Sashe 60
Al'adun Wasu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hamza ya shiga gidansa da murna ya ajiye Nana ya hau sama har yana tsallake bene uku uku don sauri. Dakin Izzatu ya fara shiga yaji alamun tana bandaki ya fita. Dama dai ba nan yafi damuwa da zuwa ba.
Cike da murna ya bude kofar dakin Zuhra yana tunanin me ya hanata fitowa tarbarsa a waje. Turus ya tsaya tun bai gama shiga ba, dakin yayi kura tamkar ya shekara babu shara. Da sauri ya fito ya koma dakin Izzatu wadda ke labe a jikin kofa. Zuciyarsa sai raya masa abubuwa take tun kafin ya tambayi ina Zuhra take.
Muryar Izzatu da kyar take fita saboda tsoro tace tun ranar da ka tafi ta bar gidan nan. Wani irin kallo ya bita dashi sannan ya dauki waya ya kira Zuhra. A kashe yaji wayar bayan ko da suka tsaya canjin jirgi sunyi waya. Nan take gaban [truncated by WhatsApp]
[10/24, 3:43 PM] +234 705 352 3457: AL'ADUN WASU 76
Batul Mamman(Mrs)
A yadda ya dago kai dole Izzatu ta kara tsorata ta shige daki ta kulle kofar da mukulli. Hamza bai kulata ba ya sauka ya tambayi Tala ina Zuhra take. Tala tace ita tun washegarin tafiyarsa rabon da ta ganta. Da ta dawo daga kauye ma bata gidan.
Wannan abu da daure kai yake. Maigadi ma irin amsar da ya bayar kenan. Murna da dokin dawowarsa gida duk suka bace a lokacin sai zulumin abinda ke faruwa.
Kofar dakin Izzatu ya koma yana bugawa iya karfinsa....Izzy ki bude kofar nan idan kina son kanki da arziki.
Daga ciki tace bazan bude ba Hamza. So kake ka taba lafiyar jikina akan abinda bani da masaniya akan sa.
Daurewa yayi yace ni ba dukanki zanyi ba. We need to talk. Ko kina da amsar da zaki bawa iyayenta ne?
Duk da haka Izzatu bata bude kofar ba sai da ya tabbatar mata babu abinda zaiyi mata.
Dakin nata duk a hargitse yake kamar ana wasan dambe aciki. Ko a mafarki bai taba tunanin akwai ranar da Izzy zata yi kazanta ba saboda ba halinta bane.
Kujerar gaban mudubi ya jawo ya zauna. Iyakar dauriya yake yi kada ya tsorata Izzatu taki bashi amsar da yake nema. A nutse ya fara magana.....Izzy kin tuna lokacin da muka fara haduwa?kunzo school dinmu ke da yayarki Zeenatu a Canada ko. Idan kin tuna ours was love at first sight. Daga haduwar farko bamu rabu ba sai da nasan gidanku da numbar wayarki. Kuma sanin kanki ne ko bayan aurenmu duk wata suka da ake kawo min game dake ban taba saurare ba saboda son da nake miki. Hatta iyayena basa son irin zaman da muke yi amma kullum ina supporting dinki. Haka ne???
A dan tsorace ta gyada kai.
Hamza yace good, ashe kenan duk ranar da kika ga na juya miki baya bai kamata kiga laifina ba. Kinfi kowa sanin da yadda na auri Zuhra. Kafin ba aureta na soma ganin sauyi a rayuwata wanda yasa dole na sake tunani akan yadda muke gudanar da rayuwarmu a matsayinmu na musulmi. Na rokeki da mu canja kika ki. Sai Allah Ya kawo matar da sanadiyarki ta shigo gidana amma sai ta dace da irin dabi'un da duk mai hankali yasan sune dabi'un da suka dace da al'adun mu. Bin al'adun wasu da muke yi tamkar mun saka mask(fuska)ne. Duk yadda muka so da nuna mu turawa ne hakan bazai taba tabbata ba saboda a karkashin fuskar nan mu na ainihin muna nan. Da ace kin dauki shawarata babu wani abu da Zuhra zata yi da zai dauke min hankali. Ke kika yi sake har yarinya kamarta ta zame min abin alfahari. Duk da haka kinsan a irin abubuwan da kike min kuma har yanzu kike gidan nan akwai sonki a zuciyata.
Duk tsarin zancen nan na Hamza hankalin Izzatu ba a kwance yake ba. Babu abinda take tsoro kamar yasan gaskiya ya saketa. Idan Hamza ya saketa tabbas zata iya rasa rayuwarta. Babu wani mutum da take so kamarsa.
A hankali yaje gabanta ya rike kafadunta. Idanunsa sunyi ja sosai...Izzy ki taimakeni ki fada min inda Zuhra take.
Hannunsa ta ture dama nasan duk wannan tsarin zancen kana yi ne don kawai kaji inda matarka take. To ni ban sani ba. Da zaka tafi ai ba ajiyarta ka bani ba. Tunda ka tafi bata sake kwana a gidan nan ba.
Kan Hamza ya daure...ranakun da kika ce tana dakinta ko ta fita duk karya ne kenan?
Izzatu tace karya ne. Nima nemanta nake yi saboda gudun rana irin wannan. Ka dawo ka fara blaming dina.
Shekaru sama da goma Hamza ya gama sanin Izzatu ya kuma san lokacin da zancenta yake karya...kisa mayafi ki fito ina jiranki, ki taho min da key din mota. Yana fadin haka ya fita daga dakin. Ji yake kamar ya shake Izzatu amma bazaiyi haka ba. Gara ya daure kila ta fadi gaskiya.
Sai da ya bita ciki har sau biyu tana kin fitowa karshe kusan janta yayi ya turata a mota. Gudu yake kamar motar zata tashi bai tsaya ko'ina ba sai gidansu.
Dama su Alhaji sun san hakan zai faru shiyasa aka hana Zuhra zaman falo. A dakin su Hamida ta zauna tayi tagumi. Ta rasa gane dalilin su Hajiya na kin sanar da Hamza inda take. Tana wannan zaman taji muryarsa a falo...gabanta ne ya fadi taji kamar ta fita. Ba karamin kewarsa takeyi ba. Domin ya dan wuce wata biyun kafin ya dawo.
*****
Hamida ya gani a falo tana masa sannu da zuwa ko amsawa baiyi ba yace ina Alhaji? Hanyar dakinsa ta nuna ya wuce yana jan hannun Izzatu.
Sallama ya rinka yi Mama ta fito da sauri. Itama Hajiya ta fito daga dakinta. Kana ganinsa kasan hankalinsa a tashe yake Mama tace Yaya lafiya?
Mama ina Alhaji?
Tace yana falonsa. Itama tausayi Hamza ya bata. Zata so a barshi yaga matarsa. Ta tabbatar ko zama baiyi ba ya fito.
Suna zazzaune a falon Alhajin Hamza ya gaishesu. Batare da ya jira sun amsa ba bare a tambayeshi ya hanya yace Zuhra ta bata.
Kamar gaske suka nuna mamakinsu. Alhaji yace wace irin magana ce wannan?
Hamza yace tunda na dawo banganta ba. Kuma kafin na taho kullum muna waya da ita amma yanzu na kasa samu. Na tambaya a gidan duk sunce tunda na tafi basu kara ganinta ba. Nayi tunanin zuwa gidansu amma ina tsoron ko bata can kada na tadawa su Baba hankali.
Alhaji ya kalli Izzatu yace ke kalle ni nan. Ai kuwa ta daga kai ta masa kiri da ido. Yayi murmushi irin na manya...tunda mijinku yayi tafiya kin fada mana baki ga Zuhra ba? Sai yau zaku zo nan kuna nemanta? Da kika zo gidan nan kwanaki ba cewa kika yi tana gida ba?
Hamza yace Alhaji duk karya take. Don Allah ku taimakeni....
Hajiya ta tashi zata bar falon. Tausayin danta take ji.
Maganar Izzatu ta dakatar da ita...Baby ina jin fa kauyensu ta koma. Kasan tun farko munyi shawarar zaka saketa bayan wata shida...
Ba kunya Hamza yasa hannu ya toshewa Izzatu baki a gaban iyayensa. Idan ya kyaleta zata baro masa matsala ne.
Alhaji yace sakar mata baki tayi magana.
Sakinta yayi yana harararta. Izzatu tace tunda aka yi auren ba sonta yake ba muka yanke shawarar bayan wata shida zai saketa. Ina jin saukaka masa tayi ta tafi kauye wurin 'yan uwansu.
Hamza ya dafe kai Izzatu kuwa tayi murmushi..ko ba komai yanzu ta fitar da kanta daga zargi.
Ran Alhaji a bace yace Yaya da gaske da girmanka da hankalinka ka taba fadar magana irin wannan?
Kai a kasa Hamza yace eh Alhaji, amma tuntuni maganar ta wuce.
Alhaji ya mike to ni babu ruwana. Tunda har yanzu bakayi hankali ba Allah Yasa a dace ka ganta. Kwana uku na baka ka nemo 'yar mutane ka bata takardarta. Na zata auren da nayi maka gata ne ashe kai tunanin mafita kawai kake yi.
Hamza ya fara bawa Alhaji hakuri. Wannan magana ta dade Alhaji. Don Allah kada kace na saketa wallahi ina sonta.
Idan ka iya nemota nan da kwana uku shikenan idan ba haka ba kuwa duk inda aka ganta zaka saketa ne. Ka tashi ka bani wuri.
Jiki ba kwari Hamza ya fita Izzatu na bin bayansa hankali ya dan kwanta ance zai saki Zuhra.
Suna fita Hajiya ta koma ta zauna. Alhaji yace kinga shirme irin na babana ko? Ni so nayi wannan mara kunyar ta fada da bakinta abinda tayiwa Zuhra yaji sai gashi ashe shima akwai nasa laifin. Ni kam da gaske idan auren nan bazai yiwu ba gara su rabu kada watarana su kashe 'yar mutane.
Mama tace anya Alhaji batun rabuwa bai taso ba. Yaran nan suna son junansu. Kayi hakuri ta koma dakinta. Tunda kace zaka hukunta Izzatu ai shikenan.
Shima Yayan sai na hukunta shi. Niyata a yau dinnan ya dauki matarsa. Amma tunda naji wannan zancen hukuncinsa shine ya tafi nemanta. Yadda suka kuntata mata a gidan nan suma su dandana.
****
Kwanaki biyu sun wuce a lokacin da Alhaji ya bawa Hamza. Police station din da yaje shi kanshi bai san adadinsu ba. Maganar bacci dama sai dai ya sace shi. Abinci ma rabonsa da abin kirki tun a jirgi. Lokaci guda duk ya zabge. Yana son bada cigiya a gidan rediyo da talabijin amma yana gudun kada su Umma su gani.
Da daddare ya bude jakar kayansa ya dauko tasu tsarabar. Babu wanda ya bawa komai sai a lokacin ya dauka ya tafi gidansu Zuhra.
Su Baba suna ta tambayarsa ya hanya amma hankalinsa na ga ta ina zai ga bullowar Zuhra. Sai da Umma tace tana fatan Zuhra lafiya kwana biyu basa samunta a waya ya tabbatar bata gidan. To shi yanzu ina zai duba kuma???
Da ya tafi Umma har kuka tayi tace ita wallahi zata fada masa inda Zuhra take....Haba Baban Zuhra ka duba kaga yadda ya rame duk ya fita hayyacinsa.
Baba yace nima ina tausayinsa amma ki bari muga iya gudun ruwan Alhaji. Mu bashi dama kamar yadda ya nemi alfarma.
Cike da murna ya bude kofar dakin Zuhra yana tunanin me ya hanata fitowa tarbarsa a waje. Turus ya tsaya tun bai gama shiga ba, dakin yayi kura tamkar ya shekara babu shara. Da sauri ya fito ya koma dakin Izzatu wadda ke labe a jikin kofa. Zuciyarsa sai raya masa abubuwa take tun kafin ya tambayi ina Zuhra take.
Muryar Izzatu da kyar take fita saboda tsoro tace tun ranar da ka tafi ta bar gidan nan. Wani irin kallo ya bita dashi sannan ya dauki waya ya kira Zuhra. A kashe yaji wayar bayan ko da suka tsaya canjin jirgi sunyi waya. Nan take gaban [truncated by WhatsApp]
[10/24, 3:43 PM] +234 705 352 3457: AL'ADUN WASU 76
Batul Mamman(Mrs)
A yadda ya dago kai dole Izzatu ta kara tsorata ta shige daki ta kulle kofar da mukulli. Hamza bai kulata ba ya sauka ya tambayi Tala ina Zuhra take. Tala tace ita tun washegarin tafiyarsa rabon da ta ganta. Da ta dawo daga kauye ma bata gidan.
Wannan abu da daure kai yake. Maigadi ma irin amsar da ya bayar kenan. Murna da dokin dawowarsa gida duk suka bace a lokacin sai zulumin abinda ke faruwa.
Kofar dakin Izzatu ya koma yana bugawa iya karfinsa....Izzy ki bude kofar nan idan kina son kanki da arziki.
Daga ciki tace bazan bude ba Hamza. So kake ka taba lafiyar jikina akan abinda bani da masaniya akan sa.
Daurewa yayi yace ni ba dukanki zanyi ba. We need to talk. Ko kina da amsar da zaki bawa iyayenta ne?
Duk da haka Izzatu bata bude kofar ba sai da ya tabbatar mata babu abinda zaiyi mata.
Dakin nata duk a hargitse yake kamar ana wasan dambe aciki. Ko a mafarki bai taba tunanin akwai ranar da Izzy zata yi kazanta ba saboda ba halinta bane.
Kujerar gaban mudubi ya jawo ya zauna. Iyakar dauriya yake yi kada ya tsorata Izzatu taki bashi amsar da yake nema. A nutse ya fara magana.....Izzy kin tuna lokacin da muka fara haduwa?kunzo school dinmu ke da yayarki Zeenatu a Canada ko. Idan kin tuna ours was love at first sight. Daga haduwar farko bamu rabu ba sai da nasan gidanku da numbar wayarki. Kuma sanin kanki ne ko bayan aurenmu duk wata suka da ake kawo min game dake ban taba saurare ba saboda son da nake miki. Hatta iyayena basa son irin zaman da muke yi amma kullum ina supporting dinki. Haka ne???
A dan tsorace ta gyada kai.
Hamza yace good, ashe kenan duk ranar da kika ga na juya miki baya bai kamata kiga laifina ba. Kinfi kowa sanin da yadda na auri Zuhra. Kafin ba aureta na soma ganin sauyi a rayuwata wanda yasa dole na sake tunani akan yadda muke gudanar da rayuwarmu a matsayinmu na musulmi. Na rokeki da mu canja kika ki. Sai Allah Ya kawo matar da sanadiyarki ta shigo gidana amma sai ta dace da irin dabi'un da duk mai hankali yasan sune dabi'un da suka dace da al'adun mu. Bin al'adun wasu da muke yi tamkar mun saka mask(fuska)ne. Duk yadda muka so da nuna mu turawa ne hakan bazai taba tabbata ba saboda a karkashin fuskar nan mu na ainihin muna nan. Da ace kin dauki shawarata babu wani abu da Zuhra zata yi da zai dauke min hankali. Ke kika yi sake har yarinya kamarta ta zame min abin alfahari. Duk da haka kinsan a irin abubuwan da kike min kuma har yanzu kike gidan nan akwai sonki a zuciyata.
Duk tsarin zancen nan na Hamza hankalin Izzatu ba a kwance yake ba. Babu abinda take tsoro kamar yasan gaskiya ya saketa. Idan Hamza ya saketa tabbas zata iya rasa rayuwarta. Babu wani mutum da take so kamarsa.
A hankali yaje gabanta ya rike kafadunta. Idanunsa sunyi ja sosai...Izzy ki taimakeni ki fada min inda Zuhra take.
Hannunsa ta ture dama nasan duk wannan tsarin zancen kana yi ne don kawai kaji inda matarka take. To ni ban sani ba. Da zaka tafi ai ba ajiyarta ka bani ba. Tunda ka tafi bata sake kwana a gidan nan ba.
Kan Hamza ya daure...ranakun da kika ce tana dakinta ko ta fita duk karya ne kenan?
Izzatu tace karya ne. Nima nemanta nake yi saboda gudun rana irin wannan. Ka dawo ka fara blaming dina.
Shekaru sama da goma Hamza ya gama sanin Izzatu ya kuma san lokacin da zancenta yake karya...kisa mayafi ki fito ina jiranki, ki taho min da key din mota. Yana fadin haka ya fita daga dakin. Ji yake kamar ya shake Izzatu amma bazaiyi haka ba. Gara ya daure kila ta fadi gaskiya.
Sai da ya bita ciki har sau biyu tana kin fitowa karshe kusan janta yayi ya turata a mota. Gudu yake kamar motar zata tashi bai tsaya ko'ina ba sai gidansu.
Dama su Alhaji sun san hakan zai faru shiyasa aka hana Zuhra zaman falo. A dakin su Hamida ta zauna tayi tagumi. Ta rasa gane dalilin su Hajiya na kin sanar da Hamza inda take. Tana wannan zaman taji muryarsa a falo...gabanta ne ya fadi taji kamar ta fita. Ba karamin kewarsa takeyi ba. Domin ya dan wuce wata biyun kafin ya dawo.
*****
Hamida ya gani a falo tana masa sannu da zuwa ko amsawa baiyi ba yace ina Alhaji? Hanyar dakinsa ta nuna ya wuce yana jan hannun Izzatu.
Sallama ya rinka yi Mama ta fito da sauri. Itama Hajiya ta fito daga dakinta. Kana ganinsa kasan hankalinsa a tashe yake Mama tace Yaya lafiya?
Mama ina Alhaji?
Tace yana falonsa. Itama tausayi Hamza ya bata. Zata so a barshi yaga matarsa. Ta tabbatar ko zama baiyi ba ya fito.
Suna zazzaune a falon Alhajin Hamza ya gaishesu. Batare da ya jira sun amsa ba bare a tambayeshi ya hanya yace Zuhra ta bata.
Kamar gaske suka nuna mamakinsu. Alhaji yace wace irin magana ce wannan?
Hamza yace tunda na dawo banganta ba. Kuma kafin na taho kullum muna waya da ita amma yanzu na kasa samu. Na tambaya a gidan duk sunce tunda na tafi basu kara ganinta ba. Nayi tunanin zuwa gidansu amma ina tsoron ko bata can kada na tadawa su Baba hankali.
Alhaji ya kalli Izzatu yace ke kalle ni nan. Ai kuwa ta daga kai ta masa kiri da ido. Yayi murmushi irin na manya...tunda mijinku yayi tafiya kin fada mana baki ga Zuhra ba? Sai yau zaku zo nan kuna nemanta? Da kika zo gidan nan kwanaki ba cewa kika yi tana gida ba?
Hamza yace Alhaji duk karya take. Don Allah ku taimakeni....
Hajiya ta tashi zata bar falon. Tausayin danta take ji.
Maganar Izzatu ta dakatar da ita...Baby ina jin fa kauyensu ta koma. Kasan tun farko munyi shawarar zaka saketa bayan wata shida...
Ba kunya Hamza yasa hannu ya toshewa Izzatu baki a gaban iyayensa. Idan ya kyaleta zata baro masa matsala ne.
Alhaji yace sakar mata baki tayi magana.
Sakinta yayi yana harararta. Izzatu tace tunda aka yi auren ba sonta yake ba muka yanke shawarar bayan wata shida zai saketa. Ina jin saukaka masa tayi ta tafi kauye wurin 'yan uwansu.
Hamza ya dafe kai Izzatu kuwa tayi murmushi..ko ba komai yanzu ta fitar da kanta daga zargi.
Ran Alhaji a bace yace Yaya da gaske da girmanka da hankalinka ka taba fadar magana irin wannan?
Kai a kasa Hamza yace eh Alhaji, amma tuntuni maganar ta wuce.
Alhaji ya mike to ni babu ruwana. Tunda har yanzu bakayi hankali ba Allah Yasa a dace ka ganta. Kwana uku na baka ka nemo 'yar mutane ka bata takardarta. Na zata auren da nayi maka gata ne ashe kai tunanin mafita kawai kake yi.
Hamza ya fara bawa Alhaji hakuri. Wannan magana ta dade Alhaji. Don Allah kada kace na saketa wallahi ina sonta.
Idan ka iya nemota nan da kwana uku shikenan idan ba haka ba kuwa duk inda aka ganta zaka saketa ne. Ka tashi ka bani wuri.
Jiki ba kwari Hamza ya fita Izzatu na bin bayansa hankali ya dan kwanta ance zai saki Zuhra.
Suna fita Hajiya ta koma ta zauna. Alhaji yace kinga shirme irin na babana ko? Ni so nayi wannan mara kunyar ta fada da bakinta abinda tayiwa Zuhra yaji sai gashi ashe shima akwai nasa laifin. Ni kam da gaske idan auren nan bazai yiwu ba gara su rabu kada watarana su kashe 'yar mutane.
Mama tace anya Alhaji batun rabuwa bai taso ba. Yaran nan suna son junansu. Kayi hakuri ta koma dakinta. Tunda kace zaka hukunta Izzatu ai shikenan.
Shima Yayan sai na hukunta shi. Niyata a yau dinnan ya dauki matarsa. Amma tunda naji wannan zancen hukuncinsa shine ya tafi nemanta. Yadda suka kuntata mata a gidan nan suma su dandana.
****
Kwanaki biyu sun wuce a lokacin da Alhaji ya bawa Hamza. Police station din da yaje shi kanshi bai san adadinsu ba. Maganar bacci dama sai dai ya sace shi. Abinci ma rabonsa da abin kirki tun a jirgi. Lokaci guda duk ya zabge. Yana son bada cigiya a gidan rediyo da talabijin amma yana gudun kada su Umma su gani.
Da daddare ya bude jakar kayansa ya dauko tasu tsarabar. Babu wanda ya bawa komai sai a lokacin ya dauka ya tafi gidansu Zuhra.
Su Baba suna ta tambayarsa ya hanya amma hankalinsa na ga ta ina zai ga bullowar Zuhra. Sai da Umma tace tana fatan Zuhra lafiya kwana biyu basa samunta a waya ya tabbatar bata gidan. To shi yanzu ina zai duba kuma???
Da ya tafi Umma har kuka tayi tace ita wallahi zata fada masa inda Zuhra take....Haba Baban Zuhra ka duba kaga yadda ya rame duk ya fita hayyacinsa.
Baba yace nima ina tausayinsa amma ki bari muga iya gudun ruwan Alhaji. Mu bashi dama kamar yadda ya nemi alfarma.