← Book details Mar'adams Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 61 OF 111

Sashe 61

Mar'adams Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

dukowa tayi sosai idanunta na kallon wani guri har gefen mayafinta datayi rolling din kanta dashi ya makale ajikin karfen suit din da yake sanye dashi kasancewar akwai manyan stone ajiki “maryama !”ya kira sunanta a harzuke yana rufe laptop dinsa da qarfi "yes! yes sir !! tayi maza ta dawo haiyacinta da sauri zata mike tsaye ta kasa sakamakon mayafinta daya makale ajikinsa "ta soma kokarin cirewa tana bashi hakuri “kayi hakuri sir bansan yaakayi ba sai dai rawar da jikinta yake yasa ta kasa cirewa dan haka ya soma kokarin ya cire itama tana qoqarin ta cire duk ta rude sai hakuri take bashi "maryam !”ya sake kirata a tsawace “kin dameni da ban hakuri ki bari na cire tunda kin kasa cirewa ya fad’a tare hadawa da tsintsiyar hannunta ya rike yayinda idanunsu ya tsarke cikin juna yana kallonta cike da tsantsar qaunarta ita kuwa a matukar tsorace take kallonsa .”numfashi ya sake sakamakon jin jikinta da yayi ya dauki zafi ya sake tsareta sosai da idanunshi yana son yasan damuwarta dan tunda ta fara aiki dashi bai ta'ba ganin yanayinta haka ba sai yau .”

ta kalli hannunta dake rike cikin nashi tayi sauri ta cire tana shafa tsintsiyar hannuta ta cigaba da tsayuwa tana jiran ya cire mayafinta har ta bude baki zatai magana yayi saurin daga mata dan yatsansa alamun tai masa shiru ,ahankali ya cire da karfi yana furza da iska mai zafi daga bakinsa sannan ya mike ya tsaya yana fuskartata sosai dan har yana iya jiyo saukar numfashinta "what's the matter ?”nothing sir! ta bashi amsa tana sauke numfashi da kyar saboda kusanci da suka samu sai da yayi mata kallon second goma sannan ya cire idanunshi akanta yana kawar da kanshi gefe tare da zagayowa ya tsaya abayanta yana sauke mata numfashin bakinsa "meye damuwarki ?” shiru tayi qirjinta na bugawa da sauri sauri “ko zaki iya fad'a min damuwarki ?”idan zai yiwu ina son nasani ?.ahankali ta juyo suka fuskanci juna ido cikin ido suke kallon kwayar idanun junansu muryarta a sanyaye tace “sir ai baka bada wannan damar ba ,babu wata damar daka bayar ayi maganar wani abu daya danganci matsalar wani bayan ta aiki?” bance ki tsaya fad'a min wani kaidodin aiki ba ki fad'a min abinda me damunki "?shine abinda nake bukata yanzu .”yayi maganar yana sake motsata.”

Mmn sudais💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

             Page 29

Kallonta ya shiga yi tun daga foring head dinta har zuwa d'an  qaramin bakinta kafin ahankali ya kai  yatsan hannunsa kan pink lip's dinta ya  fara shafa wa ahankali ahankali yana kallon cikin kwayar idanunta yana sake maimaita tambayar da yayi mata "maryama fad'a min abinda ke damunki "?cike da jin fad'uwar gaba tace "babu komai sir idan ma akwai karka damu da matsalata na gode sosai da kulawar ka," ta fad'a tana kawar da fuskarta gefe  zuciyarta na bugawa da sauri sauri ,kamo fuskarta yayi ya had'e da tashi yana wurga mata harara mai tattare da zallar qaunarta had'e jan dogon hancinta "tell me maryama i want to know your problem's ".ya fad'a a can qasan makoshisa "babu komai sir duk yadda yaso yasan damuwarta amman taki.  shiru mr ata yayi yana kallon kyakkyawar fuskarta zuciyarsa cike da tsananin tausayinta ya sani da wata acikin ma'aikatansa  yayiwa wannan tamabayr cike da kulawa lallai zata fad'a masa  fiyye da damuwarta amman gata ita ta kasa fad'a masa "ko wani irin zurfin ciki gareta haka ?yayi tambayar acikin ransa. "yasan akwai tarin damuwa atattare daita amman ta kasa fad'a masa abinda ke damunta “ina ma zata fad'a masa damuwarta da babu abinda zai hana bai magance mata ba, dan zuciyarsa bata son ganinta cikin damuwa."

Ahankali maryama ta zame jikinta daga nashi tana cewa "na gode sosai sir " babu bukatar ki gode min fatan kin ga desings din dana nuna miki yanzu kuma zamuje mu hadu da wani  abokin business dinmu zuwa anjima “ shiru tayi na second goma kafin ahankali muryarta ta fito. "sir me yasa sai tare dani zaka  bayan akwai tarin ma'aiktan dake bukatar haka ."eh na sani amman dake nayi ra'ayin zuwa any problem?no sir!"ta fad’a cike da jin haushinsa dan tasan yau ma so yake ya ‘bata mata lokaci ya d’an kalleta da gefen idanunsa yaga yadda ta mugun had’e rai nan take yaji zuciyarsa ta damu amman dai yace “ kije ki fara shiri at anytime zan nemeki “.
jikin maryama a matukar sanyaye ta juya ta fita ranta bai so fitar da zai yi daita ba ,yabi bayanta da kallo yana tunanin abinda ke damunta”. bayan maryama ta koma office ta bud’e durowar data ajiye wayar anifa ,ta dauko wayar ta zauna rike da wayar tana duba screen din wayar inda taga miss call da yawa amamn babu damar taga sunan masu missed call sakamakon wayar nada security code bata jima da zama ba kira ya shigo wayar da wata number dabam qirjinta na bugawa ta d’aga batare da tayi magana ba .”har kusan second goma wayar na manne a kunnenta jin bazaayi magana ba yasa daga can bangaren akace “hello !” a natse ta motsa lip’s dinta tace “ina ji dawa nake magana ?” still shiru akayi can sai aka katse kiran .”

acan bangare kuwa yaya sadam ne ya waiga ya kalli inda nadiya take tsaye ransa duk a ‘bace “na fad’a miki wannan murayar muryar maryama ce yaakayi ma wayarki taje hannunta .” I don’t know my heart !”ni dai nasan na rasa takardar dana saka documents dinka da wayata ,tsaki yaja yana dafe goshinsa da hannuwansa duka “nadiya ta kai hannunta ta dafa kafad’ansa tana cewa “me yasa zaka damu bayan mun san inda zamu ganta “kina nufin muje gareta kenan?”ya fad’a yana d’ago kanshi ya zuba mata idanunshi “ idan bamuje ba har ta bude taga documents dinka kaga ai ka shiga matsala inda wayata ce kad’ai wannna mai sauki ne “ko wayarki kad’ai ba abu ne mai sauki ba “ya fad’a yana sake shiga tashin hankali “wallahi nadiya kin cika care less dayawa just rike takarda ya zame miki aiki “
“Wani irin careless gareni ?nifa banga dalilin da zai sa ka damu kanka dayawa ba .maryama tana da ilimi da fahimta my heart ka fito ka mata magana a zahirinka,ya kamata tasan komai ka saketa ka nemi ta rufa maka asiri muyi rayuwarmu that’s all idan son samu ne ni ba haka bane araina ya cigaba da kallonta atsanake tana magana da d’agawa “yes ni ba haka bane araina banason boye boye arayuwata nafi son komai forwardstret ka saki maryama kawai sannna ka koma gida idan kace baka son maryama akwai wanda zai maka dole ne ?” numfashin ya sauke kawai yana dubanta “ my heart ya kamata ka furta mata saki .”

“Kinga mu bar maganr nan haka nadiya nemo mana mafuta lallai ya kamata documents dina da wayarki su dawo garemu “nadiya tayi shiru kawai tana dubansa dan ita a halin yanzu rashin sakin maryama ya zame mata qalubali ga rayuwarta zata só kafin suyi aure ya zamanto babu wata halaka atsakaninsu amman ta rasa dalili da yasa yaki sakinta bayan kullum lallabashi take akan ya saketa “.ya mike zai wuceta tayi saurin riko tafin hannunsa cikin nata cak yaja ya tsaya kafin ahankali ya juyo gbdy ya fuskanceta , cike da matsanancin sonshi ta qara taku biyu ta zube jikinsa muryarta cike da rauni tace “my heart ko ka fara son maryama “?numfashinsa ya hau sauke mata a fuska da wuyanta “ka fad’a min idan ka fara sonta ne ni na hakura na bar mata kai ?” tayi mgn a shagwabe kamar zatai kuka hannuwansa duka ya kai ya zagaye kugunta dashi ,inda nadiya ta sake shige masa sosai tana tado masa da sha’awarsa “kema kinsan ke kad’ai zuciyata take so “amman me yasa ka kasa sakin maryama ni so nake naji ka raba kanka da ….bata qarasa mgnr ba taji saukar lips dinsa akan nata alamun tayi shiru “sau nawa zan fad’a miki bata cikin rayuwata ?ba dai saki kike da bukata nayi mata ba ?”ta gyda masa kai tana mai lumshe masa ido “ki kwantar da hankalinki zanyi “.
ai nadiya bata tsaya wata wata ba ta soma sucking din lip’s dinsa ,sun dade suna shan bakin juna kafin ahankali suka tsurawa juna ido “ina sonka my heart. “baki kai ni ba .ni dai nasan nafika sonka.”

kanshi ya girgiza mata yana cewa “kowa nashi ya sani amman ina mutuwar sonki nadiya ke kinsan irin abubuwan da nayi facing kafin mu kasance tare gashi sakacinki yana neman sakamu cikin matsala “in sha allahu my heart bazamu shiga matsala ba .”
sun dade makale da juna suna tsara yadda zasu bi maryama su amshi abubuwansu a hannunta ,”shiru maryama tayi tsaye tana duba screen din wayar kafin ahankali ta sake maidashi cikin durowa ta ajiye “ko me yasa suke son damun rayuwarta haka ?”ta cigaba da zama shiru tana nazarin muryar da taji yanzu wanda shine karo na uku da taji ,yadda zuciyarta ta kasa yarda cewar yaya sadam dinta bai mutu ba yana raye haka ta kasa yarda cewar wannan muryar ba muryarsa bace zuciyarta ma tafi tsaiduwa akan muryarsa ce .ranar dai kowa ya kalli yanayin maryama yasan babu lafiya kuma sai ya tambayeta amsa d’aya take bayarwa shine babu komai yayinda acan bangaren yaya sadam da nadiya abu na farko da suka fara shine trancking din number wayar nadiya domin su san takaimaiman inda maryama take cikin sauki kuwa suka gane inda take sakama kon wayar na kunne har lokacin.”
Chapter 61 · 0% Book details