← Book details Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 98

Sashe 11

Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read

Wannan ne dalilin da yasa muka kara zage damtse don mu fita kunyarsu mu ba mara da kunya, mu nuna musu ba a banza suke wahalar da suke yi damu ba, we will insha Allah make them to be proud of it ta hanyar kara zafafawa kawunanmu da karatu.
Sai dai gatan da ake nuna mana baya shafar tarbiyyar da muka taso a ciki, muka gada iyaye da kakanni, muka kuma tashi muka ga ana yi cikin gidanmu tuntuni.
Ta fannin Yaya Aliyu, ya kara zage damtse da kokarin ganin na kara hazaka sosai da hikima da basira irin nasa. Ba zan manta ba a second term (zango na biyu) da na kai masa sakamakona na yi na shida, ya nuna min bacin rai sosai, ya daina kula ni, ya daina shiga sabgata, ko kallon inda nake ya daina. Ya daina sayo min gasasshen naman da ya zame min kamar taba.
Maimakon hakan duk ya koma yiwa Zanirah wadannan abubuwan a madadina, ita da ta kawo (second position), duk na bi na damu, na shiga cikin kunci da takura na babu gaira babu dalili.
Wannan ne ya zaburar dani na takurawa kaina da karatu a zango na gaba, iyakar iyawata na kawowa Yaya Aliyu (3rd position out of 60). Yaya Aliyu ya daga ni ya yi sama yana juyi dani a falon Hajjah, kayan dadi da nama kuwa sai da Hajjah ta yi ta fada tana zai sangarta ni, in na auri wanda ba shi da halin ciyar dani nama kullum fa? In shiga raina abin da ya kawo mani?”
A zangon farkonmu na sabon aji JSS 2, su Momin ABU, Maman Kaduna da Yaya Hauwa, Aunty Zainabu da matar Baba Barau Aunty Marwa, da matan su Baba Sadi duk suka yo Bus guda suka kawo mana ziyara.
Momin ABU rungume da sabon baby dinta kyakkyawa kamar Baban ABU, na rungume shi na rasa inda zan sa kaina don farin ciki. Bakina kamar ya yage don fara’a ina rungume da babyn, na ce, “Wai ya ya sunansa Momi?”
Ta ce, “Ban sani ba, ni fa ba wurinki na zo ba Aku sarkin magana”.
Na yi narai-narai da ido kamar zan yi kuka. Yaya Hauwa ta ce, “Rabu da ita Fa’iza, sunan shi Baban Kaduna (Mukhtar) shi kenan?” Na ce, “To, Ya Hauwa ya zamu ke kiran shi?” Ta ce, “Kowa a gida yana ce mishi ‘WALID”. Dadi ya rufe ni, na ce, “Yeh! Mun samu Waleed da Waleeda”.
Ta fannin Fa’iz karatun Diploma a Kaduna Poly ya sha masa kai, a kokarinsa na hattama (ND) wato National Diploma. Fa’iz wani irin mutum ne da baya son karatun boko sam. Diplomar ma sai da suka takura masa su Baban ABU suka bude mishi wuta, don bayan kammala sakandire dinshi a Madina kin ci gaba ya yi, kai dai barshi da tukin mota.
Duk wanda ke son zuwa unguwa Fa’iz ne direbansa, ba sai ka roka ba shi zai roke ka ka ba shi key din mota ya kai ka. Babu yadda bai yi ba Baba Muntari ya ba shi mota ya ki, don ya ce tukin mota ne yake hana shi karatu don haka duka bus-bus din A.B Estate mukullan su yana hannun Fa’iz.
Kowa da (nature) dinsa, kowa da kaddararsa, to “tukin mota shine kaddarar Fa’eez Mukhtar Abubakar Giwa”.
Yana kwanan makaranta ne a Kad Poly don haka yawancin hutun da muke zuwa muna samun sa’ida. Week end kawai yake zuwa Giwa ya koma lahadi, don haka marorinmu sun sarara cikin shekarun nan.
Wannan hutun da muke zangonmu na karshe na aji uku na karamar sakandire (JSS.) mun dukufa karatun jarrabawar (placement). A wani dare a hostel na dubi Ummi wada ke nazarin wani littafin Islamic Studies na B. Aisha Lemu (For Juniors) na ce, “Ummi kin san tunanin da ya zo min kuwa?”
Ta ce, “A’a, sai kin fada”. Tare da rufe littafin da ke hannunta.
Na ce, “Wallahi tunani na yi, gara mu hada baki mu ki makarantar nan haka. Babu mai tunawa damu, babu mai zuwa mana a kan kari ko akai-akai, komai mune karshe. In ba don ma Yaya Aliyu da ke zuwa duk wata ba, ai da mun kade.
Kina da masaniyar cewa Zanirah duk sati sai an je mata an kai mata girkin Hajjah da dambun nama, gaskiya ni ba zan dawo ba”.
Ummi ta ce, “Ni babu ma abin da ya fi ban haushi irin ranar hutu, kullum mune karshen dauka bayan yunwa ta gama kwakwale mu”.
Na ce, “Abin da nake so ki gane kenan, kawai mu bude wuta mu ce mu sai Sarauniya Amina (Queen Amina College Kaduna) inda Yaya Hauwa ke aiki. Makaranta ce ta hazikai kwarai, Aunty Hauwa ta taba gaya min dan JSS 2 a Queen Amina zai iya rubuta Formal Letter ba tare da kuskure ba, duk da ba ta federal govt. ba ce”.
Ummi ta ja numfashi ta ce, “To shi kenan, sai mu bi ta kan Yaya Aliyu shi kadai zai yi mana wannan kokarin, kuma shi kadai ne zai mara mana baya, amma cewa za’a yi don muna son kusa da gida ne kawai”.
Na ce, “Ai Allah ya ga zuciyata, ni dai abin tarihi da alfahari ne a gare ni a ce na zamo daya daga cikin daliban makarantar nan mai tsohon tarihi”.
Ranar hutu muka shiga sallama da kowa kamar har mun tabbatar ba zamu dawo din ba. Bamu bar ko tsinkenmu ba, mune har da amsar address din wasu daga cikin ‘yan dakinmu da ‘yan ajinmu wadanda aka saba da juna tsayin shekaru uku.
Yaya Aliyu ya ga kaya cancarakas! Har da su loka da katifu da filallika, ya ce, “Ku lafiya? Ina za ku da wannan kayan?’
Muka kyalkyale da dariya ganin yadda ya razana, muka shiga danna kaya a but muna fadin “Mun yi graduation ne Yaya Aliyu”.
Ya ce, “Aure za ku yi?”
Muka hada baki wajen cewa, “Eh! Yaya makaranta ta ishemu aure muke sooooo!”
Ya zuba hannaye a bannet din motarsa yana fadin, “La’ilaha illallahu......”
Na ce, “Muhammadur rasulillahi.....”
Ummi ta ce, “Sallallahu alayhi wasallam”.
A kan hanya muke yi masa bayanin shawarar da muka yanke. Ya ce, “Ke dai Fa’iza ko dai don ki dinga cin abincin Aunty Hauwa ne?”
Na ce, “Wallahi a’a Yaya Aliyu, kawai ina so na zamo daya daga shahararrun daliban Sarauniya Amina wadanda tarihin Najeriya ba ya mancewa dasu (Old Student of Queen Amina College Kaduna)”.
Ya ce, “I trust you my dear sissy”.
A falon Hajjah Yaya Aliyu ya ta da zancen,ranar da muka kwana uku da komawa. Bashir da ya zo daga Kaduna ya ce, “Gaskiyar Fa’izah, don ko wannan jelen daga Giwa zuwa Gusau-Gusau zuwa Giwa ba karamin wahala bane”.
Fa’iz ya ce, “Wane irin wahala Yaya Bash? Tunda Allah ya hore abin da za a sayi man fetir din da lafiyar da za a tuka motar ba shi kenan ba? Kawai dai Fa’izah jakar yarinyar nan ka san ba son karatu take ba shine ta zuge Ummi don ita ma ta maida ta jaka kamar ta, amma ta ya ya za a ce wai Govt. School ta fi ta federal Govt. Na san don su dinga ganin Aunty Hauwa ne kurum..”
Aliyu ya yi saurin katse shi da cewa, “Ban tari hanzarinka ba Fa’eez, ban kuma ce Fa’eezah mutum ce ba jaka ba ce tunda uwarta ba A.B ba ce, don haka Fa’eezah ba mutum ba ce. Amma da ka ce wai don su dinga ganin Aunty Hauwa ne a kan me? Shin watanni nawa suke sharewa ma a nan garin ba tare da sun ziyarce ta ba ma sun taba damuwa? Ko ka taba jin tsakanin Ummi da Fa’iza wata ta taba tambayata yaushe zamu je wajen yaya Hauwa? In da ka ce Maman Kaduna to wannan sai in yarda”
Fa’iz ya kyabe baki ya ce, “Kai ai Yaya Aliyu ai dama kullum kana bayan Fa’izah, ba ta taba yin ba dai-dai ba ka kwabe ta, komi ta yi, duk hukuncin da ta yi dai-dai ne a wurinka, alhali she’s (empty-mindend)”.
Ya ce, “Yes! Fadi da babbar murya ina bayan Fa’ia a kullum, domin da ka ki da ka so FA’IZAH yarinya ce mai tunanin kanta, hikima da kaifin basira, da wuya tunanin ta in an auna shi za a ga rashin hikima a cikinsa. Kuma da kake cewa wani wai Allah ya hore kudin man fetir, to don Allah in tambaye ka, shin ka taba kashe kwandala ka sayi man ka zuba a mota ka kai ko ka dauko Fa’iza daga Gusau ko da sau daya ne? Ka taba kashe lokacinka ko da minti talatin ne ka je ka gano Fa’iza da Ummi a Gusau?
Amma Zanirah! Ka gaya mani don Allah, sau nawa kake zuwa mata visit per-term? Ko ko ka taba kawo kwandala ka basu ka ce su sayi sabulun wanka a makaranta? Amma Zanirah sau nawa kake sayen kaya ka kai mata Fa’iz! A wane dalili don Sun nemi sauyin makaranta za ka sanya baki, don haka ba damuwar ka ba ce bai shafe ka ba ina fatan ka gane?’
Fuskar Fa’eez ta yi jawur da wannan wankin babban bargo da Yaya Aliyu yai masa, ya ce, “Amma ka san ni ba wani aiki nake ba baya ga karatu, ina zan nemo kudin da zan ke musu provision har su uku, kuma su suna da nisa?”
Yaya Bashir ya ce, “Line perfect, wannan karatun naka ne kake kiran shi karatu? Wai National Diploma, amma a hakan ina kake nemo wanda kake yiwa Zanirah? Ina kake nemo wanda kake dinka sabuwar shadda duk sati? Tukunna ma, ina kake kai rabonka da ake baka na A.B family duk wata? Ban ga amfanin mutum ya tsaya yana faman cacar baki da mutumin da bai san ciwon kansa ba irin Fa’iz Bamalli....”
Hajjah ta zaburo ta ce, “Ku kun san Allah ku kiyaye ni, haka kawai kun sa min miji a gaba kuna tsiga kuna tsattsaga kamar ku kuka haifi Fa’izar da Ummin? Sai ku bari in ya zo ya ce muku yana son daya daga cikinsu sannan ku yi masa wannan gore-goren naku”.
Yaya Aliyu ya ce, “Ai shima baya fara ba, baya soma ba Hajjah, Ina! Ai alamar karfi yana ga mai kiba, kuma abin da ka yi shi za a yi maka. Makaranta ce ni Ali zan canza musu, zan ci gaba da kula da hidimarsu duka ba zan bambanta ba, ba zan fasa ba, don ni irin nawa ZUMUNCIN KENAN duka daya ake, A.B abu guda ne bana jikin-jikina kawai ba, in har ina da iko sai in ko bana numfashi Hajjah”.
Ta ce, “To Allah ya ba da sa’a, ga fili nan ga mai doki”.
Fa’iz ya ce, “Sai sukuwa Hajjah”.
Yaya Aliyu ya danna mai harara ya yi ficewarsa yana murmushin tura haushi.
Chapter 11 · 0% Book details