Sashe 13
Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Wannan ya ta da hankalin Hajjah ba kadan ba, ta yiwa Baban Kaduna maganar a kyale Fa’iz da tafiya karatun nan tunda abin ya kai ga taba lafiya.
Baban Kaduna ya ce, “Don Allah don Annabi Hajjah ki fita daga maganar nan kada kema ya kwantar mana dake, amma sai dai ya mutu na huta ganin dana yana direban tasha in dai ba zai yi yadda nake so ba”. Sai Hajjah ta yi shiru.
Cikin wani hutu da muka zo Fa’iz na shirya kayan shi cikin troller (akwatin tafiye-tafiyen bature) da muke kira (tura ni a tiles). Ummi ta yi sallama ta ba shi kaya cikin leda da Baba Na’ibi ya aiko masa ya yi guzurin tafiya.
Ganin yana loda kaya a jaka ta samu kujera ta zauna a gefensa a darare, ga mamakinta bai mata tsawa ba, bai hantare ta ba balle ya kore ta.
A hankali ta ce, “Yaya Fa’iz tafiyar kenan?”
Ya dago ya dube ta ya yi dan murmushi, “Eh, Ummi ya zan yi? Baban Kaduna ya dage. Daga nan Kaduna na nufa, daga nan mu wuce Kano inda zamu tashi ta filin jirgin Malam Aminu Kano ni da shi”.
Ummi hawaye ya cicciko idonta dai-dai sanda idonta ya kai ga wani karamin album saman kayanshi da yake hadawa. Ta dauka ta bude shafin farko ta shiga dubawa.
Shafin farko hoton Fa’iza ne ta yi tagumi jikin varanda ‘terrace’ na gidan Hajja. Shafi na biyu kyakkyawan hoton Fa’izah ne ta yi tagumi a falon Hajjah. Haka shafi na uku Fa’iza sanye da koriyar suwaita mai kauri da jan siket kanta ba dankwali, wanda hakan ya sakko da jelunan kitson (shuku) dake kanta har bisa dogon wuyanta, tana rungume da (teddy bear) a gidansu dake Zaria. Sai kusan karshe ne ta ga hotunansu da sauran kannensa duka na Giwa da na Kaduna, har da su Walida amma 80% ba album din hotunan Fa’izah ne.
A matukar mamakance Ummi ta daga ido ta dubi Ya Fa’iz hankalinshi baya kanta yana ta shirya kaya haikan. Ta zari mai rungume da Teddyn ta ce, “Hoton nan ya yi kyau Ya Fa’iz in dauka? Fa’izah ba ta san da shi ba ma sam, don Allah ina ka same shi?”
A lokacin ne ya dago ya dube ta, ya zaro ido ya ce, “Ke! Wa ya ce ki taba mani album? Ina ruwanki da kayana?” Ya fauce album din ya danna a jaka ya ja zif. Ya shiga zuba mata bala’i ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba.
Ummi dariya kamar ta kashe ta san (borin kunya ne yake nannade shi da hauka). Ta ce, “Ka yi hakuri Ya Fa’iz ban san baka so a taba ba”. Ta dauki wasu daga cikin hotunansa ta ce, “In dauki wadannan Ya Fa’iz?” Ya dube su daya bayan daya ya ce, “Me kika ce?”
Ta mike da hotunan a hannunta za ta fita, har ta kai bakin kofa ya ce, “Tsohuwa!” A kufule ta juyo don ya kirata da sunan da ta tsana a rayuwarta, amma ga mamakin Ummi sai ta ga ya yi murmushi.
“Don mi kike son hotona bayan duk kun tsane ni don kawai ina gaya muku gasiya?”
Ummi ta girgiza kai tana dariya, ta ce, “Allah Ya Fa’iz bamu tsaneka ba, daman can kai ne ka tsanemu, kuma mu har mun manta ma wallahi. Mun san kuruciya ne ga shi yanzu tunda ka shiga Poly ai baka cika shiga lamarinmu ba balle ka takura mana. Wani abin ma in aka ce ka yi ai ba za ka yi ba”.
Ya ce, “Ko? In ku kun manta ai Hussainar taku ba za ta taba mantawa ba. Domin na zalunceta na wulakanta ta na ci mata mutunci da yawa, wanda nima wallahi ban san dalili ba. Yanzu har nauyinta nake ji saboda halin RAI da muhimmancin ZUMUNCI, kunyarta nake ji wallahi-wallahi Ummi.....”
Ummi ta yi sakatoto! Tana duban sa cike da shakkar ba da Fa’izu (Abubakar) take magana ba, wani ne dai mai matukar kama da shi. Ko kuma mafarki take yi.
Ta ce, “Yaya Fa’iz wai kana nufin Fa’izah?”
Ya girgiza kai ya ce, “It may be itan, it may also be kuma ba itan ba.....”
......”Ban gane ba?” Ummi ta tambaya her voice is trembling (muryarta tana rawa).
Ya ce, “Ba za ki gane ba Ummi, kowa ma ba zai taba ganewar ba, amma Allah ya ga zuciyata na yi nadama da dana sanin abin da na yiwa Fa’izah”.
Ummi ta dan yi zuruu! Tana dubansa, ta ce, “Na tabbata na kuma hakkake cewar Fa’iza ba ta rike ka ba sam a zuci Ya Fa’iz, kullum addu’arta Allah ya shiryi Ya Fa’iz ya ganar da shi illar ‘KARYA, MUGUNTA, ZALUNCI da muhimmancin zumunci”.
Fa’iz ya dafe kai ya dubi Ummi duk idanuwansa sun sauya launi, ya ce, “Yanzu Ummi duk da wadannan sunayen Fa’izah ke kallo na? Kuma haka Ummi?” Tune din muryarshi wannan karon (in subdued) a karye.
Ita ma Ummin ta karaya a wannan gabar, ban da girgiza kai alamar, “A’a”. Ba abin da ta ce. Ya yi mata alamar ta tafi kawai ta kyale shi.
Washe gari kowa ya shirya za a tafi rakiyar Fa’iz, sai na zari mayafi na yi wuf na shige gidan Baba Barau na buya a kitchen. Neman duniya Ummi ta yi ba ta ganni ba, dole suka hakura suka shiga mota.
Daga tagar kitchen din ina hango shigar Ya Fa’iz mota, yana dan waiwaye kowacce kusurwa ta A.B Bamalli Estate kamar mai neman wani abu. Daga bisani ya shiga motar Ya Aliyu ya ja suka fita a get din.
Na yi wata irin doguwar ajiyar zuciya kamar an zare min kaya a kafa, kamar kuma an sauke dutsen Dala da Gwauron Dutse daga kaina. Na yi wata irin kakkarfar ajiyar zuciya.
****
Baban Kaduna ya ce, “Don Allah don Annabi Hajjah ki fita daga maganar nan kada kema ya kwantar mana dake, amma sai dai ya mutu na huta ganin dana yana direban tasha in dai ba zai yi yadda nake so ba”. Sai Hajjah ta yi shiru.
Cikin wani hutu da muka zo Fa’iz na shirya kayan shi cikin troller (akwatin tafiye-tafiyen bature) da muke kira (tura ni a tiles). Ummi ta yi sallama ta ba shi kaya cikin leda da Baba Na’ibi ya aiko masa ya yi guzurin tafiya.
Ganin yana loda kaya a jaka ta samu kujera ta zauna a gefensa a darare, ga mamakinta bai mata tsawa ba, bai hantare ta ba balle ya kore ta.
A hankali ta ce, “Yaya Fa’iz tafiyar kenan?”
Ya dago ya dube ta ya yi dan murmushi, “Eh, Ummi ya zan yi? Baban Kaduna ya dage. Daga nan Kaduna na nufa, daga nan mu wuce Kano inda zamu tashi ta filin jirgin Malam Aminu Kano ni da shi”.
Ummi hawaye ya cicciko idonta dai-dai sanda idonta ya kai ga wani karamin album saman kayanshi da yake hadawa. Ta dauka ta bude shafin farko ta shiga dubawa.
Shafin farko hoton Fa’iza ne ta yi tagumi jikin varanda ‘terrace’ na gidan Hajja. Shafi na biyu kyakkyawan hoton Fa’izah ne ta yi tagumi a falon Hajjah. Haka shafi na uku Fa’iza sanye da koriyar suwaita mai kauri da jan siket kanta ba dankwali, wanda hakan ya sakko da jelunan kitson (shuku) dake kanta har bisa dogon wuyanta, tana rungume da (teddy bear) a gidansu dake Zaria. Sai kusan karshe ne ta ga hotunansu da sauran kannensa duka na Giwa da na Kaduna, har da su Walida amma 80% ba album din hotunan Fa’izah ne.
A matukar mamakance Ummi ta daga ido ta dubi Ya Fa’iz hankalinshi baya kanta yana ta shirya kaya haikan. Ta zari mai rungume da Teddyn ta ce, “Hoton nan ya yi kyau Ya Fa’iz in dauka? Fa’izah ba ta san da shi ba ma sam, don Allah ina ka same shi?”
A lokacin ne ya dago ya dube ta, ya zaro ido ya ce, “Ke! Wa ya ce ki taba mani album? Ina ruwanki da kayana?” Ya fauce album din ya danna a jaka ya ja zif. Ya shiga zuba mata bala’i ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba.
Ummi dariya kamar ta kashe ta san (borin kunya ne yake nannade shi da hauka). Ta ce, “Ka yi hakuri Ya Fa’iz ban san baka so a taba ba”. Ta dauki wasu daga cikin hotunansa ta ce, “In dauki wadannan Ya Fa’iz?” Ya dube su daya bayan daya ya ce, “Me kika ce?”
Ta mike da hotunan a hannunta za ta fita, har ta kai bakin kofa ya ce, “Tsohuwa!” A kufule ta juyo don ya kirata da sunan da ta tsana a rayuwarta, amma ga mamakin Ummi sai ta ga ya yi murmushi.
“Don mi kike son hotona bayan duk kun tsane ni don kawai ina gaya muku gasiya?”
Ummi ta girgiza kai tana dariya, ta ce, “Allah Ya Fa’iz bamu tsaneka ba, daman can kai ne ka tsanemu, kuma mu har mun manta ma wallahi. Mun san kuruciya ne ga shi yanzu tunda ka shiga Poly ai baka cika shiga lamarinmu ba balle ka takura mana. Wani abin ma in aka ce ka yi ai ba za ka yi ba”.
Ya ce, “Ko? In ku kun manta ai Hussainar taku ba za ta taba mantawa ba. Domin na zalunceta na wulakanta ta na ci mata mutunci da yawa, wanda nima wallahi ban san dalili ba. Yanzu har nauyinta nake ji saboda halin RAI da muhimmancin ZUMUNCI, kunyarta nake ji wallahi-wallahi Ummi.....”
Ummi ta yi sakatoto! Tana duban sa cike da shakkar ba da Fa’izu (Abubakar) take magana ba, wani ne dai mai matukar kama da shi. Ko kuma mafarki take yi.
Ta ce, “Yaya Fa’iz wai kana nufin Fa’izah?”
Ya girgiza kai ya ce, “It may be itan, it may also be kuma ba itan ba.....”
......”Ban gane ba?” Ummi ta tambaya her voice is trembling (muryarta tana rawa).
Ya ce, “Ba za ki gane ba Ummi, kowa ma ba zai taba ganewar ba, amma Allah ya ga zuciyata na yi nadama da dana sanin abin da na yiwa Fa’izah”.
Ummi ta dan yi zuruu! Tana dubansa, ta ce, “Na tabbata na kuma hakkake cewar Fa’iza ba ta rike ka ba sam a zuci Ya Fa’iz, kullum addu’arta Allah ya shiryi Ya Fa’iz ya ganar da shi illar ‘KARYA, MUGUNTA, ZALUNCI da muhimmancin zumunci”.
Fa’iz ya dafe kai ya dubi Ummi duk idanuwansa sun sauya launi, ya ce, “Yanzu Ummi duk da wadannan sunayen Fa’izah ke kallo na? Kuma haka Ummi?” Tune din muryarshi wannan karon (in subdued) a karye.
Ita ma Ummin ta karaya a wannan gabar, ban da girgiza kai alamar, “A’a”. Ba abin da ta ce. Ya yi mata alamar ta tafi kawai ta kyale shi.
Washe gari kowa ya shirya za a tafi rakiyar Fa’iz, sai na zari mayafi na yi wuf na shige gidan Baba Barau na buya a kitchen. Neman duniya Ummi ta yi ba ta ganni ba, dole suka hakura suka shiga mota.
Daga tagar kitchen din ina hango shigar Ya Fa’iz mota, yana dan waiwaye kowacce kusurwa ta A.B Bamalli Estate kamar mai neman wani abu. Daga bisani ya shiga motar Ya Aliyu ya ja suka fita a get din.
Na yi wata irin doguwar ajiyar zuciya kamar an zare min kaya a kafa, kamar kuma an sauke dutsen Dala da Gwauron Dutse daga kaina. Na yi wata irin kakkarfar ajiyar zuciya.
****