← Book details Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 98

Sashe 24

Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

[11/02 9:41 PM] Sumayya Takori: ZUMUNTAR KENAN 2
Washe gari muka raka Momi bikin walimar ‘yar aminiyarta Dacta Ladi, cikin Tudun-Wada. Lancin din da aka yi na ‘yammata a (Congo Conference) ya taimaka ainun wurin rage mana damuwa dukkanmu, kowaccenmu ba ta dawo haka ba sai da saurayi. Suka biyo mu har gida, Momi ce ta lallabasu ta ce su dawo gobe lokacin magariba ta yi ido na ganin ido ya fi. Washe gari kuwa da safe muka tattara muka koma Kaduna.
Har muka kare satin ni da Zanirah kowanne ya kasa sakin jiki da dan’uwansa. Abin da bamu taba tunani ko a mafarki zai taba faruwa a rayuwarmu ba. Kai SO din nan bala’i ne, masifa ne ba karama ba tunda har ya iya farraka (shiga tsakanin) ni, Ummi da Zanirah.
Ranar da zamu koma makaranta mun shirya tsaf cikin uniform. A bakin gate zan shiga motar Baban Kaduna ya ajiye ni makaranta, ita kuma za ta shiga school bus direban Baban ya maida ta Giwa (GGSS Giwa) sai ta riko hannuna. Ta matse gam cikin nata, hawaye ya fito daga idanunta ta yi azamar dauke su da yatsunta.
Ta ce, “Fa’izah ki fidda damuwar dake damun ranki ki yi (facing final exams) dinki yadda ya kamata, wannan ce damarmu ta karshe ta gina (future) dinmu, kada mu bari abin da bai kaita muhimmanci ba ya rushe”.
Na murmusa ina kokarin mai da nawa hawayen na ce, “And you too Zanirah!”
Amma a zuciyata cewa nake, “Kin manta ne Zanirah, an ce “LOVE IS OVERALL!”
To haka rayuwar ta kasance mana ba dadi a makaranta ma, kullum zullumina kammaluwar jarrabawarmu, isowar karshen karatun nan.
Gab da zamu zana JAMB na shiga samun katunan fatan alkhairi daga Yaya Aliyu masu dauke da kalamai masu karfafa zuciya tare da kwantar da hankali.
A kalamanshi ya fi ambata ‘nasararki na nufin nasarata, kwanciyar hankalinki shine tushen samun nasarar, nasara ba ta zuwa da sauki, nasara sai an sha gwagwarmaya ake samun ta. Soyayyar da ba a samu tangarda ko bambance-bambancen ra’ayi ba, ba ta kai wa gaci.
Fa’izah ki sa a ranki ba zamu yi aure bane kawai in dama tun fil azal Allah ya rubuta ba zamu yin ba”
Wannan kwarai ya taimaka min wajen samun nutsuwa na zana jarrabawar JAMB lafiya cikin kyakkyawan zaton samun kyakkyawan sakamako, wanda zai fitar dani kunyar iyaye da masoyana.
Tsakanina da Ummi sai kallo da ido in an haxu a hanya, haka nan kunnuwana basa huta jiye min irin sakonnin da take samu daga Fa’iz akai-akai ba. Daga bakin Naja’atu da Haulatu. Tare da tabbatar min Ummi ta yi nisa a son Fa’iz ta yadda za ta iya batawa da kowa ma a duniya bani ba, don haka in daina tunanin zan iya hanata ko zan rinjayeta ta bi ra’ayina.
Yaya Aliyu ya kawo mana ziyara muna wata biyu da dawowa, bai fi saura sati uku mu kammala makaranta ba kenan. Hankalina ya yi mugun tashi da ganin yadda Aliyuna ya koma kashi da rai, ido a lungu, dama jikinsa fyalan-fyalan babu kwari haka yake, dogon Bamalle mai suffa irin ta Baba Na’ibi.
Baki a bude nake tambaya “Shin Ya Aliyu ulcer din ta kwantar da kai ne bamu nan?”
Ya girgiza kai ya ce, “Ko daya Fa’izah. Illah Hajjah da Baban ABU dake neman zauta ni. Hajjah ta rantse ta kuma ta rantse ba ta san zancena dake ba, ba kuma za ta yi miki aure yanzu ba.....”
A tsaye nake amma sai ji na na yi ragwaf, na yi zaman rakuma a gaban Yaya Aliyu. Idanuna ke fitar da wasu irin hawaye amsu zafi da yaji da ban taba fitar da irinsu a rayuwata ba, a yayin da nake cewa, “Ni kam Yaya Aliyu na hakura, ba zan iya jayayya da Hajjah ba, na hakura har ga Allah.
Dama an ce duk soyayyar da ta yi tsayi irin haka da kyar ne take kai labari.... Na hakura..... ko ba komai ba zan yi bakin ciki ba don ka auri ‘yar’uwata jinin jikina Zanirah ba..... ina da yaqinin ban barka a hannun da zan yi tararrabi ba, you are in safe hands, domin Zanirah nice, ni Zanirah ce, babu bambanci daga kamanni da halayya, sai ma wanda ta fini. Zan so ka yi farin cikin jin cewa Zanirah na matukar son ka, irin son da tunaninka bai taba baka ba......”
Ya katse ni cikin tsawa..... “Fa’izah baki da hankali? Kina hauka ne, kina so ki kashe ni ne? Shekaru goma sha biyu da na kwashe ina dakon soyayyarki, dai-dai da rana daya zuciyata ba ta taba hutawa ba da azabar soyayyarki da abin da za ki saka mini kenan wai kin barwa wata ni?”
Na sunkuyar da kai kasa yayin da hawayen suka sunce a kundukukina suna rige-rigen tadda kasa, aguje suke bulbula wani na bin wani suna masu tuna mini kaunar da Yaya Aliyu ya shekara nuna mini.
Wahala wadda uwa da uban da suka haife ni basu yi min kwatankwacinta ba in an dauke hakkin haihuwa. Duk da bai ambaci wahalar da ya sha a kaina ba sai ‘kauna’ da ‘soyayya’ ya zama dole ni din in tuna da wannan.
To amma babu abin da zan iya a ciki. Tsana ga Zanirah ko kuwa kin biyayya ga Hajjarmu? Gyatumar da iyayenmu ma basa tsallake umarninta?
Ina mai girgiza kai a gaggauce na rarrafa ga Yaya Aliyu yayin da na kama tafin kafarshi ina kuka, na ma manta a cikin ofishin vice muke, ina fadin “Ka yi hakuri Yaya Aliyu, ya ya kake so in yi toh? Kana nufin in baka hadin kai mu yi butulci ga Hajjah da Baban Kaduna da Mama Asma’un da ta tsuguna ta haifi Zanirah amma ta fifitani a kanta? Ko ko Hajjar da ta sha wahalarmu, wahalar da iyayenmu basu sha ta ba? Ba zan iya ba! Ka yafe ni Yaya Aliyu!!
Na san ka so ni, ka bautu a son da kaunata tsayin shekaru, to haka Zanirah ma ta kwashe shekaru tana begen zama a muhalli na. Na tabbata za ta yi maka biyayya fiye dani tunda son ta ya rinjayi naka. Sanin kanka ne Zanirah mutum ce mai sanyi da saukin hali, nutsuwa da hankali tamkar kai, it must surely be a perfect match as usual within A.B family. Nima Allahu ya bani gwarzon miji tamkar kai mai hali da aqida da kamannin Yaya Aliyu. Kundin shafukan rayuwata will be incomplete without the scenes of Yaya Aliyu.....”
Na juya ina tafiya da baya-baya ina masa murmushi ga hawaye na bulbula. Aliyu bai iya ya ce mani komi ba illa buga hannuwanshi duka a jikin garu (bango) ya kifa kai a jikinsu yana rusar kuka, kukan da bai taba yi a rayuwarshi ba, kukan da wani namiji kwatankwacin Aliyu dai bai taba yi a kan mace ba......
“Hajja kin cuce mu..... kin yanke mana buri a dab da wa’adin cikarsa..... kin guntile ingantacciyar soyayyar da aka dasa ake mata ban ruwa ta yi yado ta ba da yabanya ana gab da cin amfaninta..... Anya zamu iya yafewa Hajjah? Meye amfanin soyayyar da take nuna mana tunda a karshe cuta take zama? Babu!!
(Rabuwar mu da Yaya Aliyu kenan).

****
Na yi matukar kokarin ganin na manta da Yaya Aliyu, na fidda son Aliyu a raina, na yi kukan, na yi addu’ar, amma a kullum son Yaya Aliyu ke dawo min danye jagab, sabo fil a zuciya.
Meye sauran farin-cikin ne a yanzu a zama a A.B House a yanzu ni Fa’izah! Ummi mun rabu saboda Fa’iz, Zaneerah mun rabu saboda Aliyu, shin me zan koma in yi a Giwa? In ina da zuciya kare bai cinye ta ba daga yau na bar Hajjah Hadiza Giwa, zan koma gidanmu, ko da uwata da ubana za su kasheni ne tunda Hajja ba ta so na. Zanirah da Fa’izu ta fi so tuntuni.
Wannan haka yake ‘ya’yan Baban Kaduna take so, domin shine mai kudi, shine mai huce takaici, wato masu gidan rana. Yana kaita Hajji duk shekara ko ya ya ne? Shin ma wai me nake tsinta a kauyen Giwa ne da babu a Zaria? Zariar ma muhalli irin (Area One). Ba komai bane illa sabo da su Ummi. Tunda rayuwar ta zo da guguwar sauyi kowa ya koma gaban uwa da uban shi.
Yaya Aliyu! Yaya Aliyu!! Yaya Aliyu!!!
A kullum na tuno irin soyayyar da muka gudanar, a gaba dayan tsayin rayuwarmu, kulawar da ya yi mini, wahalar da ya sha a kaina, sai na yi kuka na gode Allah. Hawayena sun kafe, na kama kukan tunkiya, wanda babu hawaye sai sauti.
Babu abin da ya firgita ni kamar migraine (ciwon kan barin kai guda) da ya same ni a kowanne dare, ga wani zazzabi-zazzabi mai zafin gaske da nake kwana da shi da safe ya wartsake. Ban karanta ba, amma na kan ji an ce wadannan alamu ne na ciwon hauhawar jini (hypertention).
Chapter 24 · 0% Book details