Sashe 24
Al'adun Wasu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Manyan architects yau da kanka a office dina. Manaja ke magana yana tashi tsaye suka gaisa da Hamza. Kowa fuskarsa dauke da murmushi suka tambayi juna iyali. Manaja yace sai kuma naji kayi aure ba labari. Kai Hamza ya dan sosa yana tunanin yadda zance ke yawo a gari..kayi hakuri abin ne yazo a gaggauce. Babu komai Allah Ya sanya alkhairi. Yanzu dai how can I help you? Tashi Hamza yayi kada ka damu shigowa nayi mu gaisa na riga na sanar dasu a costumer care alert ne bana ji tun last friday. Kuma har a atm da na cire kudi still banji ba. Manaja yayi dariya ai dole ka damu ku masu harka da manyan kudi. Suna magana text ya shigowa Hamza. Yayi murmushi dadina da bankin nan saurin gyara abu. Gashi har alerts din sun shigo. Yanayin fuskarsa ne ya soma canjawa a take. Manaja ya naga alert na an cire ten million har sau biyu a ranar friday din? Manaja ma dena murmushi yayi ai sau biyun ne Architect. Ka turo sakatare dinka sannan ga mamakina ka turo wani Mr..Mr....mtsw na manta sunan amma dai na kira nayi confirming a wurinka kafin a sakar masa kudin.
Jiri ne ya soma dibar Hamza daga tsaye yayi saurin dafa tebur din manaja ya zauna. Da kyar ya iya cewa Mr Oscar? Eh shi kuwa manajan ya amsa. Ka tuna na kira na tambayeka kace eh kaine ka turo shi. Tabbas manaja ya kira amma a lokacin Izzatu ke faman daga murya tana masifa sai ya saki Zuhra baiji abinda manajan yace ba ya amsa masa. Wato shiyasa Oscar yace mamansa ba lafiya ya tafi garinsu gashi an kusa sati babu mai samunsa a waya. Allahumma ajirni fi musibati wa akhlufni khairan minha.
[9/25, 3:53 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 38
Batul Mamman(Mrs)
A rikice manaja ya fara tambayar Hamza ko sunyi kuskure ne. Numfashin Hamza da kyar yake fita ya dago idanunsa da suka yi nauyi lokaci guda yace babu abinda kayi manaja. Matsalar daga bangarena ne. Sau biyu yana yunkurin tashi amma kafafunsa sun kasa daukarsa. Manajan sai bashi baki yake yana rokonsa ya zauna har zuciyarsa ta daidaita amma sam yaki zama. Ko da ya shiga mota rasa wurin zuwa yayi. Gidansa zai tafi ko office zai koma. Yafi rabin awa a motar kafin ya tayar ya dauki hanya.
Lokacin da ya shiga gidan babu kowa sai Kande mai aikinsu. Da fara'arta ta tare shi tana masa sannu da zuwa. Jikinsa duk a sanyaye yake yace ina mutan gidan ne naji shiru. Nura yana daki su Adabiyya kuma sun tafi makatanta. Hajiya da Mama kuma sunje unguwa. To din ma da kyar ya iya fada sai ya tashi ya tafi dakin Hajiya. Babu abinda yake a lokacin kamar yaga mahaifiyasa. Yaji dadi a bude ta barshi kamar tasan zai zo. Gadonta ya nufa ya kwanta abinda ya dade baiyi ba. Yana rufe ido sai wasu zafafan hawaye suka sauko masa. Ji yake kamar komai nashi ya tsaya cak. Cheque din da Mr Oscar ya dauka hade da sauran da suke office dinsa idan an hada miliyan arbain kenan zai hada ya bawa su Mr Peter ya kawo karshen contract dinsu. A dalilin hada wannan kudin gabadaya maaikatansa suka amince da karban rabin albashinsu a wannan watan don kawai su tseratar da kamfanin. Yanzu gashi miliyan goma ta tafi a kudin bai san ta ina zai samu su ba. Ginin gidansa yaci kudi ba na wasa ba. Idan kuma ya tattara kudaden account dinsa tare da sayar da filayensa zai iya biyan kudin to amma rike iyalinsa zai zama da matsala domin kuwa akalla kafin kudin ayyukan da yake su fito zai dan dauki lokaci. Yana wannan tunanin bacci ya dauke shi.
Hajiya ta kira Mama ko sun taho daukarta daga tata unguwar Mama tace tun dazu nake kiranki ban samu ba. Gamu a garejin makanike ban je inda zani ba. Amma na fasa ana gamawa zamu biyo. Hajiya tace babu komai bari na bi adaidaita sahu kaina ke ciwo. To ki kira Nura mana yazo ya dauke ki. Hajiya tace babu komai shima yau da mura ya tashi. Sai kun dawo ni zan wuce gida. Tana gama wayar suka yi sallama da kawarta da taje dubawa ta fita ta hau adaidaita sahu.
Gabanta yayi mummunan faduwa ganin mutum a kwance a kan gadonta. Alhaji yana Kumo kuma ko shine da wuya ya kwanta a dakinta. Nura kuma sai da ta leka dakinsa ta dubashi sannan ta taho nata. Babu inda baya rawa a jikinta ta ja kafa ta je gefen gadon inda zata ga fuskar mai baccin. Sai da ta dan ja baya saboda wanda bata taba tsammani ba ta gani. A tsorace tace Yaya....shima kansa ke masifar ciwo ya bude idanunsa da kyar. Hawaye ne bushe a fuskarshi Hajiya ta matsa ta taba shi. Bakinta har rawa yake saboda tsoron abinda zai ce tace Yaya me ya faru? Tashi yayi ya gyara rigarsa da ta yamutse sannan ya mayar da hularsa. Yana dan murmushi yace Hajiya babu komai. Zuwa nayi mu gaisa duk bakwa gidan. Bari na koma office sai anjima. Hannunsa ta rike. Itama hawayen take yi....haba Yaya duk duniya idan akwai wanda zaka boyewa damuwarka kasan banda ni ko. Bar ganin ban fiye shiga harkarka ba duk yanayin da ka shiga nakan gane na farinciki ne ko akasinsa. Dawowa yayi yasa mata kuka kamar karamin yaro. Kai bakace Hamza bane dan shekara talatin da takwas mijin Izzatu da Zuhra. Akan kujera ta zauna tana rike da hannunsa ya zauna a gabanta. Kansa ta dora akan cinyarta yayi kukansa mai isarsa. Rabonsa da yi mata irin kukan nan tun ranar da zai tafi Canada. Duk ranar da yayi irinsa to ba karamar damuwa yake ciki ba. Babu wanda yasan yana yi sai ita mahaifiyarsa. Cike da tausayawa irin ta uwa ta rinka shafa kansa har yayi shiru. Ko da ya dago kansa murmushi ne a fuskarsa yace Hajiya na dade banyi miki kuka ba ko. Yau ma sha'awarsa nayi shine na taso daga office. Bari na koma ana jirana meeting karfe biyu da rabi. Lokacin biyu saura kwata. Tunaninsa bai wuce yadda ya mori kudinsa ba lokacin da yake dasu shi kadai. Sai da matsala ta tashi zaizo ya tayarwa da mahaifiyarsa rai. Ya santa bata da magana sosai, ba lallai ko Alhaji ta fadawa amma zata shiga damuwa. Hajiya tace tunda baka son fada min damuwarka zan tayaka addua kamar kullum. Allah Ya kawo sauki cikin dukkan al'amuranka. Ka yawaita ambaton Allah hakan yana yaye damuwa da bacin rai, sannan kayi kokarin sauke hakkin wadanda ke kanka Allah Yayi maka albarka. Wani hawayen ne ya sauko masa yayi saurin gogewa. Amin Hajiya nagode. Tana kallo ya fita ta shiga toilet tayi alwala. Tasan da kansa zaizo ya fada mata matsalar amma abinda yafi dacewa yanzu tayi zata masa. Addua ta dukufa yi masa sannan ta saka dukkan kannensa da iyalansu.
Waya yayiwa Inuwa meeting sai gobe baya jindadin jikinsa. Tunani ne fal a zuciyarsa. Sai yanzu yake tunawa cewa Allah SWT Ya na jarabtar bayinsa ta hanyoyi da dama. A irin rayuwar sakaci da addini da yayi ai dole watarana ya fuskanci irin wannan. Sai yanzu ya sake nadamar abubuwan da yayi a baya da wanda yake kanyi yanzu wato sake da hakkokin matarsa don a zahiri suna damunsa. Sonta kawai baya yi. Zaiyi kokarin kyautata alakarsa da Mahaliccinsa da sauran mutane. Itama Zuhra zaiyi kokari ya sake da ita zuwa lokacin da zai saketa. Tunda basa son juna rabuwar ce zata fi. ta yadda bazai cigaba da daukan hakkinta ba. Zai bari sai komai ya lafa masa a wurin aiki sai ya sanar da Alhaji zai saketa saboda gudun kada Allah Ya kamashi. A lokaci daya duk sai ya zama abin tausayi.
[9/25, 3:54 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 39
Batul Mamman(Mrs)
Karo na biyar kenan da Zuhra ke dandana ruwan miyarta. Yawunta duk ya tsinke saboda yadda kamshin daddawa ke tashi. Nana na biye da ita a kitchen din har ta gama. Tuwon shinkafa tayi malmala biyar yadda zai isheta taci da rana, da daddare sannan ta sami na dumame da safe. Plate ta dauko mai dan fadi da zurfi ta saka malmalar da tafi kowacce girma da miyar kukarta duk a hade. Manshanu kadan ta zuba ta goya Nana a bayanta ba zani ta dauki plate din da hannu biyu ta tafi falo. Tana tafiya tana cewa Nana rike wuyana sosai fa. Ita kuwa Nana sai murna take tace toh.
Sai da ta shimfida tabarma kusa ta dinning table sannan ta zauna cin tuwo. Loma take kaiwa kamar za'a kwace. Tana ci tana bawa Nana a baki. Sun kusa cin rabi Izzatu ta sauko...idanunta kan Zuhra tana bawa yarta tuwo a baki. Har da nan gudunta tayi saurin zuwa inda suke ta dauke Nana tana ta warin kuka da daddawa. Zuhra ya zaki bata abincinki ke da aka ce ki dafa naki ke kadai? Ni ban saba bata abinci da hannu ba kuma bama tuwo sosai saboda yayi mata nauyi. Bata nuna jin haushi ba tace kiyi hakuri ban sani ba. Ganin Izzatu tayi hanyar kitchen yasa Nana ihu tana cewa Mummy sauketa, sauketa abinci. Izzatu tace naji yunwa kike ji bari na wanke miki baki na zuba miki couscous. Bata ankara ba Nana ta galla mata cizo a kafada. Ba shiri ta sauketa tana sosa wurin. Ita kuwa da gudu ta koma gaban kwanon Zuhra. Hannu biyu tasa tana ci bata jira Zuhra ta bata ba. Sake komawa Izzatu tayi zata dauketa sai taji muryar Hamza yana sallama.
Yana shigowa Zuhra ta kai wata shirgegiyar loma bakinta. Ido suka hada ai kuwa ta kware saboda kunya. Ji yayi nauyin zuciyarsa ya ragu saboda yadda yaga tana cin tuwon cike da nishadi. Izzatu tace sweety kaga rigimar Nana wai sai taci abincin Zuhra. To ki kyaleta mana ya fada tare da wucewa sama. Ita kanta Zuhra tayi mamakin amsarsa. Bayansa Izzatu tabi tana masa sannu da zuwa.
Jiri ne ya soma dibar Hamza daga tsaye yayi saurin dafa tebur din manaja ya zauna. Da kyar ya iya cewa Mr Oscar? Eh shi kuwa manajan ya amsa. Ka tuna na kira na tambayeka kace eh kaine ka turo shi. Tabbas manaja ya kira amma a lokacin Izzatu ke faman daga murya tana masifa sai ya saki Zuhra baiji abinda manajan yace ba ya amsa masa. Wato shiyasa Oscar yace mamansa ba lafiya ya tafi garinsu gashi an kusa sati babu mai samunsa a waya. Allahumma ajirni fi musibati wa akhlufni khairan minha.
[9/25, 3:53 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 38
Batul Mamman(Mrs)
A rikice manaja ya fara tambayar Hamza ko sunyi kuskure ne. Numfashin Hamza da kyar yake fita ya dago idanunsa da suka yi nauyi lokaci guda yace babu abinda kayi manaja. Matsalar daga bangarena ne. Sau biyu yana yunkurin tashi amma kafafunsa sun kasa daukarsa. Manajan sai bashi baki yake yana rokonsa ya zauna har zuciyarsa ta daidaita amma sam yaki zama. Ko da ya shiga mota rasa wurin zuwa yayi. Gidansa zai tafi ko office zai koma. Yafi rabin awa a motar kafin ya tayar ya dauki hanya.
Lokacin da ya shiga gidan babu kowa sai Kande mai aikinsu. Da fara'arta ta tare shi tana masa sannu da zuwa. Jikinsa duk a sanyaye yake yace ina mutan gidan ne naji shiru. Nura yana daki su Adabiyya kuma sun tafi makatanta. Hajiya da Mama kuma sunje unguwa. To din ma da kyar ya iya fada sai ya tashi ya tafi dakin Hajiya. Babu abinda yake a lokacin kamar yaga mahaifiyasa. Yaji dadi a bude ta barshi kamar tasan zai zo. Gadonta ya nufa ya kwanta abinda ya dade baiyi ba. Yana rufe ido sai wasu zafafan hawaye suka sauko masa. Ji yake kamar komai nashi ya tsaya cak. Cheque din da Mr Oscar ya dauka hade da sauran da suke office dinsa idan an hada miliyan arbain kenan zai hada ya bawa su Mr Peter ya kawo karshen contract dinsu. A dalilin hada wannan kudin gabadaya maaikatansa suka amince da karban rabin albashinsu a wannan watan don kawai su tseratar da kamfanin. Yanzu gashi miliyan goma ta tafi a kudin bai san ta ina zai samu su ba. Ginin gidansa yaci kudi ba na wasa ba. Idan kuma ya tattara kudaden account dinsa tare da sayar da filayensa zai iya biyan kudin to amma rike iyalinsa zai zama da matsala domin kuwa akalla kafin kudin ayyukan da yake su fito zai dan dauki lokaci. Yana wannan tunanin bacci ya dauke shi.
Hajiya ta kira Mama ko sun taho daukarta daga tata unguwar Mama tace tun dazu nake kiranki ban samu ba. Gamu a garejin makanike ban je inda zani ba. Amma na fasa ana gamawa zamu biyo. Hajiya tace babu komai bari na bi adaidaita sahu kaina ke ciwo. To ki kira Nura mana yazo ya dauke ki. Hajiya tace babu komai shima yau da mura ya tashi. Sai kun dawo ni zan wuce gida. Tana gama wayar suka yi sallama da kawarta da taje dubawa ta fita ta hau adaidaita sahu.
Gabanta yayi mummunan faduwa ganin mutum a kwance a kan gadonta. Alhaji yana Kumo kuma ko shine da wuya ya kwanta a dakinta. Nura kuma sai da ta leka dakinsa ta dubashi sannan ta taho nata. Babu inda baya rawa a jikinta ta ja kafa ta je gefen gadon inda zata ga fuskar mai baccin. Sai da ta dan ja baya saboda wanda bata taba tsammani ba ta gani. A tsorace tace Yaya....shima kansa ke masifar ciwo ya bude idanunsa da kyar. Hawaye ne bushe a fuskarshi Hajiya ta matsa ta taba shi. Bakinta har rawa yake saboda tsoron abinda zai ce tace Yaya me ya faru? Tashi yayi ya gyara rigarsa da ta yamutse sannan ya mayar da hularsa. Yana dan murmushi yace Hajiya babu komai. Zuwa nayi mu gaisa duk bakwa gidan. Bari na koma office sai anjima. Hannunsa ta rike. Itama hawayen take yi....haba Yaya duk duniya idan akwai wanda zaka boyewa damuwarka kasan banda ni ko. Bar ganin ban fiye shiga harkarka ba duk yanayin da ka shiga nakan gane na farinciki ne ko akasinsa. Dawowa yayi yasa mata kuka kamar karamin yaro. Kai bakace Hamza bane dan shekara talatin da takwas mijin Izzatu da Zuhra. Akan kujera ta zauna tana rike da hannunsa ya zauna a gabanta. Kansa ta dora akan cinyarta yayi kukansa mai isarsa. Rabonsa da yi mata irin kukan nan tun ranar da zai tafi Canada. Duk ranar da yayi irinsa to ba karamar damuwa yake ciki ba. Babu wanda yasan yana yi sai ita mahaifiyarsa. Cike da tausayawa irin ta uwa ta rinka shafa kansa har yayi shiru. Ko da ya dago kansa murmushi ne a fuskarsa yace Hajiya na dade banyi miki kuka ba ko. Yau ma sha'awarsa nayi shine na taso daga office. Bari na koma ana jirana meeting karfe biyu da rabi. Lokacin biyu saura kwata. Tunaninsa bai wuce yadda ya mori kudinsa ba lokacin da yake dasu shi kadai. Sai da matsala ta tashi zaizo ya tayarwa da mahaifiyarsa rai. Ya santa bata da magana sosai, ba lallai ko Alhaji ta fadawa amma zata shiga damuwa. Hajiya tace tunda baka son fada min damuwarka zan tayaka addua kamar kullum. Allah Ya kawo sauki cikin dukkan al'amuranka. Ka yawaita ambaton Allah hakan yana yaye damuwa da bacin rai, sannan kayi kokarin sauke hakkin wadanda ke kanka Allah Yayi maka albarka. Wani hawayen ne ya sauko masa yayi saurin gogewa. Amin Hajiya nagode. Tana kallo ya fita ta shiga toilet tayi alwala. Tasan da kansa zaizo ya fada mata matsalar amma abinda yafi dacewa yanzu tayi zata masa. Addua ta dukufa yi masa sannan ta saka dukkan kannensa da iyalansu.
Waya yayiwa Inuwa meeting sai gobe baya jindadin jikinsa. Tunani ne fal a zuciyarsa. Sai yanzu yake tunawa cewa Allah SWT Ya na jarabtar bayinsa ta hanyoyi da dama. A irin rayuwar sakaci da addini da yayi ai dole watarana ya fuskanci irin wannan. Sai yanzu ya sake nadamar abubuwan da yayi a baya da wanda yake kanyi yanzu wato sake da hakkokin matarsa don a zahiri suna damunsa. Sonta kawai baya yi. Zaiyi kokarin kyautata alakarsa da Mahaliccinsa da sauran mutane. Itama Zuhra zaiyi kokari ya sake da ita zuwa lokacin da zai saketa. Tunda basa son juna rabuwar ce zata fi. ta yadda bazai cigaba da daukan hakkinta ba. Zai bari sai komai ya lafa masa a wurin aiki sai ya sanar da Alhaji zai saketa saboda gudun kada Allah Ya kamashi. A lokaci daya duk sai ya zama abin tausayi.
[9/25, 3:54 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 39
Batul Mamman(Mrs)
Karo na biyar kenan da Zuhra ke dandana ruwan miyarta. Yawunta duk ya tsinke saboda yadda kamshin daddawa ke tashi. Nana na biye da ita a kitchen din har ta gama. Tuwon shinkafa tayi malmala biyar yadda zai isheta taci da rana, da daddare sannan ta sami na dumame da safe. Plate ta dauko mai dan fadi da zurfi ta saka malmalar da tafi kowacce girma da miyar kukarta duk a hade. Manshanu kadan ta zuba ta goya Nana a bayanta ba zani ta dauki plate din da hannu biyu ta tafi falo. Tana tafiya tana cewa Nana rike wuyana sosai fa. Ita kuwa Nana sai murna take tace toh.
Sai da ta shimfida tabarma kusa ta dinning table sannan ta zauna cin tuwo. Loma take kaiwa kamar za'a kwace. Tana ci tana bawa Nana a baki. Sun kusa cin rabi Izzatu ta sauko...idanunta kan Zuhra tana bawa yarta tuwo a baki. Har da nan gudunta tayi saurin zuwa inda suke ta dauke Nana tana ta warin kuka da daddawa. Zuhra ya zaki bata abincinki ke da aka ce ki dafa naki ke kadai? Ni ban saba bata abinci da hannu ba kuma bama tuwo sosai saboda yayi mata nauyi. Bata nuna jin haushi ba tace kiyi hakuri ban sani ba. Ganin Izzatu tayi hanyar kitchen yasa Nana ihu tana cewa Mummy sauketa, sauketa abinci. Izzatu tace naji yunwa kike ji bari na wanke miki baki na zuba miki couscous. Bata ankara ba Nana ta galla mata cizo a kafada. Ba shiri ta sauketa tana sosa wurin. Ita kuwa da gudu ta koma gaban kwanon Zuhra. Hannu biyu tasa tana ci bata jira Zuhra ta bata ba. Sake komawa Izzatu tayi zata dauketa sai taji muryar Hamza yana sallama.
Yana shigowa Zuhra ta kai wata shirgegiyar loma bakinta. Ido suka hada ai kuwa ta kware saboda kunya. Ji yayi nauyin zuciyarsa ya ragu saboda yadda yaga tana cin tuwon cike da nishadi. Izzatu tace sweety kaga rigimar Nana wai sai taci abincin Zuhra. To ki kyaleta mana ya fada tare da wucewa sama. Ita kanta Zuhra tayi mamakin amsarsa. Bayansa Izzatu tabi tana masa sannu da zuwa.