← Book details Yar Tallah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 90

Sashe 27

Yar Tallah Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read

*CHAPTER 15*

gobe qarfe biyar na yamma, ina da taro a Hotel sai na
dawo." Ta juya ta fice abin ta babu maganar mayafi
Matar ta mikawa Saude wata leda tana fadar, “Wadannan
su ne kayan da za ki saka.�
Saude tasa hannu ta karbi kayan jikinta a sanyaye.
Matar ta yi wani takaitaccen murmushi tana fadar, “Ya na
ga farawa da iyawa har kin yi la’asar, haba Saudat kar ki
karaya mana ki batawa Hajiya rai kin dauke ni matsayin
Auntynki ki yarda da abin da zan fada miki, ki sawa zuciyar
ki za ki iya abin da aka saki da kuruciyar ki ai babu abin da
zai gagare ki-Maigidan ‘mutum ne mai saukin kai yanayin
rayuwarsa irin ta Turawa ce idan dai ki ka nutsu komai zai
zo miki da sauki, kin ji?�
Saude ta daga mata kai alamar eh sannan ta karbi kayan ta
koma Bangarenta ta fada kan gadonta da. kayan zuciyarta
na barazanar
fashewa.
Tsawon Iokaci ta dauka tana saka da warwara, , sannan ta
yunkura ta tashi zaune ta zazzage kayan daga ‘cikin ledar
tana daddagawa. Suite ce baKaKe riga da siket sai ta cikin
fara, ta tsaya tana kallon
kayan sun burge ta sosai, ta linke su ta maida a leda.
Ta yunkura ta sauka daga kan gadon ta janyo abincin da
Aunty ta kawo mata ta bude
Tuwon shinkafa ne da miyar agushi, Saude ta zauna ta ci
abincinta sosai ta gama ta mike tayo alwala ta dawo ta yi
sallah sannan ta koma ta
kwanta.
Sai dai fargabar da ke zuciyarta babu abin da ya canza
yinin yau haka ta yi shi, ba kuzari a jikinta tana tsoron abin
da zai iya faruwa idan ta kasa yin abinda Asma ta sanya ta
ba ta san irin hukuncin da za ta yanke mata ba qila ma ta
iya kashe ta kawai.
'Zuciyarta ta kara tsinkewa wasu irin hawaye masu zafi
suka taru a idanuwanta, watakila ajali ne ya kawo ta gidan,
tasa hannu ta goge ‘yar kwallyar da ta tarar mata ta juya
daga gefen da take ta lumshe idanuwanta, amma ba barci
take ba.
Washe gari Saude na zaune a qasa gefen gadonta, tana
tunanin da ya zame mata jiki, zuciyarta ta lula duniyar
tunanin Hamid da irin kulawar da ya. ba ta a rayuwa. K0 a
yanzu ba ta fidda rantaba tana ji a jikinta za ta koma gida ta
same shi, tana ji a jikinta shi ne mijin da zai aureta su yi
rayuwarsu cikin kulawa da Kauna.
Aunty ta turo kofa ta shigo tare da sallama, Saude ta bude
idanuwanta tana amsawa. Aunty ta tsaya daga bakin kofa
tana fadar, “Ya na gan ki anan zaune, k0 kin manta ne yau
ne ranar da aikin ki zai soma?�
Saude ta kalli tace Na sani Aunnty ba ta ce sai Karfe
biyar ba?�
Annty ta yi wani takaitaccen murmushi kafin ta ce “YallaBai
ya yi tafiya zuwa qasar China sati ukun da suka wuce, don
haka yanzn za ki tashi ki fara gyara masa Bangaren shi ki
zauna har ya iso.� Ta wurgowa Saude makullai tana fadar,
“Ungo
wannan sune makullan bangaren sa.�
Saude ta cafe lokacin da bugun zuciyarta ya tsananta,
Annnty ta juya tana fadar, “Ki tashi ki shirya ina falo ina
jiran ki na raka ki Bangaren nasa.�
Saude ta taKarKare ta mike ta nufi bandaki ta dade a tsaye
zuciyarta na faman kaiwada komowa, sannan ta daure ta
watso ruwan ta fito, ta zauna bakin gadonta ta ciro kayan
daga cikin ledarsu ta sanya kamar yanda Aunty ta nuna
mata, ta mike tsaye siket din bai Karasa isowa kasa ba ya
dai wuce gwiwoyinta, sannan ta janyo hijabinta ta sanya
sannan ta kawo takalmin da ke cikin kayan ta saka wanda
yake sawu-ciki, sannan ta fito ta samu Aunty zaune tana
jiranta tana fitowa suka jera suka fita. ~ '
Gaba daya suka fita daga wannan shashin, suka . nufi daya
Bangaren wanda ke hagu. Aunty ta karBi makullin ta bude
sashin suka shiga, komai na sashin irin na wancan ne, babu
abin da ya bambanta. Aunty ta mika mata makullin tana
fadar.
“Ga shi ki goge komai ki gyara,idan kin gama. Ki zauna har
ya iso, da ya iso ki karbi jakarsa ki kawo masa abu mai
sanyi kin ji?� Saude ta daga mata kai ' alamar eh.
Sannan ta juya ta tafi ta bar ta tsaye tana faman bin
katafaran falon da kallo. To ta ina ma za ta fara? Ita dai a
iya ganinta ba ta ga abin da ya yi datti ba, ta taBe baki
sannan ta fara takawa saman matattakalar � � benen ta
shiga cikin falon, kai tsaye wani qaton falo ne ta fara shiga
wanda, har yafi na farkon haduwa da tsaruwa.
Idanun Saude suka sauka saman wani makeken hoto
wanda yake jingine a kasan gefen bango, ta danci gaba da
bin hoton da kallo. Wani kyakkyawan namiji ne ajin qarshe
wanda shekarunsa ba zasu� wuce talatin da biyar ba, kallo
daya za kai masa ka tabbatar ya hadu tamkar wani
Balarabe, yana rungume da Asma sunyi murmushi'su duka,
sun yi * masifar kyau, dama duk kyan Asma bata kai
mutumin ba, duk da yana namiji, don shi kalar kyansa yafi
kama da na Larabawa saika rantse Balaraben Saudiyya ne
Saude ta wuce a hankali ta shiga zagaye falukan sashin da
bedroom din dake ciki, ita kanta tana ,tausayin kanta
saboda sashi~sashin dake ciki sun kai
goma, haka ta dauko mofa da tsintsiya da tawul da .bokiti
ta fito ta shiga gyaran sashin,�
Sai da ta gyara ko’ina da ina ta goge tare da kunna bona
bonar da ke falukan kowacce ta zuba turaren 'wuta a ciki,
sannan ta dauki room fresner ta dinga feffesawa a ko’ina
da ina, ta Kara gudun A.C sannan ta rurrufe ko’ina kamar
yanda Aunty ta fada mata, ta dawo falon qasa ta zauna
gefen kujera tana faman zare na mujiya, sanyin A.C na
ratsa ta. A take tamkar ta kwanta saboda tsabar gajiyar da
ta yi.
Misalin Karfe biyar da ‘yan mintina Saude ta ji an turo Kofar
falon ta zabura ta tashi tsaye kirjinta na wani masifar
bugawa da qarfl da qarfi. Shi daya ne ya shigo yana sanye
cikin shigar Kananan kaya, sai wani yaro da ke bayansa
wanda ke sanya da suit, yana rataye da irin jakar
ma’aikata.
Ahmad ya tsaya yana watsa mata wani irin kallo
wanda ya Kara hautsina mata� yan hanji, muryarta da rawa
ta fara fadar, ‘Sannu da zuwa
� Shut up! You are very stupid, get the hell out of here
Jikin Saude ya hau Bari ko’ina na jikinta rawa yake ga shi
dai ba ta san tsiyar da ya fada ba, amma yanda ya kwatsa
mata tsawa, ya tabbatar mata da korarta yake don haka jiki
na Bari ta gifta zata wuce, Ahmad ya kara daka mata
tsawa.
“Wait, na ce ki tsaya.�
Saude ta ja ta tsaya, sai faman kyarma, take, don yanda ta
ga tsantsar Bacin ransa ta tabbatar zai iya
kai mata duka cikin bacin rai yace hope baki dai hau min
sama ba?"
Saude ta yi shiru tana faman rawar murya, yaja wani dogon
tsaki ya wuce ciki, jikin ta yana rawa ta wucc, sai faman
harde qafafuwa taka , har tabar falon.
A tsaye ta samu Asma sanye da wata doguwar riga milk
colour, ta dora dan qaramin mayafi saman kanta wanda ya
tsaya iya wuyanta, gilas dinta yau a hannu yake tare da
makullin mota da alama fita za ta yi. �
Saude na shigowa ta tsaya tana kallonta, cikin tsantsar
takaici take kallonta, jikinta ya qara yin la’asar tana shirin
dukawa ta gaishe ta ta ji saukar wani mahaukacin mari' har
sau biyu, dama da hagu,
* wanda yasa sai da ta kifa cikin takaici Asma ke fadar.
“Ashe ke dakikiya ce ban sani ba sakarya, jaka ce keba?
Dube ki, dubi abinda da ke jikin ki, yanzu da wannan bakin
abun ki ka shigar masa ne? Oh! Kin gama dani, amma kin ci
sa’arsa da ya kyale ki da kin gane baki da wayo, don na
tabbatar yau k0
' ruwa ba zai iya hadiya ba.� Ta ja tsaki mts! Ta juya ta dubi
Aunty wadda ke« tsaye tace, “Rabi maza Id debo mata
kayan shafawa da turarurruka, ta cire wannan bakin abin ta
shirya, ki tabbatar ta koma ta ba shi hakuri, Wallahi
idan ki ka sake yaqi amincewa da ke zama ‘yar aikinsa na
rantse miki sai kin fuskanci fushina kin ji na rantse.�
Ta'Karasa maganar da karfi, sannan ta juya ta yi gaba abin
ta.
Wasu irin hawaye masu zafl suka biyo kuncin Saude, wayyo
Allah wannan wace irin rayuwa ce ta samu kanta a ciki?
Au'nty ta dafa ta muryarta a . sanyaye. .
“tace kizo mu je, kada dan wannan abun
ya razanar daké, na san za ki iya yin abin da ma yafi wanda
aka saka ki, idan dai har kin sawa ranki zakiyi, za ki yi
Saudat, please zo muje.� Saude dai ba ta tanka mata ba ta
juya ta bi ' bayanta suka nufi wani sashi daban, ta tura wata
'» kofa sai ga su sun fada wani dan falo irin na ' Sauden. �
Aunty ta bud‘e wata loka da ke jikin bango sai ga kayan
kwalliya kamar su ci kansu, ta dauko leda ta dibar mata
masu yawa, tun daga man shafawa, sabulan wanka, kayan
kwalliya har da turarurmka, sannan ta bude wardrobe ta
ciro dan qaramin hijabin nan mai tsayawa iya wuya wato
himar kalar ja ta
mika mata tana fadar
“Ki yi sauri ki je ki gyara ki tafi, dan na san yanzu haka
akwai abubuwa da dama da yake buqata.� Saude ta karBa
ta fice jikinta amace.
Sai data sake wani wankan sannan ta fito ta shafa mai a
jikinta ta kawo wata ‘yar qaramar powder fara ta shafawa
fuskana, ta sa man lice a bakinta, sannan ta mike ta mayar
da kayan jikinta, ta dauki qaramin hijabin ta rufe kanta.
Wani irin abu ya cunkushe mata zuciya, tunda take a duniya
bata taba irin wannan shigar ba ace kana dan Musulmi
amma ka flta a haka, kai duniya! Takaicin kanta ya kamata,
k0 tsayawa ta dubi kanta ba ta iya ba ta dauki turare ta fesa
guri uku kawai sannan ta fice zuciyarta na faman kai kawo.
Tsoronta ya qara tsananta lokacin da ta iso bakin sashin
nasa ta daure ta yi ta maza ta sa kai cikin falon cike da
fargaba. Turus! Ta ja ta tsaya ‘yar sallamar da take shirin yi
ta makale mata a makoshi,
wani irin tsoro da fargaba mai tsanani suka dirar
mata Kwance yake tsakiyar falon saman kafet ya yi
daidai. daga shi sai gajeran wando ba k0 singlet jikinsa, ya
yi matashi da hannayensa fuskarshi na kallon sama,
idanuwan shi a lumshe suke kamar mai barci.
Saude ta runtse: idanuwanta ba ’tana shirin ta juya da sauri
ta-«koma sai kuma ta tuna
Da
maganar Asma da take fadi“Wallahi idan kika sake
Yaqi amincewa dake a matsayin yar aikinsa sai kin fuskanci
fushina. "
[1/24, 9:31 AM] A A Dboy: 📚📚DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100📚📚
[1/24, 10:13 AM] A A Dboy: *YAR TALLA*
Chapter 27 · 0% Book details