← Book details Mar'adams Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 111

Sashe 17

Mar'adams Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yana tsaye yana tunani mami ta turo kofar bedroom dinsa ta shigo hannunta rike da cup din shayi da d’an qaramin tray yayinda idanunta ke kansa bai san ta shigo ba sakamakon zurfin da yayi cikin tunani “ta qarasa ta ajiye tray din hannunta akan table ta sake dawowa wajensa ta tsaya tana kiran sunansa “adamcy nah ! firgigib ya dawo haiyacinsa yana sauke wani zazzafan numfashi ya tsura mata ido itama idanunta yana kanshi tana nazarinsa “lafiya tunanin me kakeyi haka ?numfashi ya sauke da karfi yana tura hannuwansa duka cikin aljihunsa sannan ya girgiza mata kai yana yamutsa fuska alamun babu komai “okay ga shayi nan na kawo maka ka dauka ka sha “ahankali yaja qafafunsa ya isa inda ta ajiye tray ya d’auki cup din ya rike yana dubanta “sweetheart ina kikaje ne tun safe banji motsinki ba kuma na kira wayoyinki duk suna shiga bakya d’auka ?”yayi maganar kwayar idanunshi na kanta “ naje hospital”da sauri ya motso kuda daita yana kallonta a d’an tsorace “lafiya ina Ke miki ciwo ?mai yasa kike je ke kad’ai baki tasheni ba ?yayi mata tmbyr ajere cike da shiga tashin hankali “lafiya ta lau adamcy naje wajen auta ne ta sauka lafiya ta samu d’a namiji “wani naunayen ajiyar zuciya ya sauke “na tsaya ne sai da’ aka gyara bby da mamansa sannna na dawo .”

Numfashi ya sauke fuskarsa yana bayyanar da wani sihirtaccen farinciki take maryam tazo ransa da sauri ya kawar daita yana cewa “masha allah auta ta zama uwa “sosai kuwa sauran kai ma ka zama uba dan nan kusa maryam zata haihu gefen bakinsa ya kamo yana cizawa ahankali ahankali batare da yace mata komai ba “Allah ya rabata da cikin lafiya !”shiru yayi yaki cewa komai ta riko hannunsa ta zaunar dashi akan gado itama ta zauna a gefensa tana dubansa kamar zatai kuka “adamcy na rokeka ka yafewa maryam wallahi rayuwarta na bani tausayi duban mami yayi yana kankance ido “wato shi ba abun tausayi bane data cucesa sai itace abar tausayi ? yayi maganar acikin ransa “ni mahaifiyarka ce ina neman alfarma ko sau d’aya ne ka yiwa maryam addaur sauka lafiya wallahi tana cikin wani hali likitoci ma sunce da kyar zata iya haihuwa da kanka runtse idanunshi yayi kawai batare da yace komai ba kusan mintuna shabiyar tana jiran yayi magana amman yaki cewa uffan “shikenan tunda baza kace komai ba ni zan koma hospital “.ta mike ta nufi kofar fita “bari nazo muje tare bata juyo ba haka zalika bata kulasa ba sakamakon nauyin da zuciyarta tayi .”

Washegari

Ahankali maryama ta tashi tana mika da salati tare da rufe bakinta sakamakon hammar data kamata kai tsare bayi ta fad’a tayi wanka ta fito tasa kaya zuwa wani had’ad’den doguwar riga blue da ratsin yellow tayi rolling kanta da qaramin mayafi yellow ta shafa powder kawai da white lips duk da ba wani kwaliya tayi ba amman she look attractive tayi kyau sosai ta feshe ilahirin jikinta da turare ta qarasa inda takalmanta suke ta sanya flat haif shoe ta fito inda ta iske umma a falo tana ajiye kular abincin akan qaramin table da alamun duk ita tayi aikin gidan dan ga koina nan fess ta qarasa inda take ta durkusa har kasa cike da girmamawa ta gaisheta”ina kwana ummah ?kin tashi lafiya maryama ?alhamd umma “har kin shirya zuwa aiki ?eh umma na shirya sannu da aikin “yauwa maryama .mai yasa baki tasheni nayi ba ? ta fad’a tana tsura mata ido “numfashi umma ta sauke tana dubanta itama “ lafiya umma ko shigata batayi bane naje na canza ?Aa shigarki tayi kinyi min kyau né sosai fiyye da lokutan baya “murmushi maryama tayi tace “na gode sosai umma zauna kici abinci atare suka zauna umma ta zuba mata abinci ta fara ci a natse tana duba lokacj bayan ta gama ci tayi mata sallama ta fita gurin aunty ta shiga ta gaisheta tace “aunty zan fita aiki aunty tace daita “tô pricess sai kin dawo allah ya tsare.” ta fito tana ma aunty bye bye itama aunty daga mata hannu tayi cike da farinciki.”

Ahankali take d’aga qafafuwanta hannunta rike da file ta nufi office din ATA hankali take tafiya tana tuna maganganunsa na jiya “idan zakizo aiki karki zo min da wannan package din Kiyi shiri kamar kowani ma’aikaci ta furzar da numfashi tana rausayar da kwayar idanunta saboda sanin cewar ba irin shiri su tayi ba ta dai sauya daga nata shirin dan gsky bazata iya shigar suit da wondo ba da wannan tunanin ta qarasa jikin glass door tayi knowking tare da neman izinin shiga daga can bangaren aka bata umarnin shiga .”cike da sanyin jiki ta tura kofar ta shiga yana zaune akan kujera ta tsaya a gabansa tana kallon kasa ya bar abinda yake ya d’ago tsumammun idanunshi ya tsura mata yana kallonta cike da tsantsar qauna ,shigar tayi masa kyau sosai dan daman shi yana mugun son yaga doguwar mace cikin shigar dogayen kaya but yanayin aikinsu kowa shigar suit yake kusan minti shabiyar yana kallonta kafin a hankali ya d’auke kwayar idanushi .”

Muryarta a hankali ta fito “good morning sir ! bai amsa ba ya nuna mata wurin zama “ki zauna jiki a sanyaye taja kujerar dake fuskarsa baya kad’an ta zauna a hankali tamkar kazar da Kwai ya fashewa aciki yayinda zuciyarta ke wani irin rawa shi kuwa gabadaya hankalinsa da natsuwarsa suna kanta amman bazaka ta’ba iya ganewa ba stil kuma idanunshi na Kan file din hannunsa .itama haka nan ta tsinci kanta da kallonsa kyakkyawan gaske ne kuma fari ne tas tmkr balarabe yana da idanu masu dan girma da dogon hanci mr ATA iyakar haduwa ya gama haduwa sosai ajin farko yana da tsayi da fadin qirji yana da saje zuwa rabin fuskarsa sai gashin bakinshi daya zagaye gemunshi gashi dogo mara kiba sai dai ya dan fita tsayi da kad’an ”.
Shiru har tsawon mintuna ashirin bata ce uffan ba “ko zamu iya yin maganar aiki dan a tunani shi ya kawoki ba wai tsayawa kallona ba ? tai saurin d’auke idanunta akansa ta sunkuyar kasa saboda tsananin kunyar data mamayeta ahankali ta kamo yatsun hannunta tana wasa dashi “zamuyi aiki ne akan wani project kuma ina son kece zakiyi .”yayi mgnr yana dago kwayar idanunshi ya zuba mata adaidai lokacin da itama ta d’ago nata kwayar idanun nan take idanunsu ya tsarke cikin juna wani abu suka ji ya tsarga masu alokacin daya yana bin jijiyoyin jikinsu barin ma ata wanda taji tamkar ana fizgar ransa ne .”

A natse ta gyada masa kanta alamun ta gamsu cigaba da kallonta yayi tare da yi mata bayanin yadda yake son aikin ya kasance still kwayar idanu shi na cikin nata dole so yake ya dasa qaunarsa cikn zuciyarta domin ta hakan ne kawai zai samu saukin fahimtar daita sirrin dake ransa .”ya mike tsaye daga Kan kujerarsa ya d’auki system dinsa ya zagayo zuwa inda take zaune , ya zagayeta da hannunwansa duka yana nuna mata irin aikin da yake bukata yana nuna mata yana shakar numfashinta yayinda kamshi turarensa ya dinga sakata jin mummunar fad’uwar gaba mai karfi .” ya dauki tsawon lokaci suna haka kafin daga bisani ya ajiye system a gabanta ya zuba hannuwansa ciki aljihu “ina fatan kin fahimci abinda nake bukata ?In sha allahu zanyi aiki mai kyau zan kwantar da hankali nayi maka abinda kake bukata” da kyau ya fad’a ya dauki file yana dubawa muryarta na rawa tace “sir ko zan iya tafiya ?da hannunsa yayi mata alamar zata wucewa ta mike tsaye da kyar ta wuce tana mamakin hali irin nasa tunda take bata ganin mutun irinsa ba mai jin kai ,mulki da nuna isa ko da yake shi din mai tarin kudi ne kudi kuma babu abinda basa saka mutu .”

Jiki a sanyaye ta koma office ta soma aikin da sectary ta bata bata wani dauki lokaci ba ta kammala ta kai mata ta dawo office byn Kmr minti goma ata yasa aka kira ta shigo da sallama ta tsaya cike da girmamawa tace “sir gani ! “set !ya fada yana kokarin bude system sannan ya fara magana ina bukatar fresh design na kamfanin wanda yafi AGC kuma ana bukatarsa ne cikin kwana daya kacal d’an haka sai ki shirya aikinsa daga yanzu “amman sir ko zai zama kwana biyu saboda na samu natsuwar yinsa akan tsari ?”no ! ya fad’a tare da tashi tsaye ya fice daga office din ya barta zaune .” ta juya da sauri tana bin bayansa da kallo yana tafiya a natse hannunsa daya cikin aljihunsa ,goshinta ta dafe “wannan wani irin mutun ne sam baya tsayawa yaji raayin mutun babu yadda ta iya haka ta mike ta fito ta koma office ta fara shirin aiki.”

Tana zaune a office tayi concentrate sosai akan aikinta ya shigo ya tsaya akanta yana qare mata kallo kamshin daddan turarensa ne yasa ta d’ago kwayar idanunta ganishi tayi tsaye rungume da hannunwansa duka a qirji yana kallonta da tsumammun idanunshi shiru tai tana mamakin irin kallon da yake mata, fahimta yayi zata iya fassara kallonsa gareta yasa cike da sanyin jiki ya soma magana “har zuwa wani lokaci zaki kammala da wannna aikin? shiru tayi kawai tana dubansa na second biyu sannan tace “sir ina Kan kokarin yi”Kinsan dai na fad’a miki akwana daya ake bukata daga yanzu zuwa gobe da safe kenan “na sani sir zanyi qoqari in sha allahu na kammala yanzu haka ma nayi nisa so..” bai tsaya jin mai zatace ba ya fita ya barta bude da baki .”byn Kmr awa daya ya sake shigowa ya kai hannu ya d’auki makeken takadar zanenta yana dubawa ta dan kallesa ta dauke kanta tana rausayar da kwayar idanunta Kan zanen da take ji yayi kamar ya zube ajikinta ya rungumeta tsam ajikinsa yana mugun qaunar kallonta . can ya ajiye takardar ya maida kansa ga kallonta idanunta na Kan takadar zane har guda biyu “wannan zanen bai min ba gasky .” ya fad’a a tsawa ce.”
Chapter 17 · 0% Book details