Sashe 41
Al'adun Wasu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan awa uku Alh Sunusi da Raliya ke zaune a dakin da Izzatu take. Farkawarta kenan tace Mum me nake yi a nan? A fusace Raliya tace ubanki kike yi Izzatu. Nace ubanki kike yi. Shashashar banza mara hankali, iliminki da shekarunki basu kara miki komai ba sai hauka. Alh Sunusi yace haba Raliya ya zakiyi mata magana irin haka bayan kinsan halin da take ciki. Tun dazu kike kuka kina addu'ar ta farfado. Ta tashi kuma kin bita da zagi.
Raliya tace to ya zanyi da yarinyar nan? Ta hade rai ta kalli Izzatu...har kin iya zubar da ciki ko? To Allah bai nufa ba wannan dai sai kin haife shi. Izzatu ta zaro ido...Mum kina nufin bai zube ba? Meyasa basu yi min wankin ciki ba? Ni wallahi bana son sake haihuwa. Su Khalifa sun isheni.
Maganarta sam bata yiwa iyayenta dadi ba. Raliya tace kaji da kunnenka ko? Ni kam nayi nadamar kyaleku da mukayi kuka zama turawan karfi da yaji. Zeenatu ta auri mijin da dabi'unsa tamkar wani bayahude har yau ban taba sonsa ba. Amma saboda mun baku damar yin yadda kuke so a dole muka barta da zabinta. Ke da Allah Ya rufawa asiri kuma kina neman tonawa kanki. Idan Hamza yaji abinda kika yi ya sakeki zaki yi bayani.
Izzatu ta daure fuska Mum bana son irin haka. Hamza bazai taba iya rayuwa batare dani ba. Muna son juna kuma ai nayi kokari da na haifa masa har 'ya'ya uku.
Alh Sunusi ya daka mata tsawa. Ashe abinda Mamanki take fada gaskiya ne baki da hankali. Duk laifinmu ne da muka baku irin wannan tarbiyar amma wallahi idan kika kuskura kika kara yunkurin zubar da cikin nan sai ranki ya baci. Kuma ni dai bazan kira Hamza na sanar dashi abinda kika yi ba, ai da kunya. Raliya tace nima ai ba fada zanyi ba. Dama karya tayi masa ta taho shine muma zaki ha'incemu ki zubar da ciki bamu sani ba.
Izzatu ta soma kuka ni duk kun tsaneni. Kawai don nayi aure shikenan kuma bani da 'yanci na zabarwa kaina abinda ya dace? Tana magana iyayenta suka fice ta cije lebe. Ita bata ga aibun abinda tayi ba. Haihuwa ce ta isheta haka. Tunanin abinda Hamza zaiyi idan yaji zancen nan tayi gara tayi shiru tunda idan ya sani fada zaiyi mata shima. Za dai ta kirashi ya aiko mata da kudi na hannunta sun kusa karewa.
*********
Kwanaki biyu da maganar Hamza da Zuhra ya dukufa nema mata makaranta saboda yadda ta dame shi. Da samples biyu data bashi yake yawo. Cikin ikon Allah a rana da uku wadda ta kama Juma'a ya sami wasu makarantu har biyu. Ba karamin farinciki yayi ba da hakan. Har mamaki yake yi yadda yake kwantar da kai a gaban Principal ko Headmaster yana neman alfarmar a bashi wannan kwangilar. Da gaske ba karamin matsi zasu shiga ba shi kuma baya son taba kudin kamfani ayyukansu su durkushe.
Tun a hanya ya kira Zuhra ya sanar da ita. Makaranta daya bangaren nursery za'ayiwa dayar kuma secondary ce ma. Har wani tsalle take yi ta tambayeshi kalolin da aka zaba ya fada mata. Kafin ya iso gida a cikin kudinta ta aiki Tala kasuwa ta siyo mata kulu da maballai. Bai dawo gida ba ranar sai tara saura. Bayan yaci abinci yace gobe zan duba sai a siyo kayan da zaki bukata. Inda zai samo kudin yake tunani. Zuhra tayi 'yar dariya tace ai har Tala ta siyo min tun dazu. Wani daki kusa da na Tala a kasan ta nuna masa kayan. Yace wa ya baki kudin? Ya Hamza akwai 'yan kudi a hannuna. Yanzu dai ka huta sai ka nuna min irin yadda kayan nasu suke na fara aiki. Sai wani farinciki take yi zata sami damar taimakonsa. Murmushi yayi yace nagode Cutie Allah Ya baki lada, tace amin.
Jikinsa a sanyaye ya tafi daki. Bayan dan lokaci Zuhra ta bi bayansa saboda ta kula da yanayinsa. Rashin kudi a wurin wanda ya saba rike su da tausayi. A bude ta tarar da kofar falon amma baya ciki. Tana kokarin shiga dakin taji muryarsa yana waya muryarsa a raunane. Maganar karshe kafin ya ajiye wayar taji yace " Inuwa kafi kowa sanin halin da nake ciki, idan baku maida hankali sosai akan aikin nan ba karshenta yarana idan anyi hutu bazasu koma school ba.".
Izzatu ta kirashi tayi masa karya tace tana bukatar kudi zata asibiti tana zazzabi tun kwanaki biyu da suka wuce ya fada mata bashi dasu ta ranta a nata zai biyata . Tun daga ranar tayi fushi ta kashe waya baya samunta. Ita a tunaninta kuntata mata kawai ya koyi yi saboda iyayensa. Gashi tana son biyan kudin asibiti bata son tambayar iyayenta tunda fushi suke da ita. Banda ita yana tunanin yadda zai biya kudin makarantar yara boko da islamiyya duka masu tsada suke zuwa.
Komawa da baya Zuhra tayi tana kuka cike da tausayin Hamza. Inda ta ajiye kudin da Baba ya bata da sauran na hannunta ta duba. Abinda yayi mata saura dubu saba'in da uku har dan kudin sakar da ta taho dashi. Dubu hamsin ta dauko har ta kai bakin kofar dakinta sai ta dawo tana tunani. Idan ta kaiwa Hamza kudin nan bazai taba yarda ya karba ba. A take tayi murmushi da dabara tazo mata. A cikin rigarta ta boye kudin ta koma dakinsa.
Kwance ta same shi akan gafo ko kaya bai cire ba bare yayi wanka. Ta karasa kusa da gadon, Ya Hamza ba lafiya ne? Murmushin dole ya kirkiro ya tashi gajiya ce kawai Cutie ke kuma ko tausa baki taba yi min ba. Kodayake nine ban koya miki wannan karatun ba. Tace to yi wankan sai nayi maka. Amma sai ka kawo cin hanci. Dariya take tana maganar domin ta rage masa damuwa. Yace to ki jira na fito zan baki.
Shigarsa toilet keda wuya Zuhra ta bude wardrobe dinsa duk ya hargitse ta fito da kayan. Har ya fito daga wanka tana gyara masa kayansa. Yayi murmushi yau Cutie abin kirki ake ji ne. To nagode ki gyara da kyau. Ita dai bata juyo ba don tasan daga shi sai tawul. A hankali ta juya taga ba ita yake kallo ba sai ta fito da kudin dake boye a jikinta harda dariyarta ta juyo, nayi tsintuwa ba sata ba. Hamza yace kinyi satar kenan. Ai ba'a tsintuwa a cikin daki. Kudin ta nuna masa da fara'a a fuskarta. Ya Hamza har a cikin kaya kake boye kudi? Jin abinda tace ya taho wurin da sauri. Mu gani ya fada yana mika hannu. Mika masa tayi tana cewa sai ka bani ladan tsintuwa. Yanayin farincikinsa bazai misaltu ba. Ba karamin dadi yaji ba wanda hakan da Zuhra ta gani yasa wani hawaye kokarin fito mata tayi saurin mayarwa. Hamza yana ta juya kudin yace ni bazan iya tuna lokacin da na ajiyesu ba. Tace a nan gefen na gansu. Kuka ke neman kwace mata saboda yadda taga yana farinciki don ya tsinci dubu hamsin abinda yafi karfi a da. Ta dan wayance bari na duba su Khalifa na dawo. Tana fita nasa hawayen suka sakko..bai yi kokarin mayar dasu ba sai ma sujjada da yayi ta godiya ga Allah da Ya bashi Zuhra. Tunda ya fito daga toilet ya kula da yadda take yawan juyowa ta kalle shi shiyasa a na karshen yayi saurin kawar da kai. Yana kallon lokacin da ta daga rigarta ta zaro kudin. Wai shi zata yiwa wayo kada yace ta bashi kyauta yaki karba. Zuhra ta cancanci duk wata soyayya da kauna daga gareshi kuma wannan dubu hamsin din yana fata Allah Ya bashi ikon biyanta da abinda ya fisu daraja. A hankali ya furta I love you Zuhra.
[10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU 62
Batul Mamman(Mrs)
Washegari tun da Zuhra ta tashi sallar asuba bata koma bacci ba. Tana idarwa ta sauka ta shiga kitchen. Breakfast ta fara hadawa sannan ta dora miyar abincin rana, sannan ta yanka dankali 'yan madaidaita ta dafa da kwai. Bayan ta gama ta hadasu wuri daya ta yanka cucumber da koren tattasai ta gurza caras ta saka mayonnaise. Cikin kankanin lokaci potato salad dinta ya hadu ta saka a fridge inda bazaiyi sanyi sosai ba, idan tayi sallar azahar taliya kawai zata dafa. Duk wannan saurin so take ta fara sakarta ne da wuri. Tana gamawa ta tafi daki zata yi wanka ta tarar yaran duk sun tashi. Bata sami nutsuwa ba sai da ta shiryasu har suka gama cin abinci, ta barsu wurin Tala ta shige dakin da ta ajiye kayan sakar.
Duba kayan da Hamza ya kawo tayi da irin tsarin da makarantun suka bashi. Cikin dan kankanin lokaci ta soma sakarta hankali kwance. Dayake abu ne da take so ta kware a sarrafa injin sakar. Na 'yan nursery din ta fara wanda zata yi musu guda dari da hamsin a dubu daya da dari bibbiyu su kuma su sayar a dubu da dari biyar. Kokarinta ta gama ko na makaranta daya ne kafin litinin ya fara kai musu. Idan aka biya tasan kudin zaiyi masa amfani sosai.
Wayar Izzatu ce ta tashi Hamza tana sanar dashi zata dawo washegari zata biyo jirgin safe. Hamza yace to Allah Ya kawoki lafiya. Tace Amin tunda kaki aiko min da kudi wannan ma Dad dina ne ya bani. Hamza yace to Allah Ya saka masa da alkhairi ya ajiye wayar. Ace ko sau daya zata ce bata kula da yanayinsa da ya canja ba bare ta tambayeshi meye damuwarsa. Tsaki yayi ya tashi ya shiga wanka. Yana fitowa yaci karo da breakfast dinsa a falonsa. Murmushi yayi ya zauna yaci ya koshi. Aiki yake son yi amma yau ko motsin Zuhra baiji ba shiyasa ya fasa ya sauka. Su Nana kawai ya gani a falon suna ta kiriniya yace ina Maama? Junior ya nuna masa dakin da take, kuma Daddy tace kada wanda ya shiga aiki zata yi. Sai a lokacin Hamza ya tuna da zancen saka yace to ku zauna bari naje nace mata sannu da aiki na dawo.
Raliya tace to ya zanyi da yarinyar nan? Ta hade rai ta kalli Izzatu...har kin iya zubar da ciki ko? To Allah bai nufa ba wannan dai sai kin haife shi. Izzatu ta zaro ido...Mum kina nufin bai zube ba? Meyasa basu yi min wankin ciki ba? Ni wallahi bana son sake haihuwa. Su Khalifa sun isheni.
Maganarta sam bata yiwa iyayenta dadi ba. Raliya tace kaji da kunnenka ko? Ni kam nayi nadamar kyaleku da mukayi kuka zama turawan karfi da yaji. Zeenatu ta auri mijin da dabi'unsa tamkar wani bayahude har yau ban taba sonsa ba. Amma saboda mun baku damar yin yadda kuke so a dole muka barta da zabinta. Ke da Allah Ya rufawa asiri kuma kina neman tonawa kanki. Idan Hamza yaji abinda kika yi ya sakeki zaki yi bayani.
Izzatu ta daure fuska Mum bana son irin haka. Hamza bazai taba iya rayuwa batare dani ba. Muna son juna kuma ai nayi kokari da na haifa masa har 'ya'ya uku.
Alh Sunusi ya daka mata tsawa. Ashe abinda Mamanki take fada gaskiya ne baki da hankali. Duk laifinmu ne da muka baku irin wannan tarbiyar amma wallahi idan kika kuskura kika kara yunkurin zubar da cikin nan sai ranki ya baci. Kuma ni dai bazan kira Hamza na sanar dashi abinda kika yi ba, ai da kunya. Raliya tace nima ai ba fada zanyi ba. Dama karya tayi masa ta taho shine muma zaki ha'incemu ki zubar da ciki bamu sani ba.
Izzatu ta soma kuka ni duk kun tsaneni. Kawai don nayi aure shikenan kuma bani da 'yanci na zabarwa kaina abinda ya dace? Tana magana iyayenta suka fice ta cije lebe. Ita bata ga aibun abinda tayi ba. Haihuwa ce ta isheta haka. Tunanin abinda Hamza zaiyi idan yaji zancen nan tayi gara tayi shiru tunda idan ya sani fada zaiyi mata shima. Za dai ta kirashi ya aiko mata da kudi na hannunta sun kusa karewa.
*********
Kwanaki biyu da maganar Hamza da Zuhra ya dukufa nema mata makaranta saboda yadda ta dame shi. Da samples biyu data bashi yake yawo. Cikin ikon Allah a rana da uku wadda ta kama Juma'a ya sami wasu makarantu har biyu. Ba karamin farinciki yayi ba da hakan. Har mamaki yake yi yadda yake kwantar da kai a gaban Principal ko Headmaster yana neman alfarmar a bashi wannan kwangilar. Da gaske ba karamin matsi zasu shiga ba shi kuma baya son taba kudin kamfani ayyukansu su durkushe.
Tun a hanya ya kira Zuhra ya sanar da ita. Makaranta daya bangaren nursery za'ayiwa dayar kuma secondary ce ma. Har wani tsalle take yi ta tambayeshi kalolin da aka zaba ya fada mata. Kafin ya iso gida a cikin kudinta ta aiki Tala kasuwa ta siyo mata kulu da maballai. Bai dawo gida ba ranar sai tara saura. Bayan yaci abinci yace gobe zan duba sai a siyo kayan da zaki bukata. Inda zai samo kudin yake tunani. Zuhra tayi 'yar dariya tace ai har Tala ta siyo min tun dazu. Wani daki kusa da na Tala a kasan ta nuna masa kayan. Yace wa ya baki kudin? Ya Hamza akwai 'yan kudi a hannuna. Yanzu dai ka huta sai ka nuna min irin yadda kayan nasu suke na fara aiki. Sai wani farinciki take yi zata sami damar taimakonsa. Murmushi yayi yace nagode Cutie Allah Ya baki lada, tace amin.
Jikinsa a sanyaye ya tafi daki. Bayan dan lokaci Zuhra ta bi bayansa saboda ta kula da yanayinsa. Rashin kudi a wurin wanda ya saba rike su da tausayi. A bude ta tarar da kofar falon amma baya ciki. Tana kokarin shiga dakin taji muryarsa yana waya muryarsa a raunane. Maganar karshe kafin ya ajiye wayar taji yace " Inuwa kafi kowa sanin halin da nake ciki, idan baku maida hankali sosai akan aikin nan ba karshenta yarana idan anyi hutu bazasu koma school ba.".
Izzatu ta kirashi tayi masa karya tace tana bukatar kudi zata asibiti tana zazzabi tun kwanaki biyu da suka wuce ya fada mata bashi dasu ta ranta a nata zai biyata . Tun daga ranar tayi fushi ta kashe waya baya samunta. Ita a tunaninta kuntata mata kawai ya koyi yi saboda iyayensa. Gashi tana son biyan kudin asibiti bata son tambayar iyayenta tunda fushi suke da ita. Banda ita yana tunanin yadda zai biya kudin makarantar yara boko da islamiyya duka masu tsada suke zuwa.
Komawa da baya Zuhra tayi tana kuka cike da tausayin Hamza. Inda ta ajiye kudin da Baba ya bata da sauran na hannunta ta duba. Abinda yayi mata saura dubu saba'in da uku har dan kudin sakar da ta taho dashi. Dubu hamsin ta dauko har ta kai bakin kofar dakinta sai ta dawo tana tunani. Idan ta kaiwa Hamza kudin nan bazai taba yarda ya karba ba. A take tayi murmushi da dabara tazo mata. A cikin rigarta ta boye kudin ta koma dakinsa.
Kwance ta same shi akan gafo ko kaya bai cire ba bare yayi wanka. Ta karasa kusa da gadon, Ya Hamza ba lafiya ne? Murmushin dole ya kirkiro ya tashi gajiya ce kawai Cutie ke kuma ko tausa baki taba yi min ba. Kodayake nine ban koya miki wannan karatun ba. Tace to yi wankan sai nayi maka. Amma sai ka kawo cin hanci. Dariya take tana maganar domin ta rage masa damuwa. Yace to ki jira na fito zan baki.
Shigarsa toilet keda wuya Zuhra ta bude wardrobe dinsa duk ya hargitse ta fito da kayan. Har ya fito daga wanka tana gyara masa kayansa. Yayi murmushi yau Cutie abin kirki ake ji ne. To nagode ki gyara da kyau. Ita dai bata juyo ba don tasan daga shi sai tawul. A hankali ta juya taga ba ita yake kallo ba sai ta fito da kudin dake boye a jikinta harda dariyarta ta juyo, nayi tsintuwa ba sata ba. Hamza yace kinyi satar kenan. Ai ba'a tsintuwa a cikin daki. Kudin ta nuna masa da fara'a a fuskarta. Ya Hamza har a cikin kaya kake boye kudi? Jin abinda tace ya taho wurin da sauri. Mu gani ya fada yana mika hannu. Mika masa tayi tana cewa sai ka bani ladan tsintuwa. Yanayin farincikinsa bazai misaltu ba. Ba karamin dadi yaji ba wanda hakan da Zuhra ta gani yasa wani hawaye kokarin fito mata tayi saurin mayarwa. Hamza yana ta juya kudin yace ni bazan iya tuna lokacin da na ajiyesu ba. Tace a nan gefen na gansu. Kuka ke neman kwace mata saboda yadda taga yana farinciki don ya tsinci dubu hamsin abinda yafi karfi a da. Ta dan wayance bari na duba su Khalifa na dawo. Tana fita nasa hawayen suka sakko..bai yi kokarin mayar dasu ba sai ma sujjada da yayi ta godiya ga Allah da Ya bashi Zuhra. Tunda ya fito daga toilet ya kula da yadda take yawan juyowa ta kalle shi shiyasa a na karshen yayi saurin kawar da kai. Yana kallon lokacin da ta daga rigarta ta zaro kudin. Wai shi zata yiwa wayo kada yace ta bashi kyauta yaki karba. Zuhra ta cancanci duk wata soyayya da kauna daga gareshi kuma wannan dubu hamsin din yana fata Allah Ya bashi ikon biyanta da abinda ya fisu daraja. A hankali ya furta I love you Zuhra.
[10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU 62
Batul Mamman(Mrs)
Washegari tun da Zuhra ta tashi sallar asuba bata koma bacci ba. Tana idarwa ta sauka ta shiga kitchen. Breakfast ta fara hadawa sannan ta dora miyar abincin rana, sannan ta yanka dankali 'yan madaidaita ta dafa da kwai. Bayan ta gama ta hadasu wuri daya ta yanka cucumber da koren tattasai ta gurza caras ta saka mayonnaise. Cikin kankanin lokaci potato salad dinta ya hadu ta saka a fridge inda bazaiyi sanyi sosai ba, idan tayi sallar azahar taliya kawai zata dafa. Duk wannan saurin so take ta fara sakarta ne da wuri. Tana gamawa ta tafi daki zata yi wanka ta tarar yaran duk sun tashi. Bata sami nutsuwa ba sai da ta shiryasu har suka gama cin abinci, ta barsu wurin Tala ta shige dakin da ta ajiye kayan sakar.
Duba kayan da Hamza ya kawo tayi da irin tsarin da makarantun suka bashi. Cikin dan kankanin lokaci ta soma sakarta hankali kwance. Dayake abu ne da take so ta kware a sarrafa injin sakar. Na 'yan nursery din ta fara wanda zata yi musu guda dari da hamsin a dubu daya da dari bibbiyu su kuma su sayar a dubu da dari biyar. Kokarinta ta gama ko na makaranta daya ne kafin litinin ya fara kai musu. Idan aka biya tasan kudin zaiyi masa amfani sosai.
Wayar Izzatu ce ta tashi Hamza tana sanar dashi zata dawo washegari zata biyo jirgin safe. Hamza yace to Allah Ya kawoki lafiya. Tace Amin tunda kaki aiko min da kudi wannan ma Dad dina ne ya bani. Hamza yace to Allah Ya saka masa da alkhairi ya ajiye wayar. Ace ko sau daya zata ce bata kula da yanayinsa da ya canja ba bare ta tambayeshi meye damuwarsa. Tsaki yayi ya tashi ya shiga wanka. Yana fitowa yaci karo da breakfast dinsa a falonsa. Murmushi yayi ya zauna yaci ya koshi. Aiki yake son yi amma yau ko motsin Zuhra baiji ba shiyasa ya fasa ya sauka. Su Nana kawai ya gani a falon suna ta kiriniya yace ina Maama? Junior ya nuna masa dakin da take, kuma Daddy tace kada wanda ya shiga aiki zata yi. Sai a lokacin Hamza ya tuna da zancen saka yace to ku zauna bari naje nace mata sannu da aiki na dawo.