Sashe 68
Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read
A firgice na cira kai na dubi Baba. Kuka nake har naji babu dadi, na gyara dankwalina, bana ko batun takalmi balle mayafi, tuni na riga Fa'iz kaiwa bakin mota, na bude baya na shige. Na kifa kaina jikin kujerar gaba ina rusa kuka na gani kasheni!
A can cikin gida kuwa gardama ce tsakanin Fa'iz da Baba. Ya ce shi ba zai tafi dani ba a yanzun ya fasa. Ayi duba da halin da nake ciki. Wane farin ciki zai tsinta a tare dani?"
Baban ya ce, "To Fa'iz in ka saki auren ne kamar yadda take so ka bani takarda wadda zan nunawa Hajjah da sauran dangi Fa'iza tayi zama mai dalili a gidana, domin Hajjah har ta fara nuna fushinta da zaman Fa'izah tare da mu bamu mikata Kaduna ba. In kuma kana aure, to Fa'izah bata kara zamar min gida ta kara kwana daga yau. In baka tafiya da ita inda kake kasan inda zaka ajeta amma ba dai gidana ba!
Yarinya daya tal na neman zautar dani kamar ita kadai na haifa? Na gaji wallahi".
Fa'iz ya sake kwantar da murya ya ce, "Baba Fa'izah ta rantse ba zata zauna dani ba. Ta yaya zan kaita inda ake ganin mutunci na ake girmamani ta dizgani ko ta rufe ni da duka don Allah Baba? Ni kam a kyale Fa'izah, ayi mata addu'a ta samu saukin bacin ranta kafin mu tafi. Amma bai dace in tafi da ita cikin wannan hali ba".
Baba ya ce, "Na gama maganar nan Fa'izu, Fa'izah ba zata sake kwana mini cikin gida ba sai in baka aure. To wannan kuwa, bani da yadda zanyi da ita".
Fa'iz ya fice fuuu shima nashi ran a bace. Ba haushin Baba yake ji ba, zuciya yayi mai cewa ya yiwa Fa'izah duk abinda take so don a zauna lafiya. Kamar yadda Baba ya gaji shima ya gaji. In so cuta ne to hakuri ma magani ne. Bai taba ganin yarinya mai taurin kai da taurin zuciyar Fa'izah ba da kullaci wanda baya jin lallashi.
Ya bude kofar motar ya shiga ya zauna, har ya tayar da ita ya juyo yaga ban rufe kofar ba. Ya fito yazo ya rufe ya sake ta da motar aguje, ban san inda ya nufa ba sai dai jikina ya bani ba Kano bane, ba Kaduna bane. Ya manta shaf da Shu'aib dan rakiyarsa. Shima Shu'aib din yana kallon mu muka fita bai yi gigin binmu ba.
Nayi kuka nayi kuka har na gode Allah, na kuma ba uku lada. Hawaye sun kafe, murya ta dishe, haka idanuna sunyi luhu-luhu. Don haka nayi shiru na zubawa sarautar Allah ido ta hanyar kurawa tsirrai halittar Ubangiji ido dake giftamu aguje suna tsere da junansu (bishiyoyi da dazuzzuka). Ko ma mahalaka Fa'iz zai kaimu, a wannan lokacin ban damu ba. Domin na fidda rai da rayuwar farin ciki tunda iyayena da suka haifeni ma basa so na, na kuma tsani rayuwar ita kanta muddin tare da Fa'iz zan yi ta. Na kuma tsani wani abu wai shi farin ciki ya sake ratsowa cikin rayuwata..
A can cikin gida kuwa gardama ce tsakanin Fa'iz da Baba. Ya ce shi ba zai tafi dani ba a yanzun ya fasa. Ayi duba da halin da nake ciki. Wane farin ciki zai tsinta a tare dani?"
Baban ya ce, "To Fa'iz in ka saki auren ne kamar yadda take so ka bani takarda wadda zan nunawa Hajjah da sauran dangi Fa'iza tayi zama mai dalili a gidana, domin Hajjah har ta fara nuna fushinta da zaman Fa'izah tare da mu bamu mikata Kaduna ba. In kuma kana aure, to Fa'izah bata kara zamar min gida ta kara kwana daga yau. In baka tafiya da ita inda kake kasan inda zaka ajeta amma ba dai gidana ba!
Yarinya daya tal na neman zautar dani kamar ita kadai na haifa? Na gaji wallahi".
Fa'iz ya sake kwantar da murya ya ce, "Baba Fa'izah ta rantse ba zata zauna dani ba. Ta yaya zan kaita inda ake ganin mutunci na ake girmamani ta dizgani ko ta rufe ni da duka don Allah Baba? Ni kam a kyale Fa'izah, ayi mata addu'a ta samu saukin bacin ranta kafin mu tafi. Amma bai dace in tafi da ita cikin wannan hali ba".
Baba ya ce, "Na gama maganar nan Fa'izu, Fa'izah ba zata sake kwana mini cikin gida ba sai in baka aure. To wannan kuwa, bani da yadda zanyi da ita".
Fa'iz ya fice fuuu shima nashi ran a bace. Ba haushin Baba yake ji ba, zuciya yayi mai cewa ya yiwa Fa'izah duk abinda take so don a zauna lafiya. Kamar yadda Baba ya gaji shima ya gaji. In so cuta ne to hakuri ma magani ne. Bai taba ganin yarinya mai taurin kai da taurin zuciyar Fa'izah ba da kullaci wanda baya jin lallashi.
Ya bude kofar motar ya shiga ya zauna, har ya tayar da ita ya juyo yaga ban rufe kofar ba. Ya fito yazo ya rufe ya sake ta da motar aguje, ban san inda ya nufa ba sai dai jikina ya bani ba Kano bane, ba Kaduna bane. Ya manta shaf da Shu'aib dan rakiyarsa. Shima Shu'aib din yana kallon mu muka fita bai yi gigin binmu ba.
Nayi kuka nayi kuka har na gode Allah, na kuma ba uku lada. Hawaye sun kafe, murya ta dishe, haka idanuna sunyi luhu-luhu. Don haka nayi shiru na zubawa sarautar Allah ido ta hanyar kurawa tsirrai halittar Ubangiji ido dake giftamu aguje suna tsere da junansu (bishiyoyi da dazuzzuka). Ko ma mahalaka Fa'iz zai kaimu, a wannan lokacin ban damu ba. Domin na fidda rai da rayuwar farin ciki tunda iyayena da suka haifeni ma basa so na, na kuma tsani rayuwar ita kanta muddin tare da Fa'iz zan yi ta. Na kuma tsani wani abu wai shi farin ciki ya sake ratsowa cikin rayuwata..