi ta nufi dakinta.
Hamza ya bi bayanta da sauri don ya zata wani abin ne ya faru...Izzy saurin me kike yi haka ko gama sauraron abinda nace bakiyi ba?
Wardrobe ta bude ta janyo wata jaka sannan ta fuskance shi...naji abinda kace mana. Sai dai Sweety nasan ba abin mamaki bane idan kayi nasara saboda I believe in you my darling. Kayana zan hada na tafiyarmu Abujan....ta daga jakar sama, kana ganin wannan zata isa ko tayi kankanta?
Rasa bakin magana yayi sai binta yake da ido kamar lokacin ya fara ganinta. Babu godewa Allah, babu taya shi murna sai jaka da ta dauko zata hada kaya bayan shi kanshi bai sami cikakken bayani game da tafiyar ba. A kalla jakar zata dauki kaya bakwai zuwa goma idan an cusa su sosai. Ko ya fada mata a Abuja zasu yi course din ne bai sani ba. Haka ya fita ya barta ba tare da ya bata amsa ba ya tafi dakin Zuhra.
Kulu ne tumuli guda a gabanta tana warewa saboda ya samar mata wata makarantar sun bada kwangilar sakar rigunan sanyin makaranta.
Da murmushi ta tarbe shi tace Ya Hamza ba na hanaka satar kwana ba? Shima murmushin yayi ai kece satar kwanan. Ace mutum bashi da ikon ganin matarsa sai ranar girkinta.
Kusa da ita yaje ya zauna ya kama hannunta ya rike.
Cutie albishirinki? Idonta a kan fuskarsa tace goro Ya Hamzana.
Me zaki bani idan na fada miki?
Duk abinda kake so indai baifi karfina ba.