← Book details Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 42 OF 98

Sashe 42

Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

****

WANE NE NAZIRU GALADANCHI?
Major General Sani Galadanchi shine mahaifin Dr. Nazir. Da na farko wurin iyayenshi, kamin haihuwar shi sun kwashe shekaru masu tsaho basu samu haihuwa ba. Da Allah ya kawo Naziru sai hakan ya zamo musabbabin nuna mishi tsantsar gata wanda babu kwaba ko tsawatarwa a cikin sa.
Nazir ya tashi yaro dan hutu tun yana sakandire, sune samarin da ake kira ‘yan (high life) a lokacinsu. Haka nan bayan haihuwar Nazir sai da suka kwashe shekaru takwas zuwa tara kafin su samu haihuwar Haulatu. Daga Haulatu yara ne maza uku daya na bin daya duk bayan shekaru uku.
Duk da jin dadi da sakewar da Nazir ke samu bai sa shi yin wasa da karatu ba, domin ya ga amfanin ilimin wurin mahaifinshi. Ya so ya tafi soja don ya gaji ubansa amma Baban ya dage kan harshen Larabci yake son ya karanta, baya son shi da aikin soja, babu kwanciyar hankali a cikinsa.
Su shan sigari wannan duk a wurin Larabawa ya koya, sai dai sam in ya zo hutu baya sha a gida sai ya koma. Bai fara neman mata ba sai da ya kammala degree ya fara masters a zuwan shi bautar kasa garin Lagos, inda ya yi wani aboki Tim ya koyar da shi mu’amala da mata, don haka da ya koma Taiwan sai idonshi ya bude da hakan.
A can ya kammala PHD ya dawo Kano ya fara aikin da yake yi a Bayero. Rasuwar Tim ta hanyar muguwar cutar (SIDA) Aids bai sanya Nazir Sani kintsuwa ba sai haduwar shi da Fa’izah A.A Giwa.
Bai taba neman kowacce diya mace da niyar aure ba sai a kan Fa’iza, kamar yadda bai taba son wata diya mace tsakani da Allah ba baya ga Fa’izah. Bai taba tunanin zai bar yaudarar mata ba sai a kan Fa’izah. Daga ranar da ya dora ido a kanta, bai kara kula wata yarinya da sunan iskanci ko yaudara ba, domin yana ganin kintsattsiyar yarinya kamar Fa’izah ba ta dace da watsattsen miji kamar shi ba.
Don haka ya kimtsa kansa, tun hakan bai zamo dalilin da za a hanashi Fa’izah ba. Tunda ya tabbatarwa kansa aurenta zai yi domin Allah da soyayya.
Ya yarda ya amince da duk zargin da ake masa na cewa shi din dan iska ne, ya yarda ya kuma amince bai taba musantawa ba, kamar yadda bai taba cewa yana da wani hali na kirki ba. To amma wanda duk yake tarayya ta jiki da Naziru Sani, zai yi shaidar cewa mutum ne wanda baya wasa da sallah, kuma zuciyarsa daya ce da ita yake zaune da kowa, sannan ba shi da tsoro. Baya tsoron uban kowa, sannan abin hannunshi bai rufe mishi ido ba sam.
Daga ranar da suka yi magana da Abdullahin Haulatu, ranar ba ta zagayo ba sai da Dr. Nazir ya gabatar da maganar Fa’izah ga iyayenshi, ya kuma roke su da aje mishi neman auren ta sati mai kamawa.
Hajiyar su Haulatu ta yi matukar farin ciki da Allah ya nuna mata ranar da Nazir ya kawo mata zancen aure da bakinsa da ranta kafin mutuwar ta. ‘Yammata iri-iri ta sha nemawa Naziru yana fitittikewa, shi aure ba yanzu ba sai ya ci lokacinsa matarshi ma ba a haife ta ba.
Da farin cikinta da rawar jikinta ta isar da sakon Nazir ga General, shima ya yi farin ciki sosai, suka yi ta yiwa Allah godiya. Tabbas addu’ar iyaye ba ta faduwa kasa banza a kan ‘ya’yansu, ko ba jima ko ba dade.
A washegari ya tura kanin mahaifinsa da kanensa biyu da wan Hajiyarsu wurin iyayen Fa’izah. Haulatu ce ta ce dasu Kaduna za su wurin Alh. Muntari don shine madaurin auren su, ta karbi address wurin Aunty Rabi.
Tarba ta girma da mutunci Mama ta yiwa iyayen Nazir ita da Baban Kaduna da suka ce daga Kano suke neman auren Fa’iza wa dansu Naziru, malami a inda Fa’izar take karatu. Sai mama ta kalli Baban Kaduna shima ya kalle ta aka rasa mai yin magana.
Tun daga nan jikin dattijan ya fara sanyi. Da kyar Baban Kaduna ya ce, “Na yi mamaki da kuka zo neman aure ba tare da kun yi bincike a kan gidan su yarinyar ba. Ban da haka duk wanda ya san zuri’ar Abubakar Giwa, ya san basa auren bare. Ban fadi haka don yaron wajena ne mijin Fa’izah ba, sai don cewa ka’idar gidanmu kenan da muke bi tun iyaye da kakanni. Ina mai bai ma Naziru hakuri, ya yi hakuri, ya yi hakuri Fa’izah TA YI AURE!!!”
Da wannan bakin labari Hajiyar Dr. N ta tare shi a dawowarsa daga wajen aiki. Labarin da ya yi masa bugun da wani labari bai taba yi masa ba. Ya dauki mukullin motarshi ya nufi kofa Hajiyarsa na kira, bai juyo ba yake fadin “Barni in je Hajiya, Giwan za ni in tambayi Fa’izah dalilin da yasa ni ban yaudareta ba ita ta yaudare ni...... ta san auren gida ake musu amma ta yi min haka.... me na yiwa Fa’izah da za ta zabi ta yi min wannan yankan kaunar ta yi dai-dai da zuciya da farin ciki na?”
Gudun da yake shararawa a kan titin da zai kai shi garin Giwa ya fi kama da na ‘yan sumogal. Zagin duniya ya sha shi daga motocin gaban shi da bayanshi. A dai-dai kwanar da zai karya ya shiga Giwa suka yi arangama da motar shanu ta bi ta kan motarsa ta murkusheta irin murjewar da sai wani babban ikon Allah za a fidda mai rai a cikinta.

****
Chapter 42 · 0% Book details