Sashe 15
Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
*****
Washe gari muna gidan Baba Na’ibi (gidan su Yaya Aliyu) muna kallon wani wasan kwaikwayo na ANTAR-BN-SHADDAD da ABLAH, domin mu zuri’armu kaf daga shekara kasa da sha takwas, ba a kallon finafinan Turawa, na Hausa ko na India, ko na ‘yan kudu (Nigerian Film), sai hikayoyi na Larabci da Risalah, ko tarihin Sahabbai da ake yi a matsayin film kamar na Khulafa’ur-Rashidun.
Domin wannan finafinai da na zayyano a sama a ganin Hajjah duk nau’i ne na illata tarbiyyar yara da hana su mai da hankali ga karatu. Daga na yake-yaken Larabci (Adventure) sai zaluncin da Isra’el ke yiwa ‘yan’uwa musulmi na yankin Gaza, sai Islamic Channel wadanda suke nuna halin da kasashe marasa karfi ke ciki, irin su Somalia da irin tallafin da NGO’s suke yi musu, irin su ‘Human Appeal Organization’ masu daukar nauyin irin wadannan kasashe ta hanyar abinci, ilimi, asibiti da tufafi.
Wadannan al’umma masu ban tausayi abubuwa ne dake karawa yara imani da wadatar zuci. Sai ko labaran Larabci na Al-jazeera, CNN, BBC. Saboda yawan kallon al’amuran Larabawa da nake, da sauran labaran Larabci da kallon rayuwarsu a talabijin, dadin-dadawa ana yin Larabci as (Subject) a ajinmu, sai ya kasance na iya Larabci sosai, kuma shine harshe mafi soyuwa a gare ni tun ina (Area One). Tun ina karama Allah ya dora min kaunar Alifun-Ba’un, Alifun-Arnabun, Ba’un-Baqaratun.
Maryam ta dube ni muna cikin kallon ta ce, “Wai me Antaru ya ce kenan Fa’izah?’ Na fassara mata, ban ida rufe bakina ba Yaya Aliyu ya shigo.
Ya samu gefen mahaifiyarshi ya zauna, ta ce, “Ya ya dai Yayansu? Na ganka rather moody? In ce ko ka dauki abincinka ka ci?”
Ya dan yi tsaki ya ce, “Mama na sha kunun alkama fa a wurin Hajjah yanzun nan”.
Ta dube shi tsaf, cikin babbar murya ta ce, “Aliyu!” Da hanzari ya dago ya dube ta.
“Na gaji kullum magana daya ta ki ci ta ki cinyewa. Yanzu kamar kai Aliyu sai an rarrasheka ka ci abinci za ka ci, sai ka ce wani karamin yaro, da gangan kake wasa da lafiyarka, to na daina, sai dai ka kashe kanka kai kadai, wallahi ka kwanta ciwo ko hanyar asibiti ba za ka ganni ba. Ko da yake in ka kashe kanka ai kai ka jiyo, wa ka yiwa asara?”
Na juyo daga kallon T.V na ce, “Mama mu mana? Mu aka yiwa asara”.
Zanirah ma ta ce, “Tabbas mu ya yiwa asara, we cannot, never found a caring brother like him, Yaya Aliyo don Allah daure ka dinga cin abinci in ka mutu mun shiga uku”.
Na ce, “Mun shiga uku ko mun shiga tara?”
Ummi ta ce, “Har mun lalace”.
Zanirah ce ta mike ta yi kitchen da zafin namanta, ta shako plate da dankali soyayye da murtukekn kwai, ta zo ta zauna tsakanin Mama da Yaya Aliyu kasancewar suna zaune kujera daya ne mai cin mutum uku.
Cike da kulawa ta mika mishi, kana cikin muryar lallashi da kulawa ga karamin yaro in ya ki cin abinci ta ce, “Yaya Aliyu don Allah ka ci”.
Gaba daya aka kwashe da dariya har Maman dake bambamin fada, babu shakka yadda muke kula da Yaya Aliyu da hidimarsa, da yadda shima yake kula damu da al’amuranmu, yana yi mata dadi, don ko Maryam da suke ciki daya ba ta kulawa da al’amarinsa kamar yadda muke masa, haka shima.
Ga shi tana masifar son Yaya Aliyu kamar ba dan fari ba. Ita cikakkiyar lauya ce mai zaman kanta, sam ba ta irin kawaicin Momina, mu’amalarta da Yaya Aliyu kamar ta Yaya da kaninta mai binta da suka fito ciki daya. Hakan ba karamin bani sha’awa yake ba, in yi ta dakacen ina-ma a ce nice.
Na taso tsam daga inda nake zaune zuwa garesu na ce, “Mama tashi ki bamu fili in bai ci ba dura zamu yi masa”.
Ita da Yaya Aliyu suka sa dariya, ta ce, “Lallai kam ‘yammatan Hajjah kadan daga aikin ku, kuma aikinku yana kyau, Allah ka bani tsawon ran da zan ga da wacce za ayi tsakanin ke, Ummi da Zanirah.....”
A hargitse Yaya Aliyu ya yi ma Mama gyaran murya ga alama bai ji dadin abin da ta fada a gabanmu ba. Ta mike ta bar mana falon tana dariya tana fadin “Sannu-sannu ba ta hana zuwa sai dai a dade ba a je ba”. Sai da muka tilastawa Yaya Aliyu ya cinye abincin nan tas, sannan muka kyale shi.
Ya ce, “Ummi ban ji yadda aka riski Queen Amina ba?” Ta ce, “Tambayi gimbiyar taka mana ni ai baka yi dani Yaya Aliyu, ka kawo mata nama, Zanirah pack din Bounty, amma ni ko sannu don ni lukuta ce tun ranar da ka fada Zanirah ke tsokanata ba a yayin lokutayen mata”.
Ya murmusa a hankali, ya fiddo pack din kit-kat a aljihunsa ya cillawa Ummi. Ta dauke tana dariya tana godiya, ya ce, “Saboda Allah Zanira ina ruwan ki cikin wannan maganar har da kike tada ta bana nan?”
Ta ce, “Rabu da ita Yaya Aliyu, ita ta fara ce min mai wuya uwa marikin lema, an fada din, ba a yayin lukataye sai ‘slim’ din ki yi duk abin da za ki yi”.
Ya fiddo mata ido ya ce, “Kada na kara jin irin wannan maganar, babu kyau gorin halitta Zanirah, kada na kara ji”.
Ummi ta ce, “Rabu da ita Yaya Aliyi, so take jikinta ya gaya mata ta ga ranar lukutin jiki, sai shegen cika bakin tsiya babu kwanji, don ta ji Hajjah na cewa ta girmemu to ba shekaru biyu ba ko goma kika bani in kika kara ce min lukuta lallasaki zan yi”.
Yaya Aliyu ya rasa inda zai sa kansa don dariya, ya ce, “Ana girma ana cin kasa Ummi da Zanirah! Inda Fa’izah ke burgeni kenan, tunda kuka shiga aji hudu ta watsar da shirme ta bar muku”.
Ummi ta ce, “Eh, ai daman a wajenka Yaya Aliyu Fa’iza ba ta laifi, ita ce ta iya komai, bayan ita din a bayan idonka tantiriyar kanta ce”.
Yana dariya ya ce, “Bakya son a fadi gaskiya, amma Fa’izah ta fiku hankali, nutsuwa da kamewa. Ko zaman wuni guda mutum ya yi daku zai fuskanci haka”.
Ummi ta sake kuluwa, ta tashi faram-faram ta fice. Yana kiranta yana ba ta hakuri amma ba ta juyo ba. Zanirah ko a jikinta, daman ita yarinya ce mai matukar sanyi cikin al’amuranta ba ta da fushi, ba ta da daukar zafi ko kadan a kan duk abin da za ka yi mata, da wuya ka ga bacin ranta. Kullum fuskarta cikin annuri take, ita dai barta a cika baki da kokarin karatu kamar Alhuda-Huda.
Ya maido duban shi gare ni ya ce, “Fa’izah ba a bani labarin Sarauniya Amina ba”. Na ce, “To Yaya Aliyu me zan ce maka ga yara duk sun zubo min ido?”
Maryam ta ce, “Lallai ma, su waye yaran naki?” Na ce, “Gaku nan mana juniors ‘yan JSS”. Ta ce, “Mts! Ke har yaushe kika fara SS din da za ki raina mutane?”
Yaya Aliyu ya ce, “Ke rufe mana baki ko na hambareki, wa ya sako ki cikin zancen nan? Ko sa’arki ce?” Na faki idonsa na yi mata gwalo, ta dalla min harara.
“Maza dauko biro da takarda ta rubuta min labarin Queen Amina”.
Zanirah ta ce, “Ba za ta iya ba Yaya Aliyu, ba ta iya Turanci sosai ba”.
Ya ce, “Da kowacce luggah Fa’izah rubuta min labarin Queen Amina, be it Hausa, Arabic, English, Fulfulde, Kanuri, Yoruba or Igbo, in har kika rubuta am sure zan iya karantawa in fahimta”.
Da karsashi na karbi takardar da biro, na matsa nesa dasu na soma yarfawa Yaya Aliyu kyawawan rubutu da harshen Larabci tsaftatacce. Na mika masa ya shiga karanta musu a fili, ga fassarar abin da na rubuta.
“Yaya Aliyu mun je Queen Amina lafiya, makarantar Sarauniya Amina babbar makaranta ce mai kyawun tsari, tsohuwa mai tsohon tarihi. Malamansu da dalibai duka masu kwazo ne. Bamu da kawaye, amma muna gaisuwar musulunci da duk wanda wata mu’amala ta hadamu da shi. An kai ni ajin Arabic, an kai Ummi ajin zane-zane (Art) saboda shi ta fi iyawa.
Akwai club-club a Queen Amina, irin su Maths Club, English Club, Jet Club, Arabic Club, Hausa Club, Science da sauran su. Na raba kafa na shiga Clubs har guda biyu, wato Arabiyya da English Clubs, Ummi ta shiga Jet don Allah bai halicce ta da kwakwalwar rike karatu ba, Jet kuma ana koyar da sana’o’in gida ga dalibai ne.
Aunty Hauwa ba ta kulamu ba ta neman mu, ta ce don ita muka dawo Queen Amina, don haka ba ruwanta damu mu manta mun santa, ba abin da take kawo mana daga gidanta ta ce mu karata”.
Nice Kanwarka.
Fa’izah A.A Giwa.
Yaya Aliyu ya ajiye takardar ya ce, “Good, very good, a tafawa Fa’iza, na ce a tafa mata!” Raf! Raf!! Raf!!! Suka hau tafi. Ya yin da Yaya Aliyu ya shiga manna min sababbin wa-zo-bia a goshina har guda shida.
Washe gari muna gidan Baba Na’ibi (gidan su Yaya Aliyu) muna kallon wani wasan kwaikwayo na ANTAR-BN-SHADDAD da ABLAH, domin mu zuri’armu kaf daga shekara kasa da sha takwas, ba a kallon finafinan Turawa, na Hausa ko na India, ko na ‘yan kudu (Nigerian Film), sai hikayoyi na Larabci da Risalah, ko tarihin Sahabbai da ake yi a matsayin film kamar na Khulafa’ur-Rashidun.
Domin wannan finafinai da na zayyano a sama a ganin Hajjah duk nau’i ne na illata tarbiyyar yara da hana su mai da hankali ga karatu. Daga na yake-yaken Larabci (Adventure) sai zaluncin da Isra’el ke yiwa ‘yan’uwa musulmi na yankin Gaza, sai Islamic Channel wadanda suke nuna halin da kasashe marasa karfi ke ciki, irin su Somalia da irin tallafin da NGO’s suke yi musu, irin su ‘Human Appeal Organization’ masu daukar nauyin irin wadannan kasashe ta hanyar abinci, ilimi, asibiti da tufafi.
Wadannan al’umma masu ban tausayi abubuwa ne dake karawa yara imani da wadatar zuci. Sai ko labaran Larabci na Al-jazeera, CNN, BBC. Saboda yawan kallon al’amuran Larabawa da nake, da sauran labaran Larabci da kallon rayuwarsu a talabijin, dadin-dadawa ana yin Larabci as (Subject) a ajinmu, sai ya kasance na iya Larabci sosai, kuma shine harshe mafi soyuwa a gare ni tun ina (Area One). Tun ina karama Allah ya dora min kaunar Alifun-Ba’un, Alifun-Arnabun, Ba’un-Baqaratun.
Maryam ta dube ni muna cikin kallon ta ce, “Wai me Antaru ya ce kenan Fa’izah?’ Na fassara mata, ban ida rufe bakina ba Yaya Aliyu ya shigo.
Ya samu gefen mahaifiyarshi ya zauna, ta ce, “Ya ya dai Yayansu? Na ganka rather moody? In ce ko ka dauki abincinka ka ci?”
Ya dan yi tsaki ya ce, “Mama na sha kunun alkama fa a wurin Hajjah yanzun nan”.
Ta dube shi tsaf, cikin babbar murya ta ce, “Aliyu!” Da hanzari ya dago ya dube ta.
“Na gaji kullum magana daya ta ki ci ta ki cinyewa. Yanzu kamar kai Aliyu sai an rarrasheka ka ci abinci za ka ci, sai ka ce wani karamin yaro, da gangan kake wasa da lafiyarka, to na daina, sai dai ka kashe kanka kai kadai, wallahi ka kwanta ciwo ko hanyar asibiti ba za ka ganni ba. Ko da yake in ka kashe kanka ai kai ka jiyo, wa ka yiwa asara?”
Na juyo daga kallon T.V na ce, “Mama mu mana? Mu aka yiwa asara”.
Zanirah ma ta ce, “Tabbas mu ya yiwa asara, we cannot, never found a caring brother like him, Yaya Aliyo don Allah daure ka dinga cin abinci in ka mutu mun shiga uku”.
Na ce, “Mun shiga uku ko mun shiga tara?”
Ummi ta ce, “Har mun lalace”.
Zanirah ce ta mike ta yi kitchen da zafin namanta, ta shako plate da dankali soyayye da murtukekn kwai, ta zo ta zauna tsakanin Mama da Yaya Aliyu kasancewar suna zaune kujera daya ne mai cin mutum uku.
Cike da kulawa ta mika mishi, kana cikin muryar lallashi da kulawa ga karamin yaro in ya ki cin abinci ta ce, “Yaya Aliyu don Allah ka ci”.
Gaba daya aka kwashe da dariya har Maman dake bambamin fada, babu shakka yadda muke kula da Yaya Aliyu da hidimarsa, da yadda shima yake kula damu da al’amuranmu, yana yi mata dadi, don ko Maryam da suke ciki daya ba ta kulawa da al’amarinsa kamar yadda muke masa, haka shima.
Ga shi tana masifar son Yaya Aliyu kamar ba dan fari ba. Ita cikakkiyar lauya ce mai zaman kanta, sam ba ta irin kawaicin Momina, mu’amalarta da Yaya Aliyu kamar ta Yaya da kaninta mai binta da suka fito ciki daya. Hakan ba karamin bani sha’awa yake ba, in yi ta dakacen ina-ma a ce nice.
Na taso tsam daga inda nake zaune zuwa garesu na ce, “Mama tashi ki bamu fili in bai ci ba dura zamu yi masa”.
Ita da Yaya Aliyu suka sa dariya, ta ce, “Lallai kam ‘yammatan Hajjah kadan daga aikin ku, kuma aikinku yana kyau, Allah ka bani tsawon ran da zan ga da wacce za ayi tsakanin ke, Ummi da Zanirah.....”
A hargitse Yaya Aliyu ya yi ma Mama gyaran murya ga alama bai ji dadin abin da ta fada a gabanmu ba. Ta mike ta bar mana falon tana dariya tana fadin “Sannu-sannu ba ta hana zuwa sai dai a dade ba a je ba”. Sai da muka tilastawa Yaya Aliyu ya cinye abincin nan tas, sannan muka kyale shi.
Ya ce, “Ummi ban ji yadda aka riski Queen Amina ba?” Ta ce, “Tambayi gimbiyar taka mana ni ai baka yi dani Yaya Aliyu, ka kawo mata nama, Zanirah pack din Bounty, amma ni ko sannu don ni lukuta ce tun ranar da ka fada Zanirah ke tsokanata ba a yayin lokutayen mata”.
Ya murmusa a hankali, ya fiddo pack din kit-kat a aljihunsa ya cillawa Ummi. Ta dauke tana dariya tana godiya, ya ce, “Saboda Allah Zanira ina ruwan ki cikin wannan maganar har da kike tada ta bana nan?”
Ta ce, “Rabu da ita Yaya Aliyu, ita ta fara ce min mai wuya uwa marikin lema, an fada din, ba a yayin lukataye sai ‘slim’ din ki yi duk abin da za ki yi”.
Ya fiddo mata ido ya ce, “Kada na kara jin irin wannan maganar, babu kyau gorin halitta Zanirah, kada na kara ji”.
Ummi ta ce, “Rabu da ita Yaya Aliyi, so take jikinta ya gaya mata ta ga ranar lukutin jiki, sai shegen cika bakin tsiya babu kwanji, don ta ji Hajjah na cewa ta girmemu to ba shekaru biyu ba ko goma kika bani in kika kara ce min lukuta lallasaki zan yi”.
Yaya Aliyu ya rasa inda zai sa kansa don dariya, ya ce, “Ana girma ana cin kasa Ummi da Zanirah! Inda Fa’izah ke burgeni kenan, tunda kuka shiga aji hudu ta watsar da shirme ta bar muku”.
Ummi ta ce, “Eh, ai daman a wajenka Yaya Aliyu Fa’iza ba ta laifi, ita ce ta iya komai, bayan ita din a bayan idonka tantiriyar kanta ce”.
Yana dariya ya ce, “Bakya son a fadi gaskiya, amma Fa’izah ta fiku hankali, nutsuwa da kamewa. Ko zaman wuni guda mutum ya yi daku zai fuskanci haka”.
Ummi ta sake kuluwa, ta tashi faram-faram ta fice. Yana kiranta yana ba ta hakuri amma ba ta juyo ba. Zanirah ko a jikinta, daman ita yarinya ce mai matukar sanyi cikin al’amuranta ba ta da fushi, ba ta da daukar zafi ko kadan a kan duk abin da za ka yi mata, da wuya ka ga bacin ranta. Kullum fuskarta cikin annuri take, ita dai barta a cika baki da kokarin karatu kamar Alhuda-Huda.
Ya maido duban shi gare ni ya ce, “Fa’izah ba a bani labarin Sarauniya Amina ba”. Na ce, “To Yaya Aliyu me zan ce maka ga yara duk sun zubo min ido?”
Maryam ta ce, “Lallai ma, su waye yaran naki?” Na ce, “Gaku nan mana juniors ‘yan JSS”. Ta ce, “Mts! Ke har yaushe kika fara SS din da za ki raina mutane?”
Yaya Aliyu ya ce, “Ke rufe mana baki ko na hambareki, wa ya sako ki cikin zancen nan? Ko sa’arki ce?” Na faki idonsa na yi mata gwalo, ta dalla min harara.
“Maza dauko biro da takarda ta rubuta min labarin Queen Amina”.
Zanirah ta ce, “Ba za ta iya ba Yaya Aliyu, ba ta iya Turanci sosai ba”.
Ya ce, “Da kowacce luggah Fa’izah rubuta min labarin Queen Amina, be it Hausa, Arabic, English, Fulfulde, Kanuri, Yoruba or Igbo, in har kika rubuta am sure zan iya karantawa in fahimta”.
Da karsashi na karbi takardar da biro, na matsa nesa dasu na soma yarfawa Yaya Aliyu kyawawan rubutu da harshen Larabci tsaftatacce. Na mika masa ya shiga karanta musu a fili, ga fassarar abin da na rubuta.
“Yaya Aliyu mun je Queen Amina lafiya, makarantar Sarauniya Amina babbar makaranta ce mai kyawun tsari, tsohuwa mai tsohon tarihi. Malamansu da dalibai duka masu kwazo ne. Bamu da kawaye, amma muna gaisuwar musulunci da duk wanda wata mu’amala ta hadamu da shi. An kai ni ajin Arabic, an kai Ummi ajin zane-zane (Art) saboda shi ta fi iyawa.
Akwai club-club a Queen Amina, irin su Maths Club, English Club, Jet Club, Arabic Club, Hausa Club, Science da sauran su. Na raba kafa na shiga Clubs har guda biyu, wato Arabiyya da English Clubs, Ummi ta shiga Jet don Allah bai halicce ta da kwakwalwar rike karatu ba, Jet kuma ana koyar da sana’o’in gida ga dalibai ne.
Aunty Hauwa ba ta kulamu ba ta neman mu, ta ce don ita muka dawo Queen Amina, don haka ba ruwanta damu mu manta mun santa, ba abin da take kawo mana daga gidanta ta ce mu karata”.
Nice Kanwarka.
Fa’izah A.A Giwa.
Yaya Aliyu ya ajiye takardar ya ce, “Good, very good, a tafawa Fa’iza, na ce a tafa mata!” Raf! Raf!! Raf!!! Suka hau tafi. Ya yin da Yaya Aliyu ya shiga manna min sababbin wa-zo-bia a goshina har guda shida.