← Book details Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 98

Sashe 7

Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

****
Gabatowar karshen zangon karatu na farko muka fara gwaji wato (test), inda na kara zage damtse iyakar iyawata na yi dan abin a zo a gani. Wannan ne dalilin da yasa kafin zuwan jarabawa na dan rike wasu abubuwa da yawa, don haka da muka fara sai ta zo min da sauki, na cinye darasin Arabic da English tsaf, sauran subject din dai gasu nan dai la ba’asa ya fi la shai’in in ji Larabawa. Su Hajjah sun zo mana visiting (ziyarar dalibai) har da su Inna Kubra.
Ranar hutu da murnar mu muka nufi bakin gate a zaton mu Yayanmu Aliyu ya zo daukar mu, don baki ganni ba fuska kamar gonar auduga don murmushi. Ina rike da (report card) dina wanda nake kyautata zaton na yi abin kirkin da zai faranta ran Yaya Aliyu, na sauke nauyin alkawari na yi abin a zo a gani.
Amma murnata ta daka tsalle ta burma ciki sakamakon ganin mutumin da na tsana da gani a rayuwata, mutumin da na tsani jin muryarshi da ganin fuskarshi mara alheri a gare ni, dan uwan da da za a bani wuka a ce in caka mishi ba komai da na yi gaggawar aikatawa. FA’EEZ MUKHTAR ABUBAKAR BAMALLI GIWA.
Sanye da makubar shadda ‘getzner’ dinkin samarin garin Kaduna masu ji da tashen samartaka, bakar dara mai gezar bakin gashi ya kara haske sosai ya yi fresh ta yadda ko ni da bani son shi a duniya na san Fa’ezz namiji ne abin so ga kowa, ba ga mata kadai ba har maza jinsinsa ba za su bar yiwa kansu fatan zama ko dakacen komawa kamar shi ba.
Jingine jikin motar Yaya Aliyu kirar ‘Picanto’ (Kia), fuskar nan dinke babu alamun rahama kamar kullum, na damko hannun Ummi kam, kirjina na dukan tara-tara ba ma uku-uku ba. Fuskar Ummi kamar an aiko mata da Manzon rahama ta saki hannuna ta sheka da gudu aguje wai za ta rungume shi.
Ya kuwa doka mata tsawar da ta sa ta tsugunnewa a kasa cikin gigicewa. Ganin yadda ya tsoratata ya gigitata ya yankwanata a gaban sauran daliban da ke gefe, ko me ya tuna? Ya yi dan murmushi gajere wanda ya fidda lotsawar gefen kuncinsa na dama.
Ya ce, “To ai ke ce abin naki babu kan gado tsohuwa (sunan da suke tsokanarta don ita ce mai sunan Hajjah, shi kuma su Yaya Aliyu su ce mishi tsoho kasantuwar shi mai sunan marigayi Abubakar Giwa (A.B Bamalli Giwa). Ya ce, “Kai! Ummi ba a girma”.
Sannan ne ta iya mikewa a darare. Ni dai ina daga gefe hannuwana sarke a kirji ina kallonsu, a zuciyata in ban da Allah ya kara ba abin da nake yiwa Ummi.
Ya budewa Ummi kofa ta zauna a gidan gaba ya rufe, yana sanya kayanmu a boot din mota ya juyo inda nake tsaye ya dube ni, ina tsaye jikin bishiya kawai ina kallon su. Ya rufe boot din motar ya shiga mazaunin shi zai ja motar.
Ummi ta ce, “Ya Fa’iz, Fa’iza fa ba ka ganta bane?”
Wata muguwar harara ya yi mata, ya ce, “In na ganta sai me? Sai me zan yi? Ita ba ta ganin mutane? Ba ta san ta gaishe su ba ko don UWARTA! Ta koya mata rashin tarbiyya irin tasu ta kabilu”.
Sai kawai ya ja motar ya badeni da kura. Ummi kira take “Fa’iza! Fa’iza!! Fa’iza!!!” Amma ko sauraron ta bai yi ba.
Na durkushe a nan na soma kuka, na yi kuka har muryata ta dashe. Na daga kai na dubi dai-daikun daliban da suka rage kwata-kwata babu ‘yan Kaduna, Zaria balle garinmu. Daga ‘yan Kano sai ‘yan Jigawa, sai ko dai-daiku daga jihar Gombe da Adamawa.
Na dora hannuna aka na rafsa kuka. Duk dokina na son ganin Hajjah, Zanirah da Yaya Aliyu ya gushe, sai wani irin tukuki da zuciyata ke yi.
Wannan wace irin kiyayya ce Ya Fa’iz ke min? Wace irin kiyayya yake yiwa mahaifiyata da ta shafe ni? Wannan ma ai rashin imani ne ba kiyayya ba. Duk irin kin da nake wa Fa’iz babu yadda za ayi in baro shi a jejin da na san ba shi da kowa, a gari mai nisa da babu kowa nashi.
Na rasa inda zan sa kaina don bakin ciki, kawai sai na samu gefen bishiyar darbejiya na share na kwanta a wurin ina kuka. Ina addu’ar Allah ya kashe Fa’iz in huta.
“Ke me kike a nan a kwance a kasa? Ko ba a zo daukar ki bane?”
Muryar wata malama ta doki dodon kunnena. Na dube ta idona jage-jage da hawaye na ce, “Eh”.
“Yar wane State ce ke?”
“Na zo ne daga Giwa”.
“Giwa? Giwa ta jihar Kaduna? Oh! Ke Bamalliya ce ko?”
“Eh”. Na amsa a gajarce.
“Amma kin yi nisa sosai, yanzu ya za ayi kenan?”
Na ce, “Zan kara jira a nan zuwa yamma na san za a zo min”.
Ta ce, “Ba zai yiwu ki yi ta zama ke kadai a nan ba, ki tashi ki shiga daga Library tare da yaran can ‘yan Niger State, kinga za ki fi hango duk mai shigowa ki fidda naki”.
A sanyaye na ce, “To”. Na mike na kade jikina na dauki jakar littattafaina na rataya, da yake duk sauran kayan sawarmu suna cikin kayan da Ummi ta tafi dasu.
Ban dade da zama ba barci ya dauke ni a kan daya daga cikin kujerun labiraren, na farka ne karfe biyar na yamma sakamakon tashin da wata yarinya ta yi min wai in tashi in yi sallar la’asar.
Sai kawai na fashe da kuka ganin yadda duhun yamma ya lullube sararin samaniyar subhana. Na bita toilet din dake jikin labiraren muka dauro alwala muka yi sallah, ni azahar ma sai a lokacin na yi ta. Har na idar da sallah kuka nake.
Ta ce, “Ki daina kuka, ai tabbas za a zo daukar mu ne, kema da baki da nisa kamarmu? Ai iyayenki babu yadda za ayi su manta dake”.
Cikin kuka na ce, “An zo an dauki Ummi, ni tafiya ya yi ya barni, in Allah ya yarda ba zan dawo makarantar nan ba....”
Shigowar daya daga cikin masu gadin makaranta yasa muka yi shiru muka zuba mishi mayunwatan idanuwanmu da yunwa da damuwa suka hadu suka jeme su, ya kira yarinyar nan wadda da alama ta girmeni cewar ta zo an zo daukar ta daga Adamawa. Ta fita tana daga min hannu har ta kule.
Na kifa kaina cikin cinyoyina na ci gaba da kuka a hankali, ban san sanda sarkin barayin ya zo ya sake sace ni ba.
Karfe bakwai na magariba na farka sakamakon azababbiyar yunwar da ta sake murda min ‘ya’yan hanjina, don saboda dokin zuwa gida ko karyawa (break fast) bamu tsaya mun yi ba saboda tunanin tuni Hajjah ta gama shirin karbarmu da hadadden girkinta.
Na dafa cikina da hannuna daya na runtse idona da karfi, ganin yadda duhun dare ya mamaye sararin sama, hawaye suka ci gaba da yi min lugude a fuska.
Hannun mutum na ji ya cira ni tsaye, na bude ido firgigit na mike a razane cikin fadin “Wayyo Allah..... wayyo Hajjah....” Abinki da cikin da ba komai, sai hajijiya ta kwashe ni yuuuu! Gaba daya na fada ga mutumin da ke tsugune a gabana, na daddage na kara sakin ihu....
“Wayyo Hajjah na shiga uku na lalace.... na mutu!”
Ya rungumeni sosai a jikinsa yana fadi cikin tattausar murya irin ta marasa koshin lafiya, “Relax, relax Fa’iza, relax”.
Na dauki lokaci ina tunanin mai muryar, kwakwalwata ta shiga tariyo min inda na san mai murya mai taushi da rashin amo. In ban yi kuskure ba zan iya cewa ta YAYA ALIYU CE.... YA YA ALIYU HAIDAR NA’IBI A.B GIWA.
Na lumshe idona na dan lokaci, bugun zuciyata na saisaita da zazzafan jikin Aliyu, zuciyata da ta yi zafi na yi min sanyi kadan-kadan.
Tsayin minti biyar Yaya Aliyu na rike dani, ya ce cikin kankanuwar murya, “Fa’izah are you ok?”
Na gyada kai, ya sake ni muka mike a tare yana rike da hannuna. Ya dauki jakar litattafaina da daya hannun nasa na hagu muka fita daga dakin karatun, ya bude gidan baya na shiga, ya fiddo cooler din abinci ya bude, kamshin girkin Hajjah ne ya doki hancina, ba girkin cikin gida ba, wannan girki ne da take yi lokaci zuwa lokaci da hannunta, da na dade da sani ya baibaye ni, ya tado min tsohuwar yunwar da na wuni da ita.
Yawun bakina ya wani irin tsinke tun kamin in kai lomar farko sanda Yaya Aliyu ke zuba min a farantin cin abinci (plate), dafadukar shinkafa ce da aka yi rabinta da zallar tsokar kaza da ganyen alayyahu da kabeji.
Ya bude wata foil paper din ya fiddo gasasshen naman nan na kan hanyar Gusau da ya saya mana a hanya a zuwanmu, duk ya ajiye min ya rufe kofar ya shiga mazauninshi ya ta da motar muka soma tafiya.
Bayan ya miko min robar ruwan swan mai sanyi ya ce, “Kina iya kwanciya idan kina jin barci in kin gama”. Da gudu ya fizgi motar bayan ya daga ma masu gadi hannu ya kuma yi signing shaidar cewa an dauke ni.
Amma fa ya sha fada daga malamin da ke kula da shige da ficen dalibai, har ya bawa uku lada. Magana daya yake fadi masu su yi hakuri ba laifinsa bane.
A yayin da wata danja ta tsai damu kusa da wata fitila mai hasken gaske, garin kalle-kallena mai nuna ciki ya dauka na fara dawowa hayyacina, na dubi hannun Yaya Aliyu wanda ke bisa giyar motar, allurar karin ruwa na gani soke jikin jijiyar hannunsa jini na diga amma bai kula ba, tukin shi kawai yake.
Da na kura ido sai na ga hanyar karin jini da wata siririyar allurar ita ma soke duka a hannunsa ya bi fatar jikinsa ya kwanta. Na dube shi a razane domin tun zuwan shi ban ga fuskarshi ba, ya rame sosai ya yi duhu ainun.
Na daga murya da karfi cikin tashin hankali na ce, “Yaya Aliyu ka tsaya”. Ba tare da ya juyo ba, haka nan ban ga annuri a kyakkyawar fuskarshi ba ya ce, “A kan me zan tsaya? Bakya ganin tafiyar dare zamu yi?”
Chapter 7 · 0% Book details