Sashe 29
Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
****
To Ali kam ya nuna ya haifu cikin uwarshi Zainabu, da ubanshi Na’ibi, kuma mai son farin cikin Fa’izah. A washegari ya dawo Giwa, inda ya saki kudi aka yi shagulgulan al’adarmu namu na Mallawa. Ya nuna tamkar komi bai faru ba, kamar Zanirah zabin shi ce ba zabin iyaye ba.
Amma zuciyar ta fi duhun dare duhu. Babu yadda ya iya fadan da ya fi karfin ka aka ce sai ka mai da shi wasa. Iyayen nan bashi da saman su, Hajjar nan ta fi karfin komi a garemu in har muna da iko, in har bamu da shi, zamu yi iya kokarinmu mu nemo masu shi suyi mata.
Sai dai abu ne da har illa masha Allahu ba zai taba kankaruwa daga zuciyarsa ba wato SON FA’IZAH! In ka ga ramar da Yaya Aliyu ya yi kamar wanda ya taso daga gadon asibiti bayan doguwar jinya. Jirgin karfe taran dare aka ajiye za su bi zuwa Lagos.
Aliyu ya dubi Hajjah ya ce, “Tunda har anyi mai wuyar Hajjah, ba a bari in koma ni kadai in shirya in dawo in dauke ta? In gyara muhallina daga na saurayi zuwa na mai iyali. Saurin da gaggawar na mene ne? Cikin abokan aikina duka babu wanda na sanar mawa na yi aure kawai sai a ganni da mata kamar na sato ta? Yanzu haka a tsakiyar aiki nake zuwa Ibadan a bani lokaci ko da sati daya ne in je in dawo don Allah.....”
Hajjah goyon Mahillah diyar Baba Barau take a bayanta ba ta ko dube shi ba. Ta sunkuci fidarta dake shake da cereal ta yi daki tana bambamin fada har da kumfar baki. Ta ce, “Karewar gyaran gida mai da gidan fadar shugaban kasa. Karewar rashin so Aliyu sayar da kan Zanirah garin Yarabawa. Amma kafarka-kafar Zannura”.
Aliyu ya yi tsit! Na fashe da dariya, Zanirah ko tsabar takaicin yadda Hajja ke mai da ta matar cushe kamar jakar da ta rasa miji na san shi yasa ta zub da kwalla.
Kamar za ta fashe da kuka ta ce, “Ni dai gaskiya Hajjah ki daina ce mun Zannura.....”
Hajjah ta ce, “Zannuraini an fada, ainahin sunanki kenan (ma’abociyar haske biyu)”.
Zanirah ta zumburi baki ta ce, “Hajjah Zunnuraini sunan namiji ne (Usman kenan)”.
Hajjah ta ce, “Allah ya bamu albarkacinsa. Abin da yasa na saka miki suna Zannura saboda an haife ki Ranar Arfah, kuma kwanan watan ya yi daidai da ranar da Najeriya ta karbi ‘yancin kanta daga hannun Turawa, ga ki fara kal kamar auduga, ga kyau ga kyan hali. In baka so Zanirah ba ina jin babu zuciya da mazantaka a tare da kai”.
Kalaman Hajjah sun girmi kunnuwan dukkanninmu daya bayan daya muka zame kowa ya bi hanya daban mai billar da shi wani sashe na gidan. Yaya Aliyu kuwa tunda ta dauko bayanin asalin sunan Zanirah ya bar dakin don haushi.
Ta fannina nima na nuna ni ‘yar halas ce, nayi ma Zanirah gudunmmuwar (kayan amfanin kitchen) masu karko da tsada ‘yan Japan. Turare mai tsada ‘versace’ da ‘hugo boss’ na ango Yaya Aliyu, na ce, “A sha kamshin amarci lafiya Aliyu da Zanirah”.
Sai a wannan lokacin ne Yaya Aliyu ya dago ido ya dube ni da wata muguwar harara da ban tsammana ba. Zanirah dake gefen shi cikin farin (swiss lace) mara nauyi mai yarfin (silver) dinkin buba da zani, kunshi baki sidik ya kama tafukan hannaye da kafafunta. Gashin nan ya sha relaxing ya kara baki ya kwanta a dogon wuyanta, amarya dai sak!
Ta dago kanta a hankali daga kan yatsun kafarta ‘yan sirara itama ta harare ni. Ga mamakinmu duka sai cewa ta yi, “Wanea irin amarci kike fade Fa’izah? A ya yin da zuciyoyi biyu basu dai-daita da juna ba? Auren da ake lallashi da takurawa mijin ya so ka, shi kike ambatawa amarci Fa’izah? Kaico da auren da ake roko da lallashin mijin ya dauki amaryar yana gudu.
ZAMANI YA CHANZA, ya kamata iyaye da kakanni irin Hajjah su gane hakan, su ajiye traditionality su bi modernity in dai ba fadar Allah da manzo bane. Domin maimakon a gyara zumuncin sai a bata, ko a zalinci daya a kasa kwatar masa hakkinsa don a dorar da zumunci”.
Ta mike ta yi waje tana mai fidda zafafan hawaye. Na kasa cewa komi sabanin Yaya Aliyu da ya kyabe baki ya gyara kwanciyar sa cikin kujera. Tsam! Nima na mike na bar wurin. Ummi ta bimu da kallon tausayi baki dayanmu.
Karfe shida saura minti talatin, iyakar rakiyar mu dasu Zanirah filin jirgin saman Kaduna, inda suka hau jirgi mai zuwa Legas.
Sai a wannan lokacin ne zuciyata ta soma turiri, tana kurma ihun yarda da zancen Zanirah ZAMANI YA CHANZA.... ya kamata Hajjah da ire-irenta su ajiye traditional false beliefs su yarda love is a natural nature that cannot be totally eradicated. Yanzu ne na tabbatar na rasa Aliyu har abada! A lokacin da tayoyin jirginsu suka rabu da kasa. Sai na fashe da kuka a lokacin da wani bakon tunani ya bakunce ni, wato yanayin idanun Zanirah (oily eyes).
Sau da dama Yaya Aliyu kan ce “Fa’izah ina ma kema irin kwayar idon Zanirah gare ki? Wallahi da na ji dadi na.....”
Hawayena suka sake ninka na da.... Ga Zanirah nan complete din ta ka samu Aliyu. Hawaye na ya sake ninka na da, na kifa kaina a kafadar Ummi muka ci gaba da kukan tare. Inda wanda ya san sirrin son da nake wa Yaya Aliyu, to Ummi ce, don tare muka rayuwa a makaranta fiye da Zanirah dake Giwa a lokacin da muka mallaki hankalin kanmu.
Babu irin tsarin da ban yiwa rayuwar aure na da Yaya Aliyu ba. Yadda za ta kasance, yadda zamu yi ta, yadda zamu gudanar da ita da yadda zamu tafiyar da ita, amma a yau Hajjah and her false beliefs (a ganina) sun rushe komai.
Lokaci guda wata irin sabuwar zuciya ta shige ni mai dauke da sabon perception. Na san dadin ‘So”, haka na san dacin rasa shi. In Allah ya yarda ba zan yarda in auri wanda bana so ba! Ba zan yi auren zumuncin ba, ba zan yi auren A.B Family ba. Zan zamo mutum ta farko da za ta canza A.B Family, zan zamo mutum ta farko da za ta yi auren soyayya a cikin zuri’ar Abubakar Bamalli Giwa.
Bare zan aura wanda zuciya da ruhina ke so da kauna, wanda zai jiyar dani dadin soyayya da zakin dake cikinta. Ko duk duniyar nan za ta taru a kaina ba zan yi auren A.B House ba sai wanda zuciyata ta aminta da shi. Nake so, yake sona da irin soyayyar da muka yiwa juna ni da Yaya Aliyu.
To Ali kam ya nuna ya haifu cikin uwarshi Zainabu, da ubanshi Na’ibi, kuma mai son farin cikin Fa’izah. A washegari ya dawo Giwa, inda ya saki kudi aka yi shagulgulan al’adarmu namu na Mallawa. Ya nuna tamkar komi bai faru ba, kamar Zanirah zabin shi ce ba zabin iyaye ba.
Amma zuciyar ta fi duhun dare duhu. Babu yadda ya iya fadan da ya fi karfin ka aka ce sai ka mai da shi wasa. Iyayen nan bashi da saman su, Hajjar nan ta fi karfin komi a garemu in har muna da iko, in har bamu da shi, zamu yi iya kokarinmu mu nemo masu shi suyi mata.
Sai dai abu ne da har illa masha Allahu ba zai taba kankaruwa daga zuciyarsa ba wato SON FA’IZAH! In ka ga ramar da Yaya Aliyu ya yi kamar wanda ya taso daga gadon asibiti bayan doguwar jinya. Jirgin karfe taran dare aka ajiye za su bi zuwa Lagos.
Aliyu ya dubi Hajjah ya ce, “Tunda har anyi mai wuyar Hajjah, ba a bari in koma ni kadai in shirya in dawo in dauke ta? In gyara muhallina daga na saurayi zuwa na mai iyali. Saurin da gaggawar na mene ne? Cikin abokan aikina duka babu wanda na sanar mawa na yi aure kawai sai a ganni da mata kamar na sato ta? Yanzu haka a tsakiyar aiki nake zuwa Ibadan a bani lokaci ko da sati daya ne in je in dawo don Allah.....”
Hajjah goyon Mahillah diyar Baba Barau take a bayanta ba ta ko dube shi ba. Ta sunkuci fidarta dake shake da cereal ta yi daki tana bambamin fada har da kumfar baki. Ta ce, “Karewar gyaran gida mai da gidan fadar shugaban kasa. Karewar rashin so Aliyu sayar da kan Zanirah garin Yarabawa. Amma kafarka-kafar Zannura”.
Aliyu ya yi tsit! Na fashe da dariya, Zanirah ko tsabar takaicin yadda Hajja ke mai da ta matar cushe kamar jakar da ta rasa miji na san shi yasa ta zub da kwalla.
Kamar za ta fashe da kuka ta ce, “Ni dai gaskiya Hajjah ki daina ce mun Zannura.....”
Hajjah ta ce, “Zannuraini an fada, ainahin sunanki kenan (ma’abociyar haske biyu)”.
Zanirah ta zumburi baki ta ce, “Hajjah Zunnuraini sunan namiji ne (Usman kenan)”.
Hajjah ta ce, “Allah ya bamu albarkacinsa. Abin da yasa na saka miki suna Zannura saboda an haife ki Ranar Arfah, kuma kwanan watan ya yi daidai da ranar da Najeriya ta karbi ‘yancin kanta daga hannun Turawa, ga ki fara kal kamar auduga, ga kyau ga kyan hali. In baka so Zanirah ba ina jin babu zuciya da mazantaka a tare da kai”.
Kalaman Hajjah sun girmi kunnuwan dukkanninmu daya bayan daya muka zame kowa ya bi hanya daban mai billar da shi wani sashe na gidan. Yaya Aliyu kuwa tunda ta dauko bayanin asalin sunan Zanirah ya bar dakin don haushi.
Ta fannina nima na nuna ni ‘yar halas ce, nayi ma Zanirah gudunmmuwar (kayan amfanin kitchen) masu karko da tsada ‘yan Japan. Turare mai tsada ‘versace’ da ‘hugo boss’ na ango Yaya Aliyu, na ce, “A sha kamshin amarci lafiya Aliyu da Zanirah”.
Sai a wannan lokacin ne Yaya Aliyu ya dago ido ya dube ni da wata muguwar harara da ban tsammana ba. Zanirah dake gefen shi cikin farin (swiss lace) mara nauyi mai yarfin (silver) dinkin buba da zani, kunshi baki sidik ya kama tafukan hannaye da kafafunta. Gashin nan ya sha relaxing ya kara baki ya kwanta a dogon wuyanta, amarya dai sak!
Ta dago kanta a hankali daga kan yatsun kafarta ‘yan sirara itama ta harare ni. Ga mamakinmu duka sai cewa ta yi, “Wanea irin amarci kike fade Fa’izah? A ya yin da zuciyoyi biyu basu dai-daita da juna ba? Auren da ake lallashi da takurawa mijin ya so ka, shi kike ambatawa amarci Fa’izah? Kaico da auren da ake roko da lallashin mijin ya dauki amaryar yana gudu.
ZAMANI YA CHANZA, ya kamata iyaye da kakanni irin Hajjah su gane hakan, su ajiye traditionality su bi modernity in dai ba fadar Allah da manzo bane. Domin maimakon a gyara zumuncin sai a bata, ko a zalinci daya a kasa kwatar masa hakkinsa don a dorar da zumunci”.
Ta mike ta yi waje tana mai fidda zafafan hawaye. Na kasa cewa komi sabanin Yaya Aliyu da ya kyabe baki ya gyara kwanciyar sa cikin kujera. Tsam! Nima na mike na bar wurin. Ummi ta bimu da kallon tausayi baki dayanmu.
Karfe shida saura minti talatin, iyakar rakiyar mu dasu Zanirah filin jirgin saman Kaduna, inda suka hau jirgi mai zuwa Legas.
Sai a wannan lokacin ne zuciyata ta soma turiri, tana kurma ihun yarda da zancen Zanirah ZAMANI YA CHANZA.... ya kamata Hajjah da ire-irenta su ajiye traditional false beliefs su yarda love is a natural nature that cannot be totally eradicated. Yanzu ne na tabbatar na rasa Aliyu har abada! A lokacin da tayoyin jirginsu suka rabu da kasa. Sai na fashe da kuka a lokacin da wani bakon tunani ya bakunce ni, wato yanayin idanun Zanirah (oily eyes).
Sau da dama Yaya Aliyu kan ce “Fa’izah ina ma kema irin kwayar idon Zanirah gare ki? Wallahi da na ji dadi na.....”
Hawayena suka sake ninka na da.... Ga Zanirah nan complete din ta ka samu Aliyu. Hawaye na ya sake ninka na da, na kifa kaina a kafadar Ummi muka ci gaba da kukan tare. Inda wanda ya san sirrin son da nake wa Yaya Aliyu, to Ummi ce, don tare muka rayuwa a makaranta fiye da Zanirah dake Giwa a lokacin da muka mallaki hankalin kanmu.
Babu irin tsarin da ban yiwa rayuwar aure na da Yaya Aliyu ba. Yadda za ta kasance, yadda zamu yi ta, yadda zamu gudanar da ita da yadda zamu tafiyar da ita, amma a yau Hajjah and her false beliefs (a ganina) sun rushe komai.
Lokaci guda wata irin sabuwar zuciya ta shige ni mai dauke da sabon perception. Na san dadin ‘So”, haka na san dacin rasa shi. In Allah ya yarda ba zan yarda in auri wanda bana so ba! Ba zan yi auren zumuncin ba, ba zan yi auren A.B Family ba. Zan zamo mutum ta farko da za ta canza A.B Family, zan zamo mutum ta farko da za ta yi auren soyayya a cikin zuri’ar Abubakar Bamalli Giwa.
Bare zan aura wanda zuciya da ruhina ke so da kauna, wanda zai jiyar dani dadin soyayya da zakin dake cikinta. Ko duk duniyar nan za ta taru a kaina ba zan yi auren A.B House ba sai wanda zuciyata ta aminta da shi. Nake so, yake sona da irin soyayyar da muka yiwa juna ni da Yaya Aliyu.