Sashe 17
Zumuntar Kenan Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
****
A shekarar aka nada wakilan malamai bayan tafiyar ‘yan aji shida, na yi mamaki matuka da aka kira ni Fa’izah Ahmad Bamalli Giwa a matsayin AMIRA! Aka kuma nada Ummi Gate Prefect. A hostel su Naja’atu Room-mates din mu ke yiwa Ummi dariya, domin ita Naja ta amshi dankwalin Head-Girl ne, ya yin da Haulatu Sani ta karbi Labour Prefect..
Ummi ta ce, “Aikin kawai, a rasa dankwalin da za a baiwa mutum sai na bakin kofa? Wani ya ce ina son mukami da za a hadani da gate?”
Muka tuntsire mata da dariya. Haulatu ta ce, “Khadija Sabi’u ke ce baki sani ba, cika idonki ya sanya (Vice-Principal) baki wannan dankwalin, don kin san an ce alamar karfi na ga mai kiba, ta san za ki yi fada (Ummi na da jiki sosai) ga masu yin latti da ‘yan komawa hostel during school hours. Zaki cikawa dalibai masu latti ido da kwarjini. Yawancin mata masu jiki fada gare su”.
Ummi ta yi tsaki ta ce, “A kan me za a bawa Fa’iza Ameerah? Wa ta fi tsoron Allah? Yarinya mai shegiyar tsiwar tsiya”. Naja ta ce, “Ai kuwa Fa’izah ta cancanci dankwalinta. Dalili;
-Duk da ta fimu nutsuwa da kula da addini.
-Zuwa jam’i a kan lokaci.
-Tun zuwanta Sarauniya Amina kullum sai ta share masallaci.
-Ita take riga kowa zuwa masallaci da asubah.
-Ta fi kowa iya Larabci, ta fi kowa iya karatun Alkur’ani, ta fi kowa iya kira’a da Tajweed. In ba a baiwa Fa’iza Ahmad ‘Amira” a makarantar nan ba ki gaya min wa za a bawa?”
Bakin Ummi ya mutu. Naja’atu ta ci gaba da cewa.
“Duk fadin Sarauniya Amina babu mai tsantseni da addini irin Fa’izah”.
Ummi ta ce, “Tana takurawa kanta ne kawai. Duk sanyi ba ta jin sa sai ta je masallaci da asuba. Da rana baka huta ba, da yamma baka huta ba haka dare. Ai ba zuwa masallaci yin sallah ne ke sanyawa Allah ya karbi sallarka ba”.
Haulatu ta ce, “Kin yi kuskure Khadija, duk taku daya zuwa masallaci lada ne da babu wanda ya san adadinsa sai sarkin sarakunan dake ba da shi. Sannan sallar jam’i ladanta ya ninka ta mutum daya, ko taka ba ta yi kyau ba Ubangiji zai duba ta na kusa da kai ya baka ladan, ai ba ma za a kwatanta ba. Kiwa ce kawai take damunmu Allah ya yaye mana”.
Ni dai ban tanka musu ba har suka gaji suka watse.
Washe gari Yaya Hauwa ta zo har ajinmu ta shigo da kaya a leda da wasika, ta ce, “In bai wa Ummi daga Fa’iz, jiya su Hajjah suka dawo Ukrain, sauran kayan bai yiwuwa a kawo su makaranta, in mun koma gida ta gani”.
Na ce, “Ayya! Yaya Hauwa da kin mika mata ajinsu don ni za ta bari da daukar kayan zuwa hostel”.
Yaya Hauwa ta yi dariya ta ce, “Ahaf! Na manta fa kayan da suka fito hannun Fa’iz-Abubakar ne, abokin fadan Fa’izah. Ya kamata ki yafi dan ‘uwanki haka girma ya hau ku ku manta kuruciyar baya, haka nan ‘yan’uwa kuke”.
Na yi dariyar yake kawai. A raina na ce, “Meye zai kankare kiyayyar Fa’iz a zuciyata? Wallahi babu shi Yaya Hauwa! Fa’iz bai so na, bai son mahaifiya ta, bai ganin girmanta balle darajarta, ya ya kuwa za ayi in taba shiri da shi a rayuwata??? Mu dai irin tamu ZUMUNTAR KENAN!
Na shigo dakinmu a gajiye tikis na ajiye (school bag) na zauna gefen gadona ina sabule socks (safar) kafa ta, na fada bayi na dan watsa ruwan sanyi a jikina, kasancewar ana tsakiyar yanayin zafi karshen watan Yuli.
Na fito na sanya riga da wando na yadin (house wear) dinmu na dan kishingida ina hutawa. Ummi ta shigo da gudu-gudu da kaya da takarda ta fado min a jiki tana shesshekar wata irin dariyar farin ciki, ta kara min takarda a fuska bayan ta zube kayan a gadona.
Sassanyan kamshin da takardar ke yi na turaren ‘Philips Lumea’ na daxe ban ji kwantaccen kamshi irisa ba, tun can wani lokaci mai tsayi da ya shude. Na lumshe gajiyayyun idanuwana a hankali na janye hannunta da takardar daga fuskata na dube ta cikin mutuwar jiki da ta zuciya gaba daya.
Ta kwanta kusa dani fuskarta dauke da annurin farin ciki da zumudi bayyanan ne, irin dai wanda kika sani a duk lokacin da wata zuciya ma’abociyar bege ta samu sakon masoyinta bayan lokaci mai tsaho.
Haulatu da Naja suka shigo suka zazzauna a gadon Ummi dake fuskantar nawa, daidai lokacin da Ummi ke fitar da kayan ledar da ta shigo da ita da Yaya Hauwa ta bani in ba ta na ki karbowa.
Littafin zane ne irin wanda su Ummi ke amfani dasu, alkaluman zane, penti kala-kala ‘yan waje da agogon hannu (hand-wrist watch) samfurin (L’OREAL) ruwan silver da zobe shima na silver dandasheshe mai kyau. Ummi ta sanya a yatsanta babban ya yi mata cif duk yadda ta juya hannunta sai ‘dot’ din zoben ya yi walainiya.
Ta rungume su Haulatu tana dariyar dadi gani kashe ni. Haulatu ta ce, “Hala sakon Yaya Fa’izu ne da kullum ake bamu labari mai cin zalin Fa’izah?” Ummi murna take, bakin ya gaza rufo, ta zaro hotuna cikiin ambulan din wasikar jikinta na rawa da karkarwa ta bude suka fara gani.
Kyakkyawa Fa’iz Giwa ne sanye cikin jibgegiyar rigar leda mai kare sanyi wadda ta sauko har gkwiwarsa, yana tsaye cikin dusar kankara baka ganin komai jikinsa sai fuskarsa, domin hatta hannayensa cikin bakaken safar hannu suke.
Hoto na biyu sanye yake cikin uniform na masu koyon tukin jirgin sama cikin karamin jirgi (jet) da wasu abokan karatunshi farare da bakake. Fuskarshi ta fi fitowa a wannan din sosai. ‘Yammatan uku suka ci gaba da kallon hotunan guda biyu suna kada kai kamar kadangaru, da kyar Naja’atu ta iya bude baki ta ce, “Khadija Yaya Fa’iz din ne?”
Ummi ta rungume hotuna cikin lumshe ido ta ce, “Yes, Fa’iz Bamalli kenan Naja’atu. Yau kinga yayanmu Fa’iz, tabbas Ya Fa’iz ne. Ni kaina ya canza min sosai fiye da yadda na san shi. Ya Fa’iz ya kara kyau kwarai, ya yi kiba da haske, ya kuma kara girma cikin shekaru uku kacal, kai abin da mamaki”.
Haulatu ta ce, “Amman yana da kyau fiye da ku duka, ko in ce fiye da dukkan zuri’ar A.B da na sani. Na so a ce yadda yake da kyau yana da mahadin sa wato kirki, amma kyau ba hali kyawun dan maciji ne Khadija”. (Can da jimawa Ummi ta sha basu labari na da Fa’iz tun daga kuruciya da rashin kirkinsa garemu).
Ummi ta yi murmushi kawai, ta ce, “Haule yadda kika ji labarin Yaya Fa’iz da Fa’izah ne kurum ya sanya kika fassara shi da haka, amma yana da kirki in his own unique way! Da za ki ganshi a zahiri rantsewa za ki yi ba zai ko kusa da taba iya aikata abin da yake aikatawa ba. Ni kadai na fahimci Fa’iz ciki da waje, zan iya rantsewa babu wanda ya kai ni sanin Ya Fa’iz a gidanmu, akwai dalilin da yasa Fa’iz yake kyarar Fa’iza wanda babu wanda ya sani sai shi daya sai Allah da ya halicce mu.
Amma wallahi ba gundarin halinshi kenan ba, koma da halinshi ne ni Ummi Khadija INA SON SHI HAKA! Zan iya jure kowane irin halinshi idan na yi sa’ar samun shi a matsayin miji. Ina son sa da yawa Haulatu, kamar yadda na fahimci shima yana sona kawai ba zai furta bane ko ya nuna kamar yadda Yaya Aliyu ke nuna ma Fa’izah. Ban san ina son shi ba Haule sai ranar da zai tafi”.
Ta yi shiru tana kallon yatsar kafarta kafin ta yi murmushi a hankali ta ce, “Wannan ya faru ne a dalilin babu auren na-gani-ina so cikin zuri’armu da family dinmu duka, sama da komai Fa’iz daban ne wajen halayya da dabi’a. Wanda zai ce miki ya san dukkan halinshi wallah ya fadi karya, saboda kullum sabon hali yake sakewa tamkar wahainiya mai canza launi daga wannan zuwa wannan. Irin wadannan mutanen ma’abota kaskantar da kansu ga abin da zuciyarsu ke matukar so tsiraru ne a cikin al’umma!”
Ta girgiza kai. Su kuma kamar masu daukar darasin tarihi, sai gyada kai suke, don haushi kamar na hada kawunan nasu su duka ukun na gwara, da suka tsaya suna sauraren shirmen Ummi da ba ta san inda ke mata ciwo ba.
Ta ci gaba da cewa, “Ni dai ku tayani addu’a Allah yasa Hajjah ta hadamu ni da Fa’iz, don in ba Yaya Fa’iz ta bani ba? Bana jin zan iya aure a rayuwata. Na gwammace in mutu haka nan ban yi aure ba. Zan jirayi Fa’iz ko da shekaru nawa zai yi bai dawo daga Ukrain ba in dai har Hajjah ba ta yi tunanin aurar dani ga wanin shi ba”.
A hankali na juyo da kaina sashen da su Ummi ke zaune, na dube ta tsaf. Shin mafarki nake ko ko a farke (idona biyu)? UMMI NA SON FA’IZ, FA’EEZ NA SON UMMI?
A shekarar aka nada wakilan malamai bayan tafiyar ‘yan aji shida, na yi mamaki matuka da aka kira ni Fa’izah Ahmad Bamalli Giwa a matsayin AMIRA! Aka kuma nada Ummi Gate Prefect. A hostel su Naja’atu Room-mates din mu ke yiwa Ummi dariya, domin ita Naja ta amshi dankwalin Head-Girl ne, ya yin da Haulatu Sani ta karbi Labour Prefect..
Ummi ta ce, “Aikin kawai, a rasa dankwalin da za a baiwa mutum sai na bakin kofa? Wani ya ce ina son mukami da za a hadani da gate?”
Muka tuntsire mata da dariya. Haulatu ta ce, “Khadija Sabi’u ke ce baki sani ba, cika idonki ya sanya (Vice-Principal) baki wannan dankwalin, don kin san an ce alamar karfi na ga mai kiba, ta san za ki yi fada (Ummi na da jiki sosai) ga masu yin latti da ‘yan komawa hostel during school hours. Zaki cikawa dalibai masu latti ido da kwarjini. Yawancin mata masu jiki fada gare su”.
Ummi ta yi tsaki ta ce, “A kan me za a bawa Fa’iza Ameerah? Wa ta fi tsoron Allah? Yarinya mai shegiyar tsiwar tsiya”. Naja ta ce, “Ai kuwa Fa’izah ta cancanci dankwalinta. Dalili;
-Duk da ta fimu nutsuwa da kula da addini.
-Zuwa jam’i a kan lokaci.
-Tun zuwanta Sarauniya Amina kullum sai ta share masallaci.
-Ita take riga kowa zuwa masallaci da asubah.
-Ta fi kowa iya Larabci, ta fi kowa iya karatun Alkur’ani, ta fi kowa iya kira’a da Tajweed. In ba a baiwa Fa’iza Ahmad ‘Amira” a makarantar nan ba ki gaya min wa za a bawa?”
Bakin Ummi ya mutu. Naja’atu ta ci gaba da cewa.
“Duk fadin Sarauniya Amina babu mai tsantseni da addini irin Fa’izah”.
Ummi ta ce, “Tana takurawa kanta ne kawai. Duk sanyi ba ta jin sa sai ta je masallaci da asuba. Da rana baka huta ba, da yamma baka huta ba haka dare. Ai ba zuwa masallaci yin sallah ne ke sanyawa Allah ya karbi sallarka ba”.
Haulatu ta ce, “Kin yi kuskure Khadija, duk taku daya zuwa masallaci lada ne da babu wanda ya san adadinsa sai sarkin sarakunan dake ba da shi. Sannan sallar jam’i ladanta ya ninka ta mutum daya, ko taka ba ta yi kyau ba Ubangiji zai duba ta na kusa da kai ya baka ladan, ai ba ma za a kwatanta ba. Kiwa ce kawai take damunmu Allah ya yaye mana”.
Ni dai ban tanka musu ba har suka gaji suka watse.
Washe gari Yaya Hauwa ta zo har ajinmu ta shigo da kaya a leda da wasika, ta ce, “In bai wa Ummi daga Fa’iz, jiya su Hajjah suka dawo Ukrain, sauran kayan bai yiwuwa a kawo su makaranta, in mun koma gida ta gani”.
Na ce, “Ayya! Yaya Hauwa da kin mika mata ajinsu don ni za ta bari da daukar kayan zuwa hostel”.
Yaya Hauwa ta yi dariya ta ce, “Ahaf! Na manta fa kayan da suka fito hannun Fa’iz-Abubakar ne, abokin fadan Fa’izah. Ya kamata ki yafi dan ‘uwanki haka girma ya hau ku ku manta kuruciyar baya, haka nan ‘yan’uwa kuke”.
Na yi dariyar yake kawai. A raina na ce, “Meye zai kankare kiyayyar Fa’iz a zuciyata? Wallahi babu shi Yaya Hauwa! Fa’iz bai so na, bai son mahaifiya ta, bai ganin girmanta balle darajarta, ya ya kuwa za ayi in taba shiri da shi a rayuwata??? Mu dai irin tamu ZUMUNTAR KENAN!
Na shigo dakinmu a gajiye tikis na ajiye (school bag) na zauna gefen gadona ina sabule socks (safar) kafa ta, na fada bayi na dan watsa ruwan sanyi a jikina, kasancewar ana tsakiyar yanayin zafi karshen watan Yuli.
Na fito na sanya riga da wando na yadin (house wear) dinmu na dan kishingida ina hutawa. Ummi ta shigo da gudu-gudu da kaya da takarda ta fado min a jiki tana shesshekar wata irin dariyar farin ciki, ta kara min takarda a fuska bayan ta zube kayan a gadona.
Sassanyan kamshin da takardar ke yi na turaren ‘Philips Lumea’ na daxe ban ji kwantaccen kamshi irisa ba, tun can wani lokaci mai tsayi da ya shude. Na lumshe gajiyayyun idanuwana a hankali na janye hannunta da takardar daga fuskata na dube ta cikin mutuwar jiki da ta zuciya gaba daya.
Ta kwanta kusa dani fuskarta dauke da annurin farin ciki da zumudi bayyanan ne, irin dai wanda kika sani a duk lokacin da wata zuciya ma’abociyar bege ta samu sakon masoyinta bayan lokaci mai tsaho.
Haulatu da Naja suka shigo suka zazzauna a gadon Ummi dake fuskantar nawa, daidai lokacin da Ummi ke fitar da kayan ledar da ta shigo da ita da Yaya Hauwa ta bani in ba ta na ki karbowa.
Littafin zane ne irin wanda su Ummi ke amfani dasu, alkaluman zane, penti kala-kala ‘yan waje da agogon hannu (hand-wrist watch) samfurin (L’OREAL) ruwan silver da zobe shima na silver dandasheshe mai kyau. Ummi ta sanya a yatsanta babban ya yi mata cif duk yadda ta juya hannunta sai ‘dot’ din zoben ya yi walainiya.
Ta rungume su Haulatu tana dariyar dadi gani kashe ni. Haulatu ta ce, “Hala sakon Yaya Fa’izu ne da kullum ake bamu labari mai cin zalin Fa’izah?” Ummi murna take, bakin ya gaza rufo, ta zaro hotuna cikiin ambulan din wasikar jikinta na rawa da karkarwa ta bude suka fara gani.
Kyakkyawa Fa’iz Giwa ne sanye cikin jibgegiyar rigar leda mai kare sanyi wadda ta sauko har gkwiwarsa, yana tsaye cikin dusar kankara baka ganin komai jikinsa sai fuskarsa, domin hatta hannayensa cikin bakaken safar hannu suke.
Hoto na biyu sanye yake cikin uniform na masu koyon tukin jirgin sama cikin karamin jirgi (jet) da wasu abokan karatunshi farare da bakake. Fuskarshi ta fi fitowa a wannan din sosai. ‘Yammatan uku suka ci gaba da kallon hotunan guda biyu suna kada kai kamar kadangaru, da kyar Naja’atu ta iya bude baki ta ce, “Khadija Yaya Fa’iz din ne?”
Ummi ta rungume hotuna cikin lumshe ido ta ce, “Yes, Fa’iz Bamalli kenan Naja’atu. Yau kinga yayanmu Fa’iz, tabbas Ya Fa’iz ne. Ni kaina ya canza min sosai fiye da yadda na san shi. Ya Fa’iz ya kara kyau kwarai, ya yi kiba da haske, ya kuma kara girma cikin shekaru uku kacal, kai abin da mamaki”.
Haulatu ta ce, “Amman yana da kyau fiye da ku duka, ko in ce fiye da dukkan zuri’ar A.B da na sani. Na so a ce yadda yake da kyau yana da mahadin sa wato kirki, amma kyau ba hali kyawun dan maciji ne Khadija”. (Can da jimawa Ummi ta sha basu labari na da Fa’iz tun daga kuruciya da rashin kirkinsa garemu).
Ummi ta yi murmushi kawai, ta ce, “Haule yadda kika ji labarin Yaya Fa’iz da Fa’izah ne kurum ya sanya kika fassara shi da haka, amma yana da kirki in his own unique way! Da za ki ganshi a zahiri rantsewa za ki yi ba zai ko kusa da taba iya aikata abin da yake aikatawa ba. Ni kadai na fahimci Fa’iz ciki da waje, zan iya rantsewa babu wanda ya kai ni sanin Ya Fa’iz a gidanmu, akwai dalilin da yasa Fa’iz yake kyarar Fa’iza wanda babu wanda ya sani sai shi daya sai Allah da ya halicce mu.
Amma wallahi ba gundarin halinshi kenan ba, koma da halinshi ne ni Ummi Khadija INA SON SHI HAKA! Zan iya jure kowane irin halinshi idan na yi sa’ar samun shi a matsayin miji. Ina son sa da yawa Haulatu, kamar yadda na fahimci shima yana sona kawai ba zai furta bane ko ya nuna kamar yadda Yaya Aliyu ke nuna ma Fa’izah. Ban san ina son shi ba Haule sai ranar da zai tafi”.
Ta yi shiru tana kallon yatsar kafarta kafin ta yi murmushi a hankali ta ce, “Wannan ya faru ne a dalilin babu auren na-gani-ina so cikin zuri’armu da family dinmu duka, sama da komai Fa’iz daban ne wajen halayya da dabi’a. Wanda zai ce miki ya san dukkan halinshi wallah ya fadi karya, saboda kullum sabon hali yake sakewa tamkar wahainiya mai canza launi daga wannan zuwa wannan. Irin wadannan mutanen ma’abota kaskantar da kansu ga abin da zuciyarsu ke matukar so tsiraru ne a cikin al’umma!”
Ta girgiza kai. Su kuma kamar masu daukar darasin tarihi, sai gyada kai suke, don haushi kamar na hada kawunan nasu su duka ukun na gwara, da suka tsaya suna sauraren shirmen Ummi da ba ta san inda ke mata ciwo ba.
Ta ci gaba da cewa, “Ni dai ku tayani addu’a Allah yasa Hajjah ta hadamu ni da Fa’iz, don in ba Yaya Fa’iz ta bani ba? Bana jin zan iya aure a rayuwata. Na gwammace in mutu haka nan ban yi aure ba. Zan jirayi Fa’iz ko da shekaru nawa zai yi bai dawo daga Ukrain ba in dai har Hajjah ba ta yi tunanin aurar dani ga wanin shi ba”.
A hankali na juyo da kaina sashen da su Ummi ke zaune, na dube ta tsaf. Shin mafarki nake ko ko a farke (idona biyu)? UMMI NA SON FA’IZ, FA’EEZ NA SON UMMI?