← Book details Mar'adams Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 111

Sashe 32

Mar'adams Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

yana gama jin bayaninta ya katse kiran ya bude mota batare daya bari direbansa ya fito ya bude masa ba ya fito a hankali yana qarewa unguwar kallo tare da zuba hannuwansa duka cikin aljihunsa ."a natse ya dinga takawa yana kallon unguwar Allah yasa ba suyi nisa ba har lokacin suna farkon unguwar baya ya juya ya soma tafiya ganin haka direbansa ya juya Kan mota. wayarsa ya ciro ya soma neman layinta amman har lokacin bata shiga ya sake yin trying yaji still wayar a kashe take cak ya tsaya zuciyarsa na bugawa da karfi adaidai lokacin da idanushi ya sauka akan get din gidansu a natse ya cigaba da takawa acikin qazamin layinsu da dotti yayi masa over over gabansa na faduwa yana tunani mai zurfi tare da sake shiga tashin hankali dan tunda yake baa ta'ba kin d'aukar wayarsa ba ,ko kashe waya saboda dashi ba sai yau ko maza albarka bare ita mace hakazalika bai ta'ba  tako qafafuwansa cikin irin wannan uguwa mai cike da dotti ba. da wannna damuwar ya qaraso daf da rubabben get din gidansu sai dai tsayawa yayi cak ya kasa aiwatar da komai "

Kamar ya nufi gidansu kai tsaye yasa ayi masa sallama da iyayenta ko tana da wani layin dabam sai kuma miskilanci ya motsa dan hk ya  fasa ,ya juya a fusace ya koma cikin mota ya bawa direban umarnin su wuce ta kan titi capitol suka bi basu koma ta hanyar da suka biyo ta oniwaya ba ,sun danyi tafiya kadan daidai gidan nepa Eldorado ya hango wata kamar ita a tsakiyar titi tana qoqarin zata tsallaka, ware idanuwanshi yayi sosai babu tantama itace "stop !stop !! ya fad'a idanunshi na kanta ta yanka tabi wata kwana tana tafiya tamkar bata da laka ajikinta."ahankali direba ya samu guri a gefen titi yayi parking mr ata ya fito a natse tamkar wanda baya tare da wata damuwa ya tsallaka yabi Kwanar data bi ."

zaune ya hangota ta dafe goshinta tana wani irin Kuka mai ban tausayi hannunta rike da waya tana kallon hoton yaya sadam hawaye na sake gangarowa bisa kuncinta" shikenan na rasaka sadam ."?da gaske ka mutu baka raye ?tana kuka tana furta hakan a fili adaidai lokacin da mr ATA ya qaraso a harzuke ya soma magana cikin zafin rai da zuciya "so kina nan Kin barni cikin tsananin tashin hankali da damuwr rashin sanin halin da kike ciki ?"ya fad'a tsawace da mugun sauri ta zabura ta mike tsaye jikinta na rawa ta zuba masa shayayyun idanunta dake fitar da ruwan hawaye "sir kai ...."Kinsan irin asarar da kikasani wai ke dame kike takama."? yayi saurin tsaidaita " Kinsan yadda kasuwancina yake da matukar mahimanci agurina gabaday na daura raina akan designs dinki nasaka raina nayiwa wanda zaizo ya gani alkwari amman sai kika ki zuwa kuma idan na kiraki sai Kiyi rejecting  din kirana me ma kike yi anan ki bani amsa ?"me kike yi anan?" ya qarasa mgnr a tsawace yana kallon cikin kwayar idanunta ."

    Nan take jikinta ya kama rawa tsoron da matsanancin firgici ya mamaye dukkanin ilahirin jikinta muryarta cike da in inna ta soma mgn "sir nayi .."Karki fad'a komai bana son jin komai daga bakinki keep quite ya fad'a yana nunata "just keep quite bana son jin komai saboda nasan duk abinda zaki fad'a nonsense ne wai a haka kike son ki zama profetional a ma'aikatan mu?Kinawa mutane iskanci da kika ga dama saboda kina daukar wai dan kin iya designed yasa kike samun aiki cikin sauki ?shiru tayi ta cigaba da kukanta tunda ya hanata cewa komai da bala'i sa byn shine ya tmbyeta ."mutane dayawa suna aiki akarkashinmu kuma dukkaninsu professional ne ban ma san me yasa na baki aikin ba ,it's my mistake ."yayi mgnr yana furza mata iskar bakinsa a fuskarta "kuskurena dana yarda dake yana gama maganar ya juya mata baya yana sauke wani wahalallen numfashi tare da rike kugunsa da hannu daya ."

"Dan allah sir ko zaka bani dama nayi maka bayanin dalilina kuma ina fatan zaka fahimceni "what !?ya furta a matukar tsawace tare da juyowa ya tsura mata tsumammun idanunshi da suka canza kala "what do you want to explain?ke kullum cikin kawo uzuri kike "babu wani uzuri da zan kawo maka"
itama tayi masa magana a tsawace kallonta ya tsaya yi kamar wanda aka dasa shi a gurin "kana son kasan me yasa ban samu zuwa office na kawo maka aikinka ba ?ta  tmbayesa  hawaye masu zafi na zubo mata muryarta a raunane cike da kuka ta cigaba da magana "jiya ina tsaka da aiki sai bacci ya daukeni acikin baccina nayi mafarkin mijina sadam adaidai farm center ."

"wani mugun kallo ya dauketa dashi tunda ga samanta har kansa ta cikin glass dinsa zuciyarsa na rawa ,nan take ya tsinci kansa cikin wani yanayi mai wuyar misaltuwa wani irin kishi ne ya mamaye zuciyarsa da ilahirin jikinsa qararrawar dake kadawa a qirjinsa ta soma aiki cikin sauri sauri " nayi mafarkin mijina sadam ne kuma daman ni ina ji ajikina yana raye bai mutu ba shine na fito nemansa gashi duk na gama yawo ban samu mutun daya da yace yaga ko mai kama dashi ba ,na ma rasa ya zanyi da rayuwata domin na rasa wanda zai taimaka min ,ina tsananin bukatarsa arayuwata shine mutun nã farko daya tsaya tsayin daga ya jajurce akaina yasoni ya qaunaceni har muka zamo maaurata wanda sanadiyyar aikina muka rasashi zukatanmu na tsananin bukatarsa."tana magana tana kuka tamkar wata zautacciya ni bana son kowa bana son ganin kowa a yanzu sai shi nayi yawo har na gaji ban ..".

"Yanzu dan wannan banzar dalilin ne ya hanaki kammala aikina ?cak ta tsaida maganarta da kukanta ta tsura masa shayayyun idanunta tana kallonsa cike da tsantsar mamaki dan sam batayi tunani zai nuna rashin Imani akanta ba, ya furzar mata numfashi har sai dataji saukarsa a fuskarta "shiyasa nace miki karki fara aiki dani da wannan tunanin naki ,na fad'a miki karki zo min da tarkaen shirme irin haka ko ban fad'a miki ba ?tai shiru tana cigaba da kallonsa "ans..! ya fad'a a matukar fusace kana kallonsa kasan zuciyarsa cike take fal da matsanancin kishi duk wanda zai cigaba da adana abinda ya wuce yana tare da katoton wahala idan bakiyi qoqarin ki cire abinda ya wuce aranki ba zaki qare rayuwarki ne cikin kunci .""amman Ke naga alamun kullum kina son ki mutu da abinda ya wuce arayuwarki ne ."yayi mgnr a tsawace."

" kawai kin batawa mutane lokaci ,sannan kina ta wahalar da kanki kina yawo kawai dan akan mutumin da baya exit a wannan duniyar "wani kallo tayi masa mai dauke da fasara ya kalleta sosai "yes haka nake nufi da yana raye da iwar haka ya dawo gareku amman ina mamaki da wannna dakikiyar kwakwa luwartaki ta kasa fad'a miki gsky ta kasa yarda da ya matu tsura masa ido tayi "yes haka nake nufi ."da yana raye da iwar haka ya dawo gareku kwakwaluwarta ta sake maimaita abinda ya fad'a mata wannna Karan kam wani kallo take masa mai dauke da natsuwa akan maganarsa "kamr fa gsky yake fad'a mata ya kamata ta natsu ta dawo haiyacinta ta cire sadam a duniyarta tunda daman can ba sonshi take ba daga baya ne komai ya sauya agareta take jin wani irin tausayin umma dashi kanshi yaya sadam din har hakan yasa tayi masa kyakkyawan mazauni na musamman a zuciyarta ya zamo zazzafar soyayya ."

"ina mamakin yadda kike yin wasu abubuwan kamar baki zauna a class ba ya kamata ki zama mai dauriya akan komai karki bari rashin wani ya shafi lafiyar ki, kallonsa ta cigaba da yi ."sannan ki sani yau na rasa appotunity dina akanki babu wani mahaluki da yake iya kallon kwayar idanun  Adam Tariq abdullahi ya fad'a masa  magana amman yau kinsa anyi min ,he happened only because of you ."sheshekar kuka take tana kallonsa cike da tashin hankali "idan zaki manta past din Kiyi ki cigaba da rayuwarki  idan bazaki ba wannan matsalarki ce kece zakiyiwa iyayenki da kanki asara dan wanda ya mutu baya dawowa  "yana gama maganarsa ta karshe ya juya ya barta tsaye hankalinta a matukar tashe .ahankali ta soma yin kasa har ta zube kasa bisa gwiwayoyinta tana wani irin kuka tana kallon hoton sadam " mr ata bazaka ta'ba fahimtata ba bawai bazan iya manta sadam bane amman it's not easy to me ko dan darajan mahaifiyarsa dole ne na cigaba da son shi a zuciyata ."

Mmn sudais💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

Page 15

Cikin yanayi na tsananin tashin hankali mr ata ya cigaba da cewa “duk wannan abun ya faru ne saboda ita ba’a ta’ba tozartani ba amman yau an tozartani akanki. “kin kasa fahimtar mahimancin aikina, nayi kuskure nayi kuskure yarda da aikinki nayi kuskuren d’aukarki aiki da yakin neman soyayyarki nayi na aureki na hutawa rayuwata yaja wani dogon tsaki a lokacin daya tuno abinda yasa yayi loosing opportunities dinsa .wai akan wani matacce wanda baya exit za’a ‘bata masa aiki ” Eh mana baya exit da yana exit daya dawo gida garesu .”yana tafiya yana wannan tunani ita kuwa maryama tana can durkushe tamkar matacciya tana kallon tafiyar mr ata ,tamkar mutun mutumi haka ta koma saboda tsananin tashin hankali ta qame waje d’aya ta kasa kwakkwaran motsi . “wani irin ajiyar zuciya take ta saukewa tana jin gabad’aya duniyar tai mata zafi kuma har lokacin ta kasa yarda cewar yaya sadam dinta ya mutu .wani irin tausayi mai tattare da soyayyarsa ce ta dinga shigarta .”
Chapter 32 · 0% Book details