Sashe 56
Mar'adams Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cike da sanyin jiki mami tabi bayan mr ata da kallo kafin ahankali ta d'auke idanunta ta maida kan baba qarami dake tsaye zuciyarsa cunkushe da haushi da bakinciki abinda mr ata yayi masa "kinga kalar tarbiyar ki ko ?a gabanki d'anki yayi min zagi bayan ya wulakanta maganata "tukuna ma ina alqawarin da kika min na cewa bazai yi aikin nan ba "?numfashi mami ta sauke kawai wanda hakan yayi sanadiyar qara hassala baba qarami dan haka a tsawace yace" kin tsareni da idanuwa kin kasa cewa komai tunda kinsan da had'in bakinki yayi komai ."shikenan tunda ke da d'anki kunyi son ranku amman fa ki sani bashi kuka ci." mami ta sake kallon baba qarami dake surfa maseefa ta hade hannu wanta waje d'aya kasamcewar ta rasa me zata ce masa ya fahimce ta .kusan mintuna goma ta d'auka tana kallonsa batare da tayi yunkurin dakatar dashi ba ko ce masa wani abu ba har sai daya gama amayar da abinda ke ransa sannan ta gyara tsayuwarta muryarta cike da laushi ta soma magana "dan girman allah baba qarami kayi hakuri kai ma kasan halin adamcy da taurin kai "sai da ya ta'be bakinsa sannan yace "ai dole kince min nayi hakuri tunda ke da d'anki kun gama ci min mutunci mami bata damu da maganarsa ba dan tasan kad’an daga halina idan ranshi ya ‘baci kamar adamcy ne .”
sake kwantar da murya mami tayi "ni dai hakuri nake baka kuma in sha allahu..."saurin d’aga mata hannu yayi dan baya da bukatar alqawari ta "dakata ya isheni haka karki cika min kunne naji amman wallahi wallahi kinji na rantse ki ga yawa wannan d'an iskan d'an naki ya kiyayyeni kar ya sake gigin sake aikata mana haka "shikenan hakan ma bazai sake faruwa ba zai kiyayye yayinda aranta tace “bama zai cigaba da kula da kamfanin ba ,ya bar maku har abada domin dai tasan halin d'anta idan yace yes yes ne haka zalika idan yace no tô no ne tunda yayi mata alqawarin bar masu kamfanin tasan bazai ta'ba dawowa ya canza magana ba."da rarrashi da komai uncle jay da yaya Ibrahim da mami suka samu ya hakura ya fice daga parlour'n tare da sultan ."
yayinda mr ata ke zaune akan kujera a bedroom dinsa yana zukar sigari ahankali yana magana a fili "wannan mutumin so yake sai muyiwa juna rashinmutunci tukun zai fita a tsabgata,ko ina ruwansa da yadda zanyi da rayuwata? zanyi aiki a duk lokacin da nake so kuma dole ku barni koda kuwa ranku bai so “saboda son zuciya irin nashi kawai ya zauna yana biyewa ya'yansa inda ni d'ansa ne zai min haka ?"ya tambayi kanshi yana jan dogon tsaki tare da shafa sumar kanshi da hannu d’aya sannan ya mike ya fad’a kan bed dinsa yana cigaba da zugar sigari ."
Direban daya d'aukosu maryama, yusura ya fara saukewa sannan maryama, karfe goma daidai na dare maryama ta shiga gidansu part din umma ta shiga inda ta iske Aunty hassna zaune a parlour'n tana kallon tv "sannu da gida aunty ."ta fad'a muryarta a sanyaye sannan ta ra'ba zata wuce ta gefenta" ina kika tsaya har goma na dare"? maryama tayi matukar mamakin jin tambayarta ita da babu ruwanta da rayuwarta yau kuma me janyo wannan tambayar “ta tambayi zuciyarta tana duba agaogon hannunta goma ma har ta fara wucewa" .
“ki duba tun lokaci da kika bar gidan nan sannan ki kalli lokacin da kika shigo maryama kina yin abinda kike so acikin gidan nan kawai dan an baki dama ko ba haka ba ?"ta fad'a tana dubanta a kaskance bama zaki kira kowa ki fad'a dalilin da ya tsaida Ke ba karki manta wannna gidan namu gidan mutunci ne karkiyi abinda zaki 'bata mana sunan gida kamar yadda uwarki ta 'bata sunan gidansu dan nasan har abada irin guje gujen datai bazai ta'ba gogewa a zukatansu ba .”
Wani abu maryama taji ya caki kahon zuciyarta ranta yayi matukar 'baci zuciyarta ta dinga tuttukin bakinciki ,idan tace bata ji ciwon maganar aunty hasana ba wallahi tayiwa kanta karya ,amman data tuna bazasu wani sake d'aukar lokaci mai tsawo a gidan ba zasu tattara su barsu gidan su canza rayuwa sai kawai ta rarrashi kanta ta danne abinda take ji a yanzu muryarta a sanyaye tace "aunty hasana daman akwai wani aikai dazaa gabatar a office dinmu ne yau tun kwana uku daya gabata ake shirnsa umma ma tasan da zamansa to sai yau aka gabatar dashi shine dalilin da yasa nayi dare a waje amman in sha allahu bazanyi abinda zai ‘bata sunan family dinmu ba ,da safe ma naso na tsaya na fad'a miki koda na shigo d'akinki kina bacci amman Kiyi hakuri dan allah "ta fad'a tana ra'bawa ta bayanta zata shige daki "tsaya ! ta jiyo sautin muryarta."maryama taja ta tsaya tana lumshe idanunta "me kake ce a office ko me ?"
"uhm gskiya yanzu kin kware a iya tsara karya amman kisani na samu number wayar office dinku a hannun kanwar yusura kuma na kira an fad'a min lokacin da kika bar office a ina kike adaidai lokacin?eh amm gabad'ayanmu muna gidan mr ATA ne " me kika ce ?ta fada tana dubanta da mugun kallo "me naji kin fad'a yanzu "?sake maimaita min naji kawai dan iskanci sai ki kama hanya kije har gidansa anya ma kuwa ba iskanci kike yi awaje ba yasa maza ke gudu su barki ba ?"shi kuma wannan da yayi shahada ya aureki kin kashesa "muryar maryama ta na rawa tace "haba aunty hassana me kike kokarin cewa ? Karyar me zanyi idan nayi karya meye ribata ?" me zata bani” yanzu ke aunty hassana har kina tunanin ina yin iskanci a waje ."?dan allah ki cire wannan zargin aranki kawai dai akwai wani aikin sirri da zamuyi shine yace muje gidansa kuma bani kadai bace ki bincika zaki .."
“Kiyi min shiru banason jin wannna karyar naki yanzu dai rashi aure yasa zaki fara d’auko mana magana Allah yasa ba abinda yasa aunty tace nazo na zauna ba kenan idan ba haka me zai same ki dan kin zauna ke kad’ai “.?"akan me zanyi karya to ?" maryama ta fad'a a zafafe cike da jin haushi ta cigaba da mgn "dan allah ki daina min irin wannan kallon."ni bance ni ta gari bace amman ni ba yar iska bace idan na dawo aiki da wuri fine idan ban dawo ba shima daidai ne dan …”dakata ba dani kike wannan maganar ba da waccan uwar taki kike sannan ki bude kunnenki da kyau bazan mu yarda da wannna iskancin ba sannan shi mr ATA din akan wani dalili zai kaiku gidansa idan ba da wata manufa ba?” ko da yake sai dan iska ya bada dama sannan zaa kawo masa batun iskanci "Aunty hassan kin dade kina kirana da wannna kalmar amman idan allah yaso bazai jarabeni daita da zama yar iska ba dan bana aikata abinda ya danganci hakan , sannn karki danganta mr ata da wannna kalmar domin kuwa ke uwa ce ,kawai dai yau aikinmu ne yazo da wannna tsarin dan haka kisani naje gidansa ne kawai dan aiwatar da aikina ba dan wani abu ba .”
"idan ma kuma dan wani abu ne babu ruwan kowa da rayuwata dan babu mai ciyar dani zan iya yin duk yadda naso rayuwata ce ." tana gm fadar haka ta shige daki ta barta zaune tana Maimaita kalmar karshe data fda” idan ma kuma dan wani abu ne babu ruwan kowa da rayuwata zan iya yin duk yadda naso rayuwata ce ."cab din jan lallai yarinyar nan wuyanki ya isa yanka tunda an fara danna miki jijiya kinsan dadinta ai dole ki fad'a min haka amman kisani ba ni kika fad'awa magana ba wacan ganta lalliyar uwar taki da ta gama zubar da mutuncinta kafin aure kika fad'awa mgn ,ta fad'a tare da yin kwafa tana gyara zamanta tare da cigaba da mita “a lallai maryama anji dadin maza ina fad’a kina fad’a .duk maryama na jiyota amman ta daure ta cije dan kar tayi kuka amman sai da wasu hawaye masu zafi suka zubo mata tana sharewa wasu hawayen na zubowa daga idanunta a lokacin da take tuna asalin mahaifiyarta sannan ta tuna irin rayuwar kuncin da sukayi a baya, ynx ma gashi
irinta sukeyi. .”
“Duk runtsi duk wuya baza tayi irin kalar rayuwar mahaifiyarta ba ,bazata ta’ba zabar namiji ta bar ahlinta ba ,haka zalika bazata ta’ba yarda wani namiji yasanta diya mace ba muddin ba aure sukayi ba ,zata rike mutuncinta da darajarta ta diya mace duk mijin data kawo suka nuna basa so wallahi ta barshi kenan har abada bata da abinda zatai dashi koda kuwa da zinari akayisa ,ba dan komai ba sai dan siyawa kanta mutunci da daraja,shekaru sama da ashiri kenan amman har zuwa wannan lokacin rashin mutuncin dangin mahaifinta ba bar mahaifi yarta ta huta ba ,basu barta ba haka zalika suma ya’yanta basu tsallake rashin mutuncinsu ba .”
“amman duk wa janyowa kanshi ?ta tambayi wankakkiyar kwakwaluwarta tana sake share hawayenta ,inda ta samu waje ta zauna tare da rafka tagumi tana tunanin rayuwa “yanzu aunty haka zaki qarar da rayuwarki batare da kin koma ga ahlinki ba ?”why aunty?!me yasa bazaki koma garesu ba ?”
”me yasa kike jin tsoro ?“mikewa tayi tsaye ta had’e hannuwanta waje d’aya“lokaci yayi aunty ,lokaci yayi da zaki koma ga iyayenki dan dole nasan abun yi.”
sake kwantar da murya mami tayi "ni dai hakuri nake baka kuma in sha allahu..."saurin d’aga mata hannu yayi dan baya da bukatar alqawari ta "dakata ya isheni haka karki cika min kunne naji amman wallahi wallahi kinji na rantse ki ga yawa wannan d'an iskan d'an naki ya kiyayyeni kar ya sake gigin sake aikata mana haka "shikenan hakan ma bazai sake faruwa ba zai kiyayye yayinda aranta tace “bama zai cigaba da kula da kamfanin ba ,ya bar maku har abada domin dai tasan halin d'anta idan yace yes yes ne haka zalika idan yace no tô no ne tunda yayi mata alqawarin bar masu kamfanin tasan bazai ta'ba dawowa ya canza magana ba."da rarrashi da komai uncle jay da yaya Ibrahim da mami suka samu ya hakura ya fice daga parlour'n tare da sultan ."
yayinda mr ata ke zaune akan kujera a bedroom dinsa yana zukar sigari ahankali yana magana a fili "wannan mutumin so yake sai muyiwa juna rashinmutunci tukun zai fita a tsabgata,ko ina ruwansa da yadda zanyi da rayuwata? zanyi aiki a duk lokacin da nake so kuma dole ku barni koda kuwa ranku bai so “saboda son zuciya irin nashi kawai ya zauna yana biyewa ya'yansa inda ni d'ansa ne zai min haka ?"ya tambayi kanshi yana jan dogon tsaki tare da shafa sumar kanshi da hannu d’aya sannan ya mike ya fad’a kan bed dinsa yana cigaba da zugar sigari ."
Direban daya d'aukosu maryama, yusura ya fara saukewa sannan maryama, karfe goma daidai na dare maryama ta shiga gidansu part din umma ta shiga inda ta iske Aunty hassna zaune a parlour'n tana kallon tv "sannu da gida aunty ."ta fad'a muryarta a sanyaye sannan ta ra'ba zata wuce ta gefenta" ina kika tsaya har goma na dare"? maryama tayi matukar mamakin jin tambayarta ita da babu ruwanta da rayuwarta yau kuma me janyo wannan tambayar “ta tambayi zuciyarta tana duba agaogon hannunta goma ma har ta fara wucewa" .
“ki duba tun lokaci da kika bar gidan nan sannan ki kalli lokacin da kika shigo maryama kina yin abinda kike so acikin gidan nan kawai dan an baki dama ko ba haka ba ?"ta fad'a tana dubanta a kaskance bama zaki kira kowa ki fad'a dalilin da ya tsaida Ke ba karki manta wannna gidan namu gidan mutunci ne karkiyi abinda zaki 'bata mana sunan gida kamar yadda uwarki ta 'bata sunan gidansu dan nasan har abada irin guje gujen datai bazai ta'ba gogewa a zukatansu ba .”
Wani abu maryama taji ya caki kahon zuciyarta ranta yayi matukar 'baci zuciyarta ta dinga tuttukin bakinciki ,idan tace bata ji ciwon maganar aunty hasana ba wallahi tayiwa kanta karya ,amman data tuna bazasu wani sake d'aukar lokaci mai tsawo a gidan ba zasu tattara su barsu gidan su canza rayuwa sai kawai ta rarrashi kanta ta danne abinda take ji a yanzu muryarta a sanyaye tace "aunty hasana daman akwai wani aikai dazaa gabatar a office dinmu ne yau tun kwana uku daya gabata ake shirnsa umma ma tasan da zamansa to sai yau aka gabatar dashi shine dalilin da yasa nayi dare a waje amman in sha allahu bazanyi abinda zai ‘bata sunan family dinmu ba ,da safe ma naso na tsaya na fad'a miki koda na shigo d'akinki kina bacci amman Kiyi hakuri dan allah "ta fad'a tana ra'bawa ta bayanta zata shige daki "tsaya ! ta jiyo sautin muryarta."maryama taja ta tsaya tana lumshe idanunta "me kake ce a office ko me ?"
"uhm gskiya yanzu kin kware a iya tsara karya amman kisani na samu number wayar office dinku a hannun kanwar yusura kuma na kira an fad'a min lokacin da kika bar office a ina kike adaidai lokacin?eh amm gabad'ayanmu muna gidan mr ATA ne " me kika ce ?ta fada tana dubanta da mugun kallo "me naji kin fad'a yanzu "?sake maimaita min naji kawai dan iskanci sai ki kama hanya kije har gidansa anya ma kuwa ba iskanci kike yi awaje ba yasa maza ke gudu su barki ba ?"shi kuma wannan da yayi shahada ya aureki kin kashesa "muryar maryama ta na rawa tace "haba aunty hassana me kike kokarin cewa ? Karyar me zanyi idan nayi karya meye ribata ?" me zata bani” yanzu ke aunty hassana har kina tunanin ina yin iskanci a waje ."?dan allah ki cire wannan zargin aranki kawai dai akwai wani aikin sirri da zamuyi shine yace muje gidansa kuma bani kadai bace ki bincika zaki .."
“Kiyi min shiru banason jin wannna karyar naki yanzu dai rashi aure yasa zaki fara d’auko mana magana Allah yasa ba abinda yasa aunty tace nazo na zauna ba kenan idan ba haka me zai same ki dan kin zauna ke kad’ai “.?"akan me zanyi karya to ?" maryama ta fad'a a zafafe cike da jin haushi ta cigaba da mgn "dan allah ki daina min irin wannan kallon."ni bance ni ta gari bace amman ni ba yar iska bace idan na dawo aiki da wuri fine idan ban dawo ba shima daidai ne dan …”dakata ba dani kike wannan maganar ba da waccan uwar taki kike sannan ki bude kunnenki da kyau bazan mu yarda da wannna iskancin ba sannan shi mr ATA din akan wani dalili zai kaiku gidansa idan ba da wata manufa ba?” ko da yake sai dan iska ya bada dama sannan zaa kawo masa batun iskanci "Aunty hassan kin dade kina kirana da wannna kalmar amman idan allah yaso bazai jarabeni daita da zama yar iska ba dan bana aikata abinda ya danganci hakan , sannn karki danganta mr ata da wannna kalmar domin kuwa ke uwa ce ,kawai dai yau aikinmu ne yazo da wannna tsarin dan haka kisani naje gidansa ne kawai dan aiwatar da aikina ba dan wani abu ba .”
"idan ma kuma dan wani abu ne babu ruwan kowa da rayuwata dan babu mai ciyar dani zan iya yin duk yadda naso rayuwata ce ." tana gm fadar haka ta shige daki ta barta zaune tana Maimaita kalmar karshe data fda” idan ma kuma dan wani abu ne babu ruwan kowa da rayuwata zan iya yin duk yadda naso rayuwata ce ."cab din jan lallai yarinyar nan wuyanki ya isa yanka tunda an fara danna miki jijiya kinsan dadinta ai dole ki fad'a min haka amman kisani ba ni kika fad'awa magana ba wacan ganta lalliyar uwar taki da ta gama zubar da mutuncinta kafin aure kika fad'awa mgn ,ta fad'a tare da yin kwafa tana gyara zamanta tare da cigaba da mita “a lallai maryama anji dadin maza ina fad’a kina fad’a .duk maryama na jiyota amman ta daure ta cije dan kar tayi kuka amman sai da wasu hawaye masu zafi suka zubo mata tana sharewa wasu hawayen na zubowa daga idanunta a lokacin da take tuna asalin mahaifiyarta sannan ta tuna irin rayuwar kuncin da sukayi a baya, ynx ma gashi
irinta sukeyi. .”
“Duk runtsi duk wuya baza tayi irin kalar rayuwar mahaifiyarta ba ,bazata ta’ba zabar namiji ta bar ahlinta ba ,haka zalika bazata ta’ba yarda wani namiji yasanta diya mace ba muddin ba aure sukayi ba ,zata rike mutuncinta da darajarta ta diya mace duk mijin data kawo suka nuna basa so wallahi ta barshi kenan har abada bata da abinda zatai dashi koda kuwa da zinari akayisa ,ba dan komai ba sai dan siyawa kanta mutunci da daraja,shekaru sama da ashiri kenan amman har zuwa wannan lokacin rashin mutuncin dangin mahaifinta ba bar mahaifi yarta ta huta ba ,basu barta ba haka zalika suma ya’yanta basu tsallake rashin mutuncinsu ba .”
“amman duk wa janyowa kanshi ?ta tambayi wankakkiyar kwakwaluwarta tana sake share hawayenta ,inda ta samu waje ta zauna tare da rafka tagumi tana tunanin rayuwa “yanzu aunty haka zaki qarar da rayuwarki batare da kin koma ga ahlinki ba ?”why aunty?!me yasa bazaki koma garesu ba ?”
”me yasa kike jin tsoro ?“mikewa tayi tsaye ta had’e hannuwanta waje d’aya“lokaci yayi aunty ,lokaci yayi da zaki koma ga iyayenki dan dole nasan abun yi.”