Sashe 74
Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
***
Wajejen karfe uku sai gamu cikin garin Kaduna. Ya karya kan motar ya dauki hanyar anguwar Kabala Custain. Ni sam bam ma san nan gidan Ummi yake ba. Yayi (parking) bayan maigadin gidan ya bude get din gaba daya. Su Yahya ne suka fito ashe duk suna gidan sunzo musu wuni, abin mamaki har da su Walida, Abdallah, Kausar da Walid autanmu. Nan gidan ya rude da sowar kannen mu kamar zasu hadiye mu.
A sannan ne na gane gidan Ummi da Yaya Bashir ne ganin tangamemen hoton su (window size) ranar (cocktail) din (Indoor sport hall) kafe a kayataccen falon.
Sai na wuce kai tsaye zuwa uwar dakin matar gidan babu wanda na kula a cikinsu sai cika nake ina batsewa. Na zauna a gefen gadonta ina kallon dakin kallon kurilla, na jiyo alamar tana (toilet) ne wanda ke makale da dakin nata tana wanka.
Ummi tunda taji ana oyoyo Yaya Fa'izah, oyoyo Yaya Fa'iz tayiwa wankan baja-baja ta fito a guje duk rabin jikinta kumfa ta fado mini.
Na ture ta na ce, "Ke baki da hankali ne za ki jikani? Don kawai nazo gidanki? Ba tambayar mutum ya yake? Ko wane hali yake ciki?"
Ta daga ni tana dariya, ta rasa inda zata sa kanta don farin ciki. Na bita da kallo har cikin ta ya tasa. Na kama baki cikin tsananin mamaki domin na dauka da da wasa take kamar a bakin kofa ake tuntube da cikin?
Ta sunkuya ta zauna a gefena hannuwanta duka biyu tallabe da fuskarta tana murmushi, ta ce.
"Fa'izah matar Yaya Fa'iz! Sai kyallin amarci kuke don na hango shi ta taga, daga ina kuke haka? Naji labarin Baba ya kore ku, tsammanin mu kun bar kasar babu sallama ga kowa".
Na hade girar sama da na kasa, na ce.
"Kin san Allah ki fita daga harkata, wane irin an kore ni kamar wata shegiya? Maras kunya fitsararriya, kyallin amarcin uban wa? Amarcin yaci ta kaza-kazan sa". Na mirgino ashariya.
Ummi ta dafe baki, sai kuma ta fashe da dariya.
"Oho dai! Mun gane kiyayya taci uwatar, Pilot yayi fari yayi kiba, Fa'izah ta rame saboda wuyar amarci amma ta zama kyakkyawa. Shin wai a ina aka yada zango ne?"
Ganin tana neman maishe ni mahaukaciya na mike nayi (toilet) don inyi wanka in sauya kunzugu na ko naji dadin jikina. Na fito daure da tawul tana make-up a (dressing mirrow) fuska kamar jikakken kwaki don turbunewa na ce.
"Bani kaya in sauya, ko ba hali?"
Tayi dariya kawai, ta dauko min atamfa Vlisko mai ruwan ganye mai karamin dinki na karba na saka nayi kwalliyata sosai nayi sharr, tuni kuma tausayin 'yar uwata ya kamani ganin yadda take ta rawar jiki dani cike da kauna. Sai na ware nima muka shiga hirar arziki.
Duk sanda ta sako zancen Fa'iz cikin hirarmu bana yarda ince mata komai, dolenta ta kyale, muka koma hirar makaranta da dakace iri-iri na cewa yanzu an shiga zangon karatu na farko na sabuwar shekara babu mu, Haulatu na can tana ta (missing).
Ko da wasa Ummi bata yi zancen marigayi N.S ba, nima banyi ba. Na ce.
"Wai ina Yaya Bashir ne?"
Ta ce, "Ya koma Russia zai harhado kan takardunshi don na ce ni ban yarda yayi aiki a can ba, sai dai ya je, ni in zauna anan duk sanda ya samu dama ya neme ni, dalilin komawar shi amso takardun kenan ya dawo nan ya nemi aiki".
Nayi dariya na ce, "Kin hadu, wai kema mai tsarawa miji rayuwa ko?"
Ta ce, "Ba wani tsarin rayuwa ko dai gaskiya. Na rantse miki shashanci yake a can ba aikin da yake yi. Ya jima da gama karatu babu yadda Mama bata yi ba ya dawo yaki, wai jiran Yaya Fa'iz yake ya kammala da yake karatun Fa'iz yafi nashi nisa. Gara Fa'iz idan ya ce zai yi aiki a waje yana da hujja a Nigeria bamu da wasu Airlines na arziki, kuma ba zaki hada albashinsu da nagartarsu da 'Internationals’ ba.
Shi kuwa Yaya Bashir su Nigeria ke bukata suzo su amfanar da al'ummar su yafi, (Global; security) ya karanta.
Na samu da dabara da taimakon Allah da na addu'a na tsayar da hankalin Yaya Bashir a kaina, anan bai fita ko'ina sai tare da ni, don kar in zarge shi. Firinji kuwa (fridge) duk gidan daya ne na (kitchen) don kar ince yana boye (gulder) wani wuri. Don haka ko ya dawo ya samu aiki zan ci gaba da sa masa ido sosai duk da cewa na tabbata a yanzu yaya Bashir ya bar shashanci 90%".
Na jinjinawa Ummi a fili da zuci, kaga mace duk gabuntarta a fannin mu'amala da miji kada ka rainata. Ban taba zaton Ummi na da hankalin da yau na sameta da shi ba.
Na ce, "Bani abinci Ummi, yunwa nake ji, tun karin kumallon safe rabona da abinci, kin san kuma ba iya jure yunwa nake ba".
Ummi ta dafe kirji, kai Fa'izah, amma kin iya rashin mutunci, kin shagaltar dani ko ki tuna mani da dan uwa na dake waje cikin yara ko ruwa ban bashi ba, kanki kawai kika sani, (selfish!)".
Ummi ta fita falo da fara'arta sai taga wayam!
"Ku! Ina Yaya Fa'iz?"
Ta tambayi Walida.
"Ai tun dazu ya debi Shu'aib, Junior da Yahya suka wuce wai Zaria za su raka shi.
Haushi ya kashe Ummi ta harari Walida.
"Shi ne baku gaya min ba? Ban bashi ruwa ba, ban bashi abinci ba". Ta fada kamar ta fashe da kuka.
Abdallah ya ce, "Shi ne ya ce mu kyale ki hira ku ke, kun jima baku hadu ba. In ya dawo daukan Yaya Fa'izah gobe ko jibi kun gaisa".
Ba haka ta so ba, sai dai tayi farin cikin jin cewa ya bar mata 'yar uwarta barin rayuwarta su kwana su hantse tare, wani abu da suka rabu da samu tun barowar su Kano gidan Yaya Rabi.
Da kuzarinta ta fada (kitchen) don dora sanwar dare. Ta dawo ta ci gaba da yi min sababi, ta gaji ta koma wa'azi na hakkin miji akan matarsa da girmama shi da kula da cin shi da shansa da shimfidarsa. Amma ga mamakina na kasa tanka mata duk da nasan gaskiya take fada ban dai furta komai ba mai nuni da na amshi wa'azinta ko a'ah? Ba zata gane ba, ba zan iya bane, da zata gane ta adana yawun bakinta a gaba zai yi mata amfani, ta barni yadda ta ganni, rayuwata da tata ba zata taba zama daya ba.
[21/02 9:00 PM] Sumayya Takori: ZUMUNTAR KENAN?-4
Washegari da safe, mun karya kumallo cikin farin ciki, ni Ummi da ragowar kannen mu. Daga nan muka tare a falon Ummi muna hira muna shan dariya. Na mike na barsu nayi (toilet) din Ummi nayi wanka na sha kwalliya da daya daga cikin lesukan Ummi da ta ci biki dasu. Na dawo falon na cimma su kafin in zauna kararrawar kofar shigowa tayi kara. Sai na fasa zama a raina na ce bari in hutar da kowa. Na karasa a natse na bude kofar.
Wajejen karfe uku sai gamu cikin garin Kaduna. Ya karya kan motar ya dauki hanyar anguwar Kabala Custain. Ni sam bam ma san nan gidan Ummi yake ba. Yayi (parking) bayan maigadin gidan ya bude get din gaba daya. Su Yahya ne suka fito ashe duk suna gidan sunzo musu wuni, abin mamaki har da su Walida, Abdallah, Kausar da Walid autanmu. Nan gidan ya rude da sowar kannen mu kamar zasu hadiye mu.
A sannan ne na gane gidan Ummi da Yaya Bashir ne ganin tangamemen hoton su (window size) ranar (cocktail) din (Indoor sport hall) kafe a kayataccen falon.
Sai na wuce kai tsaye zuwa uwar dakin matar gidan babu wanda na kula a cikinsu sai cika nake ina batsewa. Na zauna a gefen gadonta ina kallon dakin kallon kurilla, na jiyo alamar tana (toilet) ne wanda ke makale da dakin nata tana wanka.
Ummi tunda taji ana oyoyo Yaya Fa'izah, oyoyo Yaya Fa'iz tayiwa wankan baja-baja ta fito a guje duk rabin jikinta kumfa ta fado mini.
Na ture ta na ce, "Ke baki da hankali ne za ki jikani? Don kawai nazo gidanki? Ba tambayar mutum ya yake? Ko wane hali yake ciki?"
Ta daga ni tana dariya, ta rasa inda zata sa kanta don farin ciki. Na bita da kallo har cikin ta ya tasa. Na kama baki cikin tsananin mamaki domin na dauka da da wasa take kamar a bakin kofa ake tuntube da cikin?
Ta sunkuya ta zauna a gefena hannuwanta duka biyu tallabe da fuskarta tana murmushi, ta ce.
"Fa'izah matar Yaya Fa'iz! Sai kyallin amarci kuke don na hango shi ta taga, daga ina kuke haka? Naji labarin Baba ya kore ku, tsammanin mu kun bar kasar babu sallama ga kowa".
Na hade girar sama da na kasa, na ce.
"Kin san Allah ki fita daga harkata, wane irin an kore ni kamar wata shegiya? Maras kunya fitsararriya, kyallin amarcin uban wa? Amarcin yaci ta kaza-kazan sa". Na mirgino ashariya.
Ummi ta dafe baki, sai kuma ta fashe da dariya.
"Oho dai! Mun gane kiyayya taci uwatar, Pilot yayi fari yayi kiba, Fa'izah ta rame saboda wuyar amarci amma ta zama kyakkyawa. Shin wai a ina aka yada zango ne?"
Ganin tana neman maishe ni mahaukaciya na mike nayi (toilet) don inyi wanka in sauya kunzugu na ko naji dadin jikina. Na fito daure da tawul tana make-up a (dressing mirrow) fuska kamar jikakken kwaki don turbunewa na ce.
"Bani kaya in sauya, ko ba hali?"
Tayi dariya kawai, ta dauko min atamfa Vlisko mai ruwan ganye mai karamin dinki na karba na saka nayi kwalliyata sosai nayi sharr, tuni kuma tausayin 'yar uwata ya kamani ganin yadda take ta rawar jiki dani cike da kauna. Sai na ware nima muka shiga hirar arziki.
Duk sanda ta sako zancen Fa'iz cikin hirarmu bana yarda ince mata komai, dolenta ta kyale, muka koma hirar makaranta da dakace iri-iri na cewa yanzu an shiga zangon karatu na farko na sabuwar shekara babu mu, Haulatu na can tana ta (missing).
Ko da wasa Ummi bata yi zancen marigayi N.S ba, nima banyi ba. Na ce.
"Wai ina Yaya Bashir ne?"
Ta ce, "Ya koma Russia zai harhado kan takardunshi don na ce ni ban yarda yayi aiki a can ba, sai dai ya je, ni in zauna anan duk sanda ya samu dama ya neme ni, dalilin komawar shi amso takardun kenan ya dawo nan ya nemi aiki".
Nayi dariya na ce, "Kin hadu, wai kema mai tsarawa miji rayuwa ko?"
Ta ce, "Ba wani tsarin rayuwa ko dai gaskiya. Na rantse miki shashanci yake a can ba aikin da yake yi. Ya jima da gama karatu babu yadda Mama bata yi ba ya dawo yaki, wai jiran Yaya Fa'iz yake ya kammala da yake karatun Fa'iz yafi nashi nisa. Gara Fa'iz idan ya ce zai yi aiki a waje yana da hujja a Nigeria bamu da wasu Airlines na arziki, kuma ba zaki hada albashinsu da nagartarsu da 'Internationals’ ba.
Shi kuwa Yaya Bashir su Nigeria ke bukata suzo su amfanar da al'ummar su yafi, (Global; security) ya karanta.
Na samu da dabara da taimakon Allah da na addu'a na tsayar da hankalin Yaya Bashir a kaina, anan bai fita ko'ina sai tare da ni, don kar in zarge shi. Firinji kuwa (fridge) duk gidan daya ne na (kitchen) don kar ince yana boye (gulder) wani wuri. Don haka ko ya dawo ya samu aiki zan ci gaba da sa masa ido sosai duk da cewa na tabbata a yanzu yaya Bashir ya bar shashanci 90%".
Na jinjinawa Ummi a fili da zuci, kaga mace duk gabuntarta a fannin mu'amala da miji kada ka rainata. Ban taba zaton Ummi na da hankalin da yau na sameta da shi ba.
Na ce, "Bani abinci Ummi, yunwa nake ji, tun karin kumallon safe rabona da abinci, kin san kuma ba iya jure yunwa nake ba".
Ummi ta dafe kirji, kai Fa'izah, amma kin iya rashin mutunci, kin shagaltar dani ko ki tuna mani da dan uwa na dake waje cikin yara ko ruwa ban bashi ba, kanki kawai kika sani, (selfish!)".
Ummi ta fita falo da fara'arta sai taga wayam!
"Ku! Ina Yaya Fa'iz?"
Ta tambayi Walida.
"Ai tun dazu ya debi Shu'aib, Junior da Yahya suka wuce wai Zaria za su raka shi.
Haushi ya kashe Ummi ta harari Walida.
"Shi ne baku gaya min ba? Ban bashi ruwa ba, ban bashi abinci ba". Ta fada kamar ta fashe da kuka.
Abdallah ya ce, "Shi ne ya ce mu kyale ki hira ku ke, kun jima baku hadu ba. In ya dawo daukan Yaya Fa'izah gobe ko jibi kun gaisa".
Ba haka ta so ba, sai dai tayi farin cikin jin cewa ya bar mata 'yar uwarta barin rayuwarta su kwana su hantse tare, wani abu da suka rabu da samu tun barowar su Kano gidan Yaya Rabi.
Da kuzarinta ta fada (kitchen) don dora sanwar dare. Ta dawo ta ci gaba da yi min sababi, ta gaji ta koma wa'azi na hakkin miji akan matarsa da girmama shi da kula da cin shi da shansa da shimfidarsa. Amma ga mamakina na kasa tanka mata duk da nasan gaskiya take fada ban dai furta komai ba mai nuni da na amshi wa'azinta ko a'ah? Ba zata gane ba, ba zan iya bane, da zata gane ta adana yawun bakinta a gaba zai yi mata amfani, ta barni yadda ta ganni, rayuwata da tata ba zata taba zama daya ba.
[21/02 9:00 PM] Sumayya Takori: ZUMUNTAR KENAN?-4
Washegari da safe, mun karya kumallo cikin farin ciki, ni Ummi da ragowar kannen mu. Daga nan muka tare a falon Ummi muna hira muna shan dariya. Na mike na barsu nayi (toilet) din Ummi nayi wanka na sha kwalliya da daya daga cikin lesukan Ummi da ta ci biki dasu. Na dawo falon na cimma su kafin in zauna kararrawar kofar shigowa tayi kara. Sai na fasa zama a raina na ce bari in hutar da kowa. Na karasa a natse na bude kofar.