← Book details Mar'adams Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 75 OF 111

Sashe 75

Mar'adams Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Sir na dade rabona da aiki da ATA company ko zan iya samun takardun tsaretsaren ayyukanku na yanzu?"me zai hana zaki samu mana ya fad'a adaidai lokacin da maryaamah ta turo kofar ,ahankali ta shigo ta maida kofar ta rufe ta had'e hannuwanta duka a qirjinta ta rungume fuskarta babu alamun wasa ko tsoro atattare daita ,jin motsin shigowa yasa nadiya ta d'an juya bayanta sai ganin maryamah tayi tsaye tana kallonta, kallo mai tattare da tunhu ma, da sauri nadiya ta mike tsaye jikinta na karkar wa tana kallon maryamah, ido cikin ido suke kallon juna dan sam bata yi expecting zata ganta ba duba da ba'a wannan company take aiki ba , maryama ta soma taku ahankali har ta qaraso kusa daita ta tsaya still kwayar idanun nadiya na cikin nata babu abinda maryamah ke gani alokacin sai tunanin ganinta na farko da taí lokacin da tazo gidansu amatsayin abokiyar aikin sadam yadda komai ke zuwa maryamah haka yake zuwa ma nadiya tunanin maganarta da sadam ne ya shiga dawo mata daki daki alokacin da take bashi labari samun aikinta a ATA company ."

"My heart na samu aiki a ATA company gsky naji dadin samun wannan aikin "ba dadi ya kamata kiji ba ,abun ki tsaya kiyi tunani ne ," me yasa suka kiraki adaidai wannan lokacin cewarsa "idan zaka tuna ai na ta'ba aiki dasu lokacin baya kafin naje kasar Índia kuma naji dadin aiki dasu haka zalika suma sun ji dadin aiki dani ,daman kuma ni bani da wani babban burin da wuce nayi aiki da ATA company yanzu ga dama ta samu sai yanzu nasan na samu aiki mai kyau "babu wani aiki mai kyau da kika samu dan baza kiyi aiki da wannan campany ba". ya fad'a tare da mikewa tsaye ya juya mata baya ,ta kallesa a matukar firgice tana cewa "me kake nufi da bazan yi aiki da wannan kamfanin ba ?ta tambayesa tana dawowa gabansa ta tsaya tana kallonsa ranta a bace "saboda maryama na aiki a d'aya daga cikin kamfanin su " to sai me idan maryaamah na aiki a AGC ? maryama na aiki a AGC ni kuma zanyi aiki a ATA ta ina zan hadu daita ."?

" kaga my heart banason wani rigima yanzu ."
kai yanzu ba kamata yayi kayi murna ba zan samu aiki da zamu ji dadin rayuwarmu kafin ka samu naka aikin ba ?"ya matsota sosai tamkar zai shige jikinta dan har masoyan suna iya shakar numfashin juna sannan ya kai hannuwansa duka ya riko kafad'unta tare da kwantar da murya "ina son ki samu aiki mana amman me yasa bazaki fahimceni ba idan ya kasance plan aka had'a miki fa taya zaki kubutar da kanki ?lokacin data kawo nan qirjinta ya dinga bugawa fiyye da kaida ."kafafuwanta suka kama rawa "tabbas zargin sadam ya tabbata plan akan shirya mata gashi kuma tana tsakiyarsa tsundum .
ta sake tuna maganar sadam ta karshe " ban amince kije ba amman idan kince lallai sai kinje duk abinda ya biyo baya babu ruwana kuma bazan saka kaina cikin rigimar ba sannan zaki nemini ki rasa rashi na har abada ".duk wannan sharad'in daya gindaya mata da zata fito sai da yayi qoqarin hanata hasalima shine dalilin da yasa bata zo akan lokaci ba dan rigima sukai sosai da kyar ta samu ta fito ."

"I hope that you recognize my face ?" maryamah ta tambayeta tana tsareta da kwayar idanunta masu matukar haske ." muryar nadiya na rawa da zuciyar ta tace "uhmm .." eh na gane ki sosai amman ban yi tunanin zanganki anan ba ." eh dole kiyi mamaki ganina tunda Kinsan abinda kikayi ,amman ni duk wannan bai dameni ba ,akwai tamabayoyin da nake son zan miki a halin yanzu,tambaya ta farko "me yasa kikazo gidanmu amatsayin abokiyar aikin sadam ? nan take gaban nadiya yayi wani irin mummunar fad'uwar kafin daga bisani ya shiga dukan tara tara, zuciyarta banda tsinkewa babu abinda take wani irin tsoro da matsanancin firgice suka mamayeta alakaci d'aya ta nemi dukkanin wata natsuwarta ta rasa kallo d'aya zaka mata kasan bata cikin kwanciyar hankali da natsuwarta ."

"sai tambaya ta gaba me yasa kika bawa wani number wayata ya kirani a tsakar dare nazo aiki da wuri ?"nan ma gabanta ya ba da dammm hantar cikinta ta kad'a "bayan kin rasa wayarki na samu wayarki a hannun wani bayan haka kika kirani domin kiji wayar tana hannun waye da kika ji muryata kikayi discounting din kira me kike nema atare dani ?duk me yasa kika min wad'an abubuwan da kika min ?nadiya tayi shiru ta kasa kwakwaran motsi yayinda jikinta ya cigaba da rawa "ta rasa wace amsa zata bata domin gamsar daita yadda nadiya ke kallon maryama cikin rashin sanin me za tace mata haka mr ata yake binsu da kallo yana mamakin qarfin halin maryama ,yar yarinya daita amman akwai kwarewa da qarfin hali da rashin jin tsoron fuskantar duk wanda zatai magana dashi sai a yanzu ya sake gasgata qarfin halinta ba iya akanshi kad'ai take yi ba ,kuma yayi imani bashi ba duk wanda yayi mata ba daidai ba sai ta saisaitashi tare da yi masa karan tsaye arayuwarsa kamar yadda take qoqarin yiwa nadiya a yanzu "

gabad'aya nadiya ta rasa abun yi domin tana cikin wani irin gigita da tashin hankali wanda bata ta'ba shiga irinsa ba ,ahankali mr ata ya maida kwayar idanunshi sosai ya zubawa maryama kamar yadda nadiya tayi kafin ya juye fuskarsa ya sake had'eta tamau kamar yadda ya saba zuwa yanayi na kamewa da rashin d'aukar raini sannan ya kalli inda nadiya take tsaye cikin tsananin gigita ya bud'e baki ya fara magana "ke... ya kikayi shiru ki bud'e baki ki bata amsar tambayoyinta, dan matsawar baki ba bata amsar tambayoyinta ba lallai bazaki bar office din nan ba idan kuma ya zama lallai sai kin barsa to ki tabbatar a hannun hukuma zaki kasance ."ya qarasa maganar yana kallonta à kaskance "ta waigo da sauri inda yake tana kallonsa a matukar tsorace "yes me yasa kike bibiyar rayuwarta tare da caza mata kwakwaluwa?.bana bibiyar rayuwarta amman a wasu lukuta yana da kyau mu bar wasu abu saboda sirrin dake ciki dan ..."sai kuma tayi shiru ta kasa qarasa maganarta "ko babu komai bazata fad'a masu abinda zai yi sanadiyyar rasa sadam arayuwarta ba domin shi din muradin ranta ne da soyayyarsa aka halicci zuciyarta kuma tayi imani sadam na matsanancin sonta ."

"me kike kokarin kice nadiya ?kinga karya bata da wani mahimanci arayuwar d'an adam bana bukatar kiyi min karya dan girman allah idan Kinsan wani abu akan yaya sadam ki fad'a min bare ma ni jikina yana bani kina tare dashi "what !"yes abinda kika ji shine abinda na fad'a "sadam fa kika ce ?"!nadiya ta furta sunansa tana duban maryama ?shifa fa ?"inji cewar maryamah "idan har sadam yana tare dani ai da tun tuni na kawo muku shi koda kuwa acikin halin hauka yake ko wani abu makanmanci haka idan kuma akan muryar da kika ji ne a waya kisani wannan muryar ba muryar sadam bane muryar sabon saurayina ne da zan aura ne ta fad'a tana saisaita natsuwarta tare da hura mata hanci amman dai zan fad'a miki wani abu domin nasan sadam bazai ta'ba fad'a miki tsakaninmu dashi ba ."nida sadam mun kasance masoyan juna ne mun had'u dashi a shekarun baya a makaranta ."

"abubuwa dayawa sun shiga tsakanina dashi tare da alqawarin aure byn nayi tafiya zuwa kasar india na samu labarin aurensa da mutuwarsa nayi matukar gigita da jin aurensa kuma naso da zarar na dawo kasar na maka shi a kotu .nan take maryam ta shiga wani sabon tashin hankali mai tsanani ta koma ta jingina jikinta da glas wanda shine madadin bango acikin office din tana cigaba da kallon nadiya cike da tsananin tashin hankali "."Ina ta qoqarin shirya yadda zan maka shi a kotu domin kwatarwa kaina hakina kwatsam sai kuma naji labarin mutuwarsa tsayawa fad'a miki irin tashin hankalin dana shiga maryama bata lokacin ne saboda ina mutuwar son sadam son da bazan iya bar ma wata halitta ba"

"actually akwai wasu hotunan da mukayi dashi kafin na bar kasar nan ,idanun maryamah ya cika da ruwan hawaye shi kuwa mr ATA jira yake nadiya ta gama maganarta ."nayi imani wadan nan hotunan suna cikin dakinsa kuma duk da baya raye zaa iya ganosu cikin sauki shine ma dalilin da yasa na dawo saboda banason kuga munin hotunan da mukayi dashi dan ya sha bani labarin yadda kuka yarda dashi kuka aminta dashi muddin kuka ga hotunan mu tare cikin wani yanayi kwarin gwiwarku akanshi zatai sanyi."hawaye masu zafi suka zubo akan kuncin maryama lokaci data ta tuna ranar data kamasa yana amsa wayar mace "banyi niyyar fad'a miki ba saboda nasan zakiji ciwo sosai acikin ranki amman wallahi wannan shine dalilin zuwana gidanku har na bukaci nabiki dakinsa sai dai a ranar ban samu naga hotunanmu ba shiyasa nayi tunanin sake dawo da daddare . lura da nayi idanunki biyu kina aiki yasa na kiraki tare da canza murya ni kaina lokacin zuciyata a tsorace take saboda banason kiga private pictures dinmu shiyasa nayi duk abinda nayi na kwashesu dan allah kiyi kokarin ki fahimceni amman fa kisani mijinki sadam ya yaudareni matukar yaudara ."

"maryamah sadam yaci amanata na yarda dashi na mika masa ragamar rayuwata amman ya watsar da yardar da nayi masa saboda bai fad'a min cewar zai yi aure ya barni ba ."na tafi kasar india da zumar idan na dawo zamuyi aure dashi amman sai labarin aurensa kawai naji yayi aure intakaice miki ana gobe zaa daura aurenku munyi waya dashi daace zaa ga wayarsa to da kin tabbatar da duk abinda na fad'a miki wata killa da zuciyarki ta buga sakamakon abinda zaki gani domin abubuwan dake tsakanina dashi ko Ke da kike matsayin matarsa bana tunanin kunyi irinsa dashi ."Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun maryama ta dinga furtawa acikin ranta hawaye na zuba akan kuncinta masu radadi da ciwo."
Chapter 75 · 0% Book details