Sashe 61
Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
***
Washegari tun safe su Ummi ke shirin wucewa Kaduna liyafa, sai shirya kaya ake ana zuge (troller). Motocin da za su kwashe su zuwa Jabi Road basu zo ba sai bayan azahar suka shiga suka tafi da kawayenmu duka daga can ne za su shirya zuwa wajen da aka tanada don yin liyafar.
Ina kwance a doguwar kujera ban ko motsa ba ina kallon fitarsu daya bayan daya. Yaya Aliyu ya shigo yana balle 'links' din hannun rigarshi ya ce da Zanirah.
"Madam, muje ko?"
Ta tashi wata tikisa da ita kamar alkubus, shi kuma aka sakalo hannu kugunta aka tallafeta, a haka suka fice ko kallona basu yi ba, suka fice. Inda ya bude mata gaban 'Porsche' dinsa ta shiga, ya rufe ya zagaya shima ya shige. Bashir aka kama hannun amarya mai kama da Princess Diana don kyau da daukar ado suka fice. Har sun kai kofa ya juyo yana ce da ni.
"Af, gwauruwa, mijin robarki fa yana jiranki a waje Yaya Sa'idu, an baki kaya don kidifiri kin ki amsa. No worries, na jikinki ma inaga ba laifi, kya samu waje ko tebirin iyaye da su".
Wani gululu yazo ya tokare ni yaki wucewa, ya tsaya min a makoshi, amma Fa'izah (is always) Fa'izah, ina da 'ki-fadi' sai na ce.
"Allah Sarki Yaya Bashir ka sallami mijin robar Fa'izah ko babu shi Fa'izah (can survive), kasan mace Allah Ya yi mata juriyar iya rayuwa ba tare da namiji ba, namijin ne bai iya rayuwa mai dadi sai da mace. I.e namiji zai saki mace, ta zauna gidan iyayenta ba tare da ta yi wani auren ba kuma ta zauna lafiya. Amma shi namiji a ranar da yayi sakin ma zai iya kawo wata, ka gane?"
Ya ce, "Ohonki kuma! Tsoron shan kunya ya hanaki zuwa (party) baki da sauran bakin surutu". Da haka ya fice.
Na mike tsam bayan fitarsu nayi wanka, na dauko lesi na na sanya, na saki dogon gashina a gadon bayana, na karkata goggoro na tsayar dashi dai dai goshi na. Na janyo takalmi da jaka na cikin kwalinsu mai tudun dunduniya siririya da siririyar igiyar daurewa na fitar na sanya, na rike 'purse' din mahadinsa wadda kudin mota kawai na zube a ciki. Nan da nan na hau walkiya kamar wata dan daren goma sha hudu.
Na kawo (fashion earing) kalar adon lesin na daura (shimmering pearls) hannu, wuya, kunne da idon sawu sai walainiya nake duk motsin da nayi. Ni kaina yau nayi mamakin yadda nake, ban taba tunanin haka Allah Ya kyautata surata ba sai yau.
Na fito harabar gidan Baba Na'ibi babu kowa don haka na tura wani almajiri yayo min hayar taxi kafin minti goma sai gashi ya dawo cikin motar tare da mai taxin.
Na ce da mai taxin ya yi duk iya gudun da zai iya ya kaini (Indoor-sport hall) na garin Kaduna cikin awa daya, ko nawa ne zan biya shi. Nan da nan ya ce in shigo mu tafi.
Dakin taron ya cika ya batse babu masaka tsinke da kyawawan iyalin A.B tabbacin a yau mallawan na biki kasurgumi da basu taba yin kwatankwacinsa ba. A cikin tafiyar nutsuwa na shiga ratsa taron jama'ar suna kallona tabbacin basu tsammaci zuwana ba ma balle wannan shiga ta firgitarwa. Ashe wajen cike yake da abokan Fa'eez na Kad-Poly irin su Surajo Nuhu wanda a halin yanzu ma'aikaci ne a Central Bank da wasu daga cikin abokan su da yawa suka mike suka tarboni muka jero tare sai tafi suke yi da dariyar farin ciki, yayin da Sa'adu Bori dake cin kasuwarsa a wajen ya karkatar da akalar wakarsa gareni ya kyale su Ummi, cewa yake.
"TAKAWARKI LAFIYA GIMBIYAR ABUBAKAR FA'IZU GIWA... AMARYA FA'IZA AMANAR FA'IZ GIWA...".
Suraj tunda na tako kafata cikin (hall) din yake min (spraying) da dollers madadin Fa'izun su kenan.
Ni kam ko a jikina, a raina fadi nake wahala ce bata ishe ku ba, ko kallo basu isheni ba.
Wajen ya hautsine da kirarin abokan Fa'iz masu video da masu camera suka juyo da akalarsu kanmu gaba daya abokan Fa'iz daukana suke hotuna wasu vedio da wayoyinsu. Ina kallon bakin su Yaya Aliyu dake (high-table) yaki rufuwa, haka Mama da tarin hamshakan matan Kaduna da ta gayyato.
Anan Yaya Rabi, Aunty Hauwa da Mama da kanta suka taso suka tarbeni suka hana ni isa ga mazaunin su Ummi.
Girgiza kai nake cikin son kecewa da kuka ina yi musu nuni da ka su barni in wuce, amma sunki hakan. Mama ta rikeni gam-gam, haka Ummi da Bashir, Zanirah da Yaya Aliyu tasowa suka yi daga mazauninsu ya saura babu kowa a gaban Sa'adu bori cikin filin sai mu 'ya'ya da jikokin Hajjah da kawayen Maman Kaduna sai ko Surajo da ya rufa min asiri suka shiga yi mana "spraying" ni da Surajo sai ka rantse da Allah shi ne angon nawa, kazalika Ummi da Bashir, Zanira da tirtsetsen cikinta da Yaya Aliyu rungume da ita, duk suka bude bakin jaka suka shiga yi mana 'spray' tako'ina. Dadi ne ko mene ne ya yi min yawa, sai gani kuka ya kece mani.
Tausayin Mama har kokon raina da jinjina kaunar da take mani na kasa jurewa nima ban san dalilin tausayin nata da ya rufeni ba, na zame da gudu na karasa mazaunin su Ummi na zauna na kifa kaina a tebirin na shiga kuka mai yawan gaske wanda ni kaina bansan dalilinsa ba.
Suraj ne yazo ya zauna a kujerar Yaya Bashir ya ce.
"Fa'izah, Fa'iz bai kyauta ba na sani, don me ya yi mana haka? Rana irin wannan mai dumbin tarihi ka tsallake ka tafi wani aiki kai kafi kowa aiki?"
Haushinsa ya kara kamani da shisshigin da yake ta yi mini tunda na sako kafata a filin wajen nan shi bai yadda ba asiri ya rufawa abokinsa, kuma abin kirki yayi.
Na dago idanuna jike jagab da hawaye,
"Kada ka kuma yi min zancen wani Fa'iz, nazo (partyn) nan ne don Ummi da Bashir, don me zaka zo kana tambaya ta wani Fa'iz bayan mun rabu tuntuni?" Dariya Surajo ya yi, "Aradu bonono Fa'iz yayi miki wai rufe kofa da barawo, waye ya ce miki Fa'iz zai iya sakin ki? Ko jiya shi ya kirani daga England ya ce in taimake shi inzo in tsaya tare da ke, bai yarda da kowa ba cikin abokanmu sai ni. Wane irin saki babu ko dadin ji? Kina hauka ne?"
Wani irin rugugi naji cikin kwanyar kaina, da kyar in ba motsin kwakwalwa bane. Na zazzaro ido ina duban Surajo ina auna abinda yake fadi cikin hankali da tunani. Nasan Surajo mutum ne mara wasa, na sanshi da can don ya so Ummi aka nuna ba za'a bashi ba ya hakura.
Abubuwan da suka faru suka shiga dawo min sabbi kar, wato yanayin Fa'iz bai nuna damuwa ko bacin rai ba a sanda yake min rubutun cikin takarda, babu wata alama ta nuna damuwa a fuskarshi. Me ya hana Baba bai lallasa ni ba, kuma su Aunty Rabi babu wanda ya yi fushi dani a lokacin? Sai ma cewa da tayi in taso mu tafi bikin Ummi Giwa? Me ya hana ni karanta takardar da kaina abin kamar tsafi?"
Raina ya yi mugun baci, hankalina ya jirkice, idanuna suka kada suka yi jawur suka wani irin cicciko da kwalla.
Suraj Nuhu, ya yi danasanin karambaninsa, ya tabbatar ya yi babban kwafsi, kuma abinda ba'a aike shi ba don son ya burge. Ya shiga in-ina yana fadin.
"Fa'izah da gangan nake, na rantse miki bamu yi maganar komi da Fa'iz ba, ni na kawo kaina...".
Ina! Surajo ya barota domin kuwa mikewa nayi gaba dayana tsam nayi hanyar fita, yayin da ya biyoni yana magiyar in saurare shi, amma kurar da ta debo shi ban kalla ba.
Su Ummi suka dakata da abinda suke yi suka biyo mu da idanu. Aliyu ya saki hannun matar shi ya biyo bayanmu, ya riqo hannun Suraj ya ce ya rabu dani, kana ya haushi da fadan.
"Don me yasa ka gaya mata Surajo? Wa ya aike ka yi mata zancen Fa'iz? Ka san haukar Fa'iza kuwa? Muna zaman zamanmu lafiya ka sayo mana tashin hankali".
Surajo cikin matsananciyar nadama ya ce.
"Ni ina na sani? Na gaya mata ne kawai Fa'iz ne ya yi min waya cewar yana Wales inzo in tsaya da ita, shi kenan abinda na fada".
Yaya Aliyu ya dafe kai yana fadin, "Shi kenan Surajo ka baro mana likin, sai gyaran Allah. Wallahi ko lallashi ba zan je ba ta je can duk inda zata je zata dawo da kafafunta, ai ba yau ta fara ba”.
Da daren washegari aka raka Ummi gidanta a Kabala Custain. Washegari Zanirah da Aliyu da ‘yarsu Fa'izah suka wuce Lagos, na Giwa suka nufi Giwa, na Zaria ma haka, haka na Kaduna.
Miftahu da Ya Rabi suma suka dauki hanyar Kano da yaransu biyu, amma Ya Rabi ta ce da Yaya Mufty su tsaya Zaria su ga halin da nake ciki.
Hajja kam ta ce da su don Allah kowa ya kyale ni inyi kida na da rawata ni kadai, kada wanda yaje inda nake balle ya wani lallasheni in bata masa rai a banza. Amma Ya Rabi ta kasa jurewa. Ko cikin 'ya'ya Fa'iza ta daban ce a wurinta, tana da matsayin da babu mai shi cikin tarin 'ya'yan nata.
Washegari tun safe su Ummi ke shirin wucewa Kaduna liyafa, sai shirya kaya ake ana zuge (troller). Motocin da za su kwashe su zuwa Jabi Road basu zo ba sai bayan azahar suka shiga suka tafi da kawayenmu duka daga can ne za su shirya zuwa wajen da aka tanada don yin liyafar.
Ina kwance a doguwar kujera ban ko motsa ba ina kallon fitarsu daya bayan daya. Yaya Aliyu ya shigo yana balle 'links' din hannun rigarshi ya ce da Zanirah.
"Madam, muje ko?"
Ta tashi wata tikisa da ita kamar alkubus, shi kuma aka sakalo hannu kugunta aka tallafeta, a haka suka fice ko kallona basu yi ba, suka fice. Inda ya bude mata gaban 'Porsche' dinsa ta shiga, ya rufe ya zagaya shima ya shige. Bashir aka kama hannun amarya mai kama da Princess Diana don kyau da daukar ado suka fice. Har sun kai kofa ya juyo yana ce da ni.
"Af, gwauruwa, mijin robarki fa yana jiranki a waje Yaya Sa'idu, an baki kaya don kidifiri kin ki amsa. No worries, na jikinki ma inaga ba laifi, kya samu waje ko tebirin iyaye da su".
Wani gululu yazo ya tokare ni yaki wucewa, ya tsaya min a makoshi, amma Fa'izah (is always) Fa'izah, ina da 'ki-fadi' sai na ce.
"Allah Sarki Yaya Bashir ka sallami mijin robar Fa'izah ko babu shi Fa'izah (can survive), kasan mace Allah Ya yi mata juriyar iya rayuwa ba tare da namiji ba, namijin ne bai iya rayuwa mai dadi sai da mace. I.e namiji zai saki mace, ta zauna gidan iyayenta ba tare da ta yi wani auren ba kuma ta zauna lafiya. Amma shi namiji a ranar da yayi sakin ma zai iya kawo wata, ka gane?"
Ya ce, "Ohonki kuma! Tsoron shan kunya ya hanaki zuwa (party) baki da sauran bakin surutu". Da haka ya fice.
Na mike tsam bayan fitarsu nayi wanka, na dauko lesi na na sanya, na saki dogon gashina a gadon bayana, na karkata goggoro na tsayar dashi dai dai goshi na. Na janyo takalmi da jaka na cikin kwalinsu mai tudun dunduniya siririya da siririyar igiyar daurewa na fitar na sanya, na rike 'purse' din mahadinsa wadda kudin mota kawai na zube a ciki. Nan da nan na hau walkiya kamar wata dan daren goma sha hudu.
Na kawo (fashion earing) kalar adon lesin na daura (shimmering pearls) hannu, wuya, kunne da idon sawu sai walainiya nake duk motsin da nayi. Ni kaina yau nayi mamakin yadda nake, ban taba tunanin haka Allah Ya kyautata surata ba sai yau.
Na fito harabar gidan Baba Na'ibi babu kowa don haka na tura wani almajiri yayo min hayar taxi kafin minti goma sai gashi ya dawo cikin motar tare da mai taxin.
Na ce da mai taxin ya yi duk iya gudun da zai iya ya kaini (Indoor-sport hall) na garin Kaduna cikin awa daya, ko nawa ne zan biya shi. Nan da nan ya ce in shigo mu tafi.
Dakin taron ya cika ya batse babu masaka tsinke da kyawawan iyalin A.B tabbacin a yau mallawan na biki kasurgumi da basu taba yin kwatankwacinsa ba. A cikin tafiyar nutsuwa na shiga ratsa taron jama'ar suna kallona tabbacin basu tsammaci zuwana ba ma balle wannan shiga ta firgitarwa. Ashe wajen cike yake da abokan Fa'eez na Kad-Poly irin su Surajo Nuhu wanda a halin yanzu ma'aikaci ne a Central Bank da wasu daga cikin abokan su da yawa suka mike suka tarboni muka jero tare sai tafi suke yi da dariyar farin ciki, yayin da Sa'adu Bori dake cin kasuwarsa a wajen ya karkatar da akalar wakarsa gareni ya kyale su Ummi, cewa yake.
"TAKAWARKI LAFIYA GIMBIYAR ABUBAKAR FA'IZU GIWA... AMARYA FA'IZA AMANAR FA'IZ GIWA...".
Suraj tunda na tako kafata cikin (hall) din yake min (spraying) da dollers madadin Fa'izun su kenan.
Ni kam ko a jikina, a raina fadi nake wahala ce bata ishe ku ba, ko kallo basu isheni ba.
Wajen ya hautsine da kirarin abokan Fa'iz masu video da masu camera suka juyo da akalarsu kanmu gaba daya abokan Fa'iz daukana suke hotuna wasu vedio da wayoyinsu. Ina kallon bakin su Yaya Aliyu dake (high-table) yaki rufuwa, haka Mama da tarin hamshakan matan Kaduna da ta gayyato.
Anan Yaya Rabi, Aunty Hauwa da Mama da kanta suka taso suka tarbeni suka hana ni isa ga mazaunin su Ummi.
Girgiza kai nake cikin son kecewa da kuka ina yi musu nuni da ka su barni in wuce, amma sunki hakan. Mama ta rikeni gam-gam, haka Ummi da Bashir, Zanirah da Yaya Aliyu tasowa suka yi daga mazauninsu ya saura babu kowa a gaban Sa'adu bori cikin filin sai mu 'ya'ya da jikokin Hajjah da kawayen Maman Kaduna sai ko Surajo da ya rufa min asiri suka shiga yi mana "spraying" ni da Surajo sai ka rantse da Allah shi ne angon nawa, kazalika Ummi da Bashir, Zanira da tirtsetsen cikinta da Yaya Aliyu rungume da ita, duk suka bude bakin jaka suka shiga yi mana 'spray' tako'ina. Dadi ne ko mene ne ya yi min yawa, sai gani kuka ya kece mani.
Tausayin Mama har kokon raina da jinjina kaunar da take mani na kasa jurewa nima ban san dalilin tausayin nata da ya rufeni ba, na zame da gudu na karasa mazaunin su Ummi na zauna na kifa kaina a tebirin na shiga kuka mai yawan gaske wanda ni kaina bansan dalilinsa ba.
Suraj ne yazo ya zauna a kujerar Yaya Bashir ya ce.
"Fa'izah, Fa'iz bai kyauta ba na sani, don me ya yi mana haka? Rana irin wannan mai dumbin tarihi ka tsallake ka tafi wani aiki kai kafi kowa aiki?"
Haushinsa ya kara kamani da shisshigin da yake ta yi mini tunda na sako kafata a filin wajen nan shi bai yadda ba asiri ya rufawa abokinsa, kuma abin kirki yayi.
Na dago idanuna jike jagab da hawaye,
"Kada ka kuma yi min zancen wani Fa'iz, nazo (partyn) nan ne don Ummi da Bashir, don me zaka zo kana tambaya ta wani Fa'iz bayan mun rabu tuntuni?" Dariya Surajo ya yi, "Aradu bonono Fa'iz yayi miki wai rufe kofa da barawo, waye ya ce miki Fa'iz zai iya sakin ki? Ko jiya shi ya kirani daga England ya ce in taimake shi inzo in tsaya tare da ke, bai yarda da kowa ba cikin abokanmu sai ni. Wane irin saki babu ko dadin ji? Kina hauka ne?"
Wani irin rugugi naji cikin kwanyar kaina, da kyar in ba motsin kwakwalwa bane. Na zazzaro ido ina duban Surajo ina auna abinda yake fadi cikin hankali da tunani. Nasan Surajo mutum ne mara wasa, na sanshi da can don ya so Ummi aka nuna ba za'a bashi ba ya hakura.
Abubuwan da suka faru suka shiga dawo min sabbi kar, wato yanayin Fa'iz bai nuna damuwa ko bacin rai ba a sanda yake min rubutun cikin takarda, babu wata alama ta nuna damuwa a fuskarshi. Me ya hana Baba bai lallasa ni ba, kuma su Aunty Rabi babu wanda ya yi fushi dani a lokacin? Sai ma cewa da tayi in taso mu tafi bikin Ummi Giwa? Me ya hana ni karanta takardar da kaina abin kamar tsafi?"
Raina ya yi mugun baci, hankalina ya jirkice, idanuna suka kada suka yi jawur suka wani irin cicciko da kwalla.
Suraj Nuhu, ya yi danasanin karambaninsa, ya tabbatar ya yi babban kwafsi, kuma abinda ba'a aike shi ba don son ya burge. Ya shiga in-ina yana fadin.
"Fa'izah da gangan nake, na rantse miki bamu yi maganar komi da Fa'iz ba, ni na kawo kaina...".
Ina! Surajo ya barota domin kuwa mikewa nayi gaba dayana tsam nayi hanyar fita, yayin da ya biyoni yana magiyar in saurare shi, amma kurar da ta debo shi ban kalla ba.
Su Ummi suka dakata da abinda suke yi suka biyo mu da idanu. Aliyu ya saki hannun matar shi ya biyo bayanmu, ya riqo hannun Suraj ya ce ya rabu dani, kana ya haushi da fadan.
"Don me yasa ka gaya mata Surajo? Wa ya aike ka yi mata zancen Fa'iz? Ka san haukar Fa'iza kuwa? Muna zaman zamanmu lafiya ka sayo mana tashin hankali".
Surajo cikin matsananciyar nadama ya ce.
"Ni ina na sani? Na gaya mata ne kawai Fa'iz ne ya yi min waya cewar yana Wales inzo in tsaya da ita, shi kenan abinda na fada".
Yaya Aliyu ya dafe kai yana fadin, "Shi kenan Surajo ka baro mana likin, sai gyaran Allah. Wallahi ko lallashi ba zan je ba ta je can duk inda zata je zata dawo da kafafunta, ai ba yau ta fara ba”.
Da daren washegari aka raka Ummi gidanta a Kabala Custain. Washegari Zanirah da Aliyu da ‘yarsu Fa'izah suka wuce Lagos, na Giwa suka nufi Giwa, na Zaria ma haka, haka na Kaduna.
Miftahu da Ya Rabi suma suka dauki hanyar Kano da yaransu biyu, amma Ya Rabi ta ce da Yaya Mufty su tsaya Zaria su ga halin da nake ciki.
Hajja kam ta ce da su don Allah kowa ya kyale ni inyi kida na da rawata ni kadai, kada wanda yaje inda nake balle ya wani lallasheni in bata masa rai a banza. Amma Ya Rabi ta kasa jurewa. Ko cikin 'ya'ya Fa'iza ta daban ce a wurinta, tana da matsayin da babu mai shi cikin tarin 'ya'yan nata.