Sashe 48
Kundin Cinikayya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ga saƙon da na tura wa Zubaida, warning ne. Kuma cikin nan tabbas nawa ne. Amma ba da yardata na same ta ba.”
Sai kowa ya tsaya cak. Zubaida ta lumshe ido, Zahra ta rufe bakinta da hannu. Sooraj yana riƙe da wayar, yana karanta saƙon.
Da sauri Zahra ta nufi inda yake tare da ƙwace wayar ta fasa.
Dariya Zubaida ta kwashe da shi ta ce. "Hakan me ya sa za ki fasa wayar, dama kenen da gaske kina da cikin Junaid bamu sani ba, dama ke ƴar iska ce ba budurwa ba, tirr da wannan halin ki, ya kamata a hukunta ki, domin wanda yayi hakan hukunci yana kansa, banza ƴar talakawa ashe haka ki ke".
Nan take hawaye ya fara gangaro wa kan fuskar Zahra. Nuna kanta Zahra ta yi ta ce. "Zubaida ke da nake ƙoƙarin kare wa za ki maida abin ya juye kaina?".
MANAGE PAGE. HAR YANZU WAYATA BATA GYARU BA
TOH ME SOORAJ ZAI YANKE? YAYA JAMA'A ZA SU ƊAUKI WANNAN SABON BAYANI? SHIN ZAI GOYI BAYAN ZUBAIDA KO YA RUNGUMI GASKIYA.
ALƘALAMIN
A'ISHA MB
ZINARIYAR JAJIRTATTU
[8/21, 8:01 AM] AYEESHER MB💞💞💞: 🔥KUNDIN CINIKAYYA🌍
A’ISHA M.B 💞
BOOK 2 – Page
1️⃣1️⃣4️⃣➡️1️⃣1️⃣5️⃣
Nan take ga baki ɗaya suka kalli juna tare da fashe wa da dariya. Sannan suka ce. "Prank me". Daidai lokacin su Mrs Lailah da su Umar tare da su Aliyu suka shigo masarauta. Bayan sauko warsu daga cikin mota. Su Safira da Amrah suka nufi inda Zahra take. Nan Masarautar ta amsa da muryoyin mutane. Suna faɗin. "Happy birthday to you, happy birthday to you, happy birthday, happy birthday, to you". Nan Sooraj ya ce. "Triplet Allah ya ƙaro shekaru masu albarka".
Share hawayenta Zahra ta yi sannan ta ce. "Kenan kuna nufin duk wannan abin da ya faru prank me?".
Nan Zubaida ta ce. "Kwarai kuwa, duk abin da ki ka ga ya faru to da sanin mu kuma duk shirin mu ne munyi hakan ne domin muyi pranking ɗin ki sannan mutaya ke da 'yan uwanki murnar ƙarin shekara".
Share hawayenta Zahra ta yi sannan ta kalle su ɗaya bayan ɗaya ta girgiza kai ta ce. "Wato shi ne kuka sa nai asaran hawaye na, kuka sa na shiga damuwa, da a ce zuciyata ta buga na mutu fa kenan duk wannan haka za ku ce prank ne?, lallai ma wallahi kun bani mamaki, to ni ba na so, Kuma kada a ƙara yi min irin wannan abun".
Kallonta Mami ta yi ta ce. "Ni kaina ban san prank suka yi miki ba, dai daga baya. Kiyi haƙuri don Allah, wallahi ban sani ba da a ce na sani da bazan biye musu ba sannan ga mahaifiyarku ma ta zo ya kamata a ce kin haƙura kuma omai ya wuce".
Kallonta Zubaida ta yi ta ce. "Yau fa ranar zagayowar haihuwar ki ne, kamata ai a ce yanzu kina farin ciki ba sai ɓacin rai ba. Kiyi farin ciki Zahra ga ƴan uwanki ma sun zo kinga wani ƙarin farin cikin ne".
Murmushi wanda yafi kuka ciwo Zahra ta yi ta ce. "Nayi farin ciki?, nayi farin cikin ne fa ki ka ce. Hmmm, kowanne birthday, kamar sabuwar ƙafa ce da nake ɗauka ina takawa kusa da kabarina.”
“Wani lokacin nakan tambayi kaina, mene ne muke murna a zagayowar shekara? Shin saboda mun ƙara tsufa ne, ko saboda muna ƙara raguwa a lokacin da ya rage mana?”
“A ganin mutane zagayowar shekara alama ce ta sabuwar dama amma a gare nu, alama ce ta ƙarewar lokaci.”
Sannan ya maida kallonta kan Mrs Lailah ta ce. "Ummah kiyi haƙuri ban so ki ka ganni a irin wannan yanayin ba, banason aikata wani da zai ɗaga miki hankali, yanzu bana cikin sukuni, ba zan iya yin wani hira ko abi na farin ciki ba, yanzu haka zuciyata hutu take buƙata. Ummah zan tafi. Kuyi haƙuri gaba ɗaya".
Jikin kowanensu ta mutun jin furucin Zahra.
Ta faɗa da zimmar zata tafi. Nan kuma saita tsaya, tare da maida kallonta kan mahaifiyarta tare da sakin fuska ta ce. "Amma matsalar Ummah ba zan iya tafiya ba tare da kin min magana ba". Ta faɗa tare da zuwa wajan Miss Lailah sannan ta rungume ta.
Murmushi miss Lailah ta yi ta ce. "Allah ya yi miki albarka".
Shi kuwa Sooraj mamaki ma ya sa ya kasa furta komai.
Daga cikin rungumar da suka yi, Mrs Lailah ta dafa bayanta a hankali, tana shafa kanta. Sannan cikin nutsuwa ta ce. "Zahra ni na haife ki, na fi kowa sanin lokacin da ki ke buƙatar shiru. Amma kada ki manta da wannan, ba kowane hawaye ba ne rashin sa'a, wasu hawaye alama ce ta tsarkakkiyar zuciya, ta zuciyar da ke jin komai da gaske. Ki yarda da zuciyarki, amma kada ki kashe farin ciki gaba ɗaya".
Zahra ta ɗaga kai ta dubi Mahaifiyarsu da ido mai cike da kwalla cikin tsantsar girmamawa. "Ummah, na gode. Ina jin kalamanki har cikin ƙasusuwana. Zan yi ƙoƙari. Amma ki bari na sami ɗan natsuwa, kawai wuri da zan zauna ni kaɗai, da tunanina, ba tare da kowa ba. Sai an jima". Ta faɗa.
Safira ta riƙe hannun Amrah tana cewa. "Wallahi na taɓa jin an ce idan mace mai taushin zuciya ta fara magana da zafi to akwai abinda ke huda zuciyarta".
Nan Mami ta janyo Zahra yayin da suka sa ta manta abinda ya faru. Nan haka haɗa babban shagali. Bayan an gama shagulgula da murnar zagayowar ranar haihuwar ƴan uku, kowa ya watse cikin farin ciki. Masarauta ta cika da dariya da nishaɗi. An ci an sha, an raira wakoki, yara da manya sun more. Daga karshe, Mami ta cika jakunkuna goma na arziki, kayan kyaututtuka, tsabar kuɗi, da kayan marmari, ta ba Miss Lailah da su tafi da su zuwa Jigawa.
Su Zubaida, Zahra da Sooraj kuwa sun nufi gida cikin motar Sooraj. Zahra na gefe, ta yi shiru cikin nazari. Zubaida kuwa bata ce uffan ba, tana nazarin abubuwan da ke faruwa. Daga fuskar ta, akwai abin da ke damunta.
Sun isa gida lafiya. Amma tuni Zubaida ta fara canzawa. Zuciyarta ta cika da ƙiyayya da fargaba, tana zargin cewa Sooraj yana son Zahra. Kullum idan Sooraj ya dubi Zahra, idan ya yi mata murmushi, idan Zubaida na jin zuciyarta kamar ta fashe.
Wata rana Zahra na zaune a falonsu tana karanta wani littafi, cikin rigar atamfa mai kyau da kwalliya irin ta mata masu tsafta da iya gyaran kai. Sooraj ya shigo falon, yana ta kokarin gyara waya a hannunsa, sannan ya ce da ita.
"My Zahra, kin ƙara kyau wallahi." Ya faɗa murmushi kan fuskarsa. Zahra ta saki murmushi ta ce. "Na gode".
Nan Zubaida ta ce.
"Zahra, dan Allah ki rage sa irin waɗannan kayan. Idan kin san kina da aure, ki dinga kamun kai. Kin fi dacewa da sutura mai da’a."
Nan Zahra ta juyo da idanta gare ta ta ce. "Wallahi kinyi ƙarya."
Zubaida ta zaro ido. "Me ki ke nufi da ƙarya?"
Zahra ta ce da girmamawa mara laifi,
"Kinyi ƙarya idan kina tunanin ni zan canza saboda ke. Idan kuma saboda kaya ne kike jin ciwon zuciya, to yanzu na fara. Ki daure ki ƙara kishi har ya hure miki ido."
Zubaida ta kasa amsa. Maganganun Zahra sun fada mata zuciya kamar ƙibiyar da aka sa wa wuta. Zahra ta ci gaba da cewa.
"Kina yawo kina nuna Sooraj naki ne, naki ne. An gaya miki duk abin da ki ka shirya a kaina ban sani ba?, duk shige da ficen ki dan ki mallake shi duk babu wanda ban sani ba. Saboda haka idan kina da damuwa, sai ki shafa man zafi. Ni kuwa zan yi duk abin da nake so a gabansa har ki yi kuka ki sha hawaye."
Zubaida ta runtse ido, hawaye na neman zubo mata amma sai ta juya ba tare da ta ce uffan ba.
Daga wannan rana, Zahra ta sauya gaba ɗaya. Duk inda Zubaida ke, sai Zahra ta gwada ta da kulawa fiye da yadda kowacce mata za ta so a nuna wa mijinta. Idan suna zaune suna cin abinci, Zahra kan ce. "My love, ƙara tuwon nan kaɗan mana, ina so ka ƙara kiba."
Zubaida na gefe, zucisrta yana cike da wuta.
Wannan sauyin na Zahra ba haka kawai ba ne, hakan ya faru ne a dalilin wata rana lokacin da Zahra ke shirin fita zuwa Garden, ta tsaya kusa da ƙofar ɗakin Zubaida domin ɗaukar takalminta. Bai kamata ta ji ba, amma sai ta jiyo murya daga cikin ɗakin, kamar ana waya, kuma kamar ana magana da zuciya.
Zubaida ce ke magana a waya tana faɗin. "Wallahi sai na mallaki Yarima Sooraj. Ko me zai faru. Zahra ba komai bace a gabana. Da sannu zan kore ta daga gidan nan. Ina da yanda zan yi."
Zahra ta tsaya kamar an dasa ta. Idonta ya cika da ƙwalla, amma ta dannata. Ta juya ba tare da ta yi magana ba. Amma zuciyarta ta ƙona kamar wutar daji.
Tun daga wannan rana, Zahra ta ɗaura ɗamara. Bata sake zama irin Zahra mai jurewa ba.
Wannan shi ne.
Zubaida ba ta iya cin wannan maganar haka ba. Ta wuce ɗaki, tana kukan rai. Washe gari ta tura saƙo zuwa wayar Zahra da nufin barazana.
"Zahra, idan kika ci gaba da wannan hali, sai na tabbatar kin fita daga gidan nan da kuka da nadama. Ki dinga rike baki da kamun kai. Kar ki farka da bala’i."
Zahra ta karanta saƙon tana dariya mai ɓacin rai. Ta ce a ranta:
"To, yanzu ne farawa. Ba ke kika fara ba? Muje zuwa."
A daren ranar, Zahra na zaune cikin ɗakin Sooraj, fuskar ta ɗaure tamkar wacce aka ci amanarta. Ta kalle shi, sannan cikin murya mai cike da ciwo da daci ta ce,
"Ka san kuwa har yanzu fushi nake da kai? Duk wannan wasa da muke a gaban Zubaida, bana jin daɗi da kai ko kaɗan."
Murmushi Sooraj ya yi ya ce. "Hmm nima na sani shi ya sa na biye miki".
Sai kowa ya tsaya cak. Zubaida ta lumshe ido, Zahra ta rufe bakinta da hannu. Sooraj yana riƙe da wayar, yana karanta saƙon.
Da sauri Zahra ta nufi inda yake tare da ƙwace wayar ta fasa.
Dariya Zubaida ta kwashe da shi ta ce. "Hakan me ya sa za ki fasa wayar, dama kenen da gaske kina da cikin Junaid bamu sani ba, dama ke ƴar iska ce ba budurwa ba, tirr da wannan halin ki, ya kamata a hukunta ki, domin wanda yayi hakan hukunci yana kansa, banza ƴar talakawa ashe haka ki ke".
Nan take hawaye ya fara gangaro wa kan fuskar Zahra. Nuna kanta Zahra ta yi ta ce. "Zubaida ke da nake ƙoƙarin kare wa za ki maida abin ya juye kaina?".
MANAGE PAGE. HAR YANZU WAYATA BATA GYARU BA
TOH ME SOORAJ ZAI YANKE? YAYA JAMA'A ZA SU ƊAUKI WANNAN SABON BAYANI? SHIN ZAI GOYI BAYAN ZUBAIDA KO YA RUNGUMI GASKIYA.
ALƘALAMIN
A'ISHA MB
ZINARIYAR JAJIRTATTU
[8/21, 8:01 AM] AYEESHER MB💞💞💞: 🔥KUNDIN CINIKAYYA🌍
A’ISHA M.B 💞
BOOK 2 – Page
1️⃣1️⃣4️⃣➡️1️⃣1️⃣5️⃣
Nan take ga baki ɗaya suka kalli juna tare da fashe wa da dariya. Sannan suka ce. "Prank me". Daidai lokacin su Mrs Lailah da su Umar tare da su Aliyu suka shigo masarauta. Bayan sauko warsu daga cikin mota. Su Safira da Amrah suka nufi inda Zahra take. Nan Masarautar ta amsa da muryoyin mutane. Suna faɗin. "Happy birthday to you, happy birthday to you, happy birthday, happy birthday, to you". Nan Sooraj ya ce. "Triplet Allah ya ƙaro shekaru masu albarka".
Share hawayenta Zahra ta yi sannan ta ce. "Kenan kuna nufin duk wannan abin da ya faru prank me?".
Nan Zubaida ta ce. "Kwarai kuwa, duk abin da ki ka ga ya faru to da sanin mu kuma duk shirin mu ne munyi hakan ne domin muyi pranking ɗin ki sannan mutaya ke da 'yan uwanki murnar ƙarin shekara".
Share hawayenta Zahra ta yi sannan ta kalle su ɗaya bayan ɗaya ta girgiza kai ta ce. "Wato shi ne kuka sa nai asaran hawaye na, kuka sa na shiga damuwa, da a ce zuciyata ta buga na mutu fa kenan duk wannan haka za ku ce prank ne?, lallai ma wallahi kun bani mamaki, to ni ba na so, Kuma kada a ƙara yi min irin wannan abun".
Kallonta Mami ta yi ta ce. "Ni kaina ban san prank suka yi miki ba, dai daga baya. Kiyi haƙuri don Allah, wallahi ban sani ba da a ce na sani da bazan biye musu ba sannan ga mahaifiyarku ma ta zo ya kamata a ce kin haƙura kuma omai ya wuce".
Kallonta Zubaida ta yi ta ce. "Yau fa ranar zagayowar haihuwar ki ne, kamata ai a ce yanzu kina farin ciki ba sai ɓacin rai ba. Kiyi farin ciki Zahra ga ƴan uwanki ma sun zo kinga wani ƙarin farin cikin ne".
Murmushi wanda yafi kuka ciwo Zahra ta yi ta ce. "Nayi farin ciki?, nayi farin cikin ne fa ki ka ce. Hmmm, kowanne birthday, kamar sabuwar ƙafa ce da nake ɗauka ina takawa kusa da kabarina.”
“Wani lokacin nakan tambayi kaina, mene ne muke murna a zagayowar shekara? Shin saboda mun ƙara tsufa ne, ko saboda muna ƙara raguwa a lokacin da ya rage mana?”
“A ganin mutane zagayowar shekara alama ce ta sabuwar dama amma a gare nu, alama ce ta ƙarewar lokaci.”
Sannan ya maida kallonta kan Mrs Lailah ta ce. "Ummah kiyi haƙuri ban so ki ka ganni a irin wannan yanayin ba, banason aikata wani da zai ɗaga miki hankali, yanzu bana cikin sukuni, ba zan iya yin wani hira ko abi na farin ciki ba, yanzu haka zuciyata hutu take buƙata. Ummah zan tafi. Kuyi haƙuri gaba ɗaya".
Jikin kowanensu ta mutun jin furucin Zahra.
Ta faɗa da zimmar zata tafi. Nan kuma saita tsaya, tare da maida kallonta kan mahaifiyarta tare da sakin fuska ta ce. "Amma matsalar Ummah ba zan iya tafiya ba tare da kin min magana ba". Ta faɗa tare da zuwa wajan Miss Lailah sannan ta rungume ta.
Murmushi miss Lailah ta yi ta ce. "Allah ya yi miki albarka".
Shi kuwa Sooraj mamaki ma ya sa ya kasa furta komai.
Daga cikin rungumar da suka yi, Mrs Lailah ta dafa bayanta a hankali, tana shafa kanta. Sannan cikin nutsuwa ta ce. "Zahra ni na haife ki, na fi kowa sanin lokacin da ki ke buƙatar shiru. Amma kada ki manta da wannan, ba kowane hawaye ba ne rashin sa'a, wasu hawaye alama ce ta tsarkakkiyar zuciya, ta zuciyar da ke jin komai da gaske. Ki yarda da zuciyarki, amma kada ki kashe farin ciki gaba ɗaya".
Zahra ta ɗaga kai ta dubi Mahaifiyarsu da ido mai cike da kwalla cikin tsantsar girmamawa. "Ummah, na gode. Ina jin kalamanki har cikin ƙasusuwana. Zan yi ƙoƙari. Amma ki bari na sami ɗan natsuwa, kawai wuri da zan zauna ni kaɗai, da tunanina, ba tare da kowa ba. Sai an jima". Ta faɗa.
Safira ta riƙe hannun Amrah tana cewa. "Wallahi na taɓa jin an ce idan mace mai taushin zuciya ta fara magana da zafi to akwai abinda ke huda zuciyarta".
Nan Mami ta janyo Zahra yayin da suka sa ta manta abinda ya faru. Nan haka haɗa babban shagali. Bayan an gama shagulgula da murnar zagayowar ranar haihuwar ƴan uku, kowa ya watse cikin farin ciki. Masarauta ta cika da dariya da nishaɗi. An ci an sha, an raira wakoki, yara da manya sun more. Daga karshe, Mami ta cika jakunkuna goma na arziki, kayan kyaututtuka, tsabar kuɗi, da kayan marmari, ta ba Miss Lailah da su tafi da su zuwa Jigawa.
Su Zubaida, Zahra da Sooraj kuwa sun nufi gida cikin motar Sooraj. Zahra na gefe, ta yi shiru cikin nazari. Zubaida kuwa bata ce uffan ba, tana nazarin abubuwan da ke faruwa. Daga fuskar ta, akwai abin da ke damunta.
Sun isa gida lafiya. Amma tuni Zubaida ta fara canzawa. Zuciyarta ta cika da ƙiyayya da fargaba, tana zargin cewa Sooraj yana son Zahra. Kullum idan Sooraj ya dubi Zahra, idan ya yi mata murmushi, idan Zubaida na jin zuciyarta kamar ta fashe.
Wata rana Zahra na zaune a falonsu tana karanta wani littafi, cikin rigar atamfa mai kyau da kwalliya irin ta mata masu tsafta da iya gyaran kai. Sooraj ya shigo falon, yana ta kokarin gyara waya a hannunsa, sannan ya ce da ita.
"My Zahra, kin ƙara kyau wallahi." Ya faɗa murmushi kan fuskarsa. Zahra ta saki murmushi ta ce. "Na gode".
Nan Zubaida ta ce.
"Zahra, dan Allah ki rage sa irin waɗannan kayan. Idan kin san kina da aure, ki dinga kamun kai. Kin fi dacewa da sutura mai da’a."
Nan Zahra ta juyo da idanta gare ta ta ce. "Wallahi kinyi ƙarya."
Zubaida ta zaro ido. "Me ki ke nufi da ƙarya?"
Zahra ta ce da girmamawa mara laifi,
"Kinyi ƙarya idan kina tunanin ni zan canza saboda ke. Idan kuma saboda kaya ne kike jin ciwon zuciya, to yanzu na fara. Ki daure ki ƙara kishi har ya hure miki ido."
Zubaida ta kasa amsa. Maganganun Zahra sun fada mata zuciya kamar ƙibiyar da aka sa wa wuta. Zahra ta ci gaba da cewa.
"Kina yawo kina nuna Sooraj naki ne, naki ne. An gaya miki duk abin da ki ka shirya a kaina ban sani ba?, duk shige da ficen ki dan ki mallake shi duk babu wanda ban sani ba. Saboda haka idan kina da damuwa, sai ki shafa man zafi. Ni kuwa zan yi duk abin da nake so a gabansa har ki yi kuka ki sha hawaye."
Zubaida ta runtse ido, hawaye na neman zubo mata amma sai ta juya ba tare da ta ce uffan ba.
Daga wannan rana, Zahra ta sauya gaba ɗaya. Duk inda Zubaida ke, sai Zahra ta gwada ta da kulawa fiye da yadda kowacce mata za ta so a nuna wa mijinta. Idan suna zaune suna cin abinci, Zahra kan ce. "My love, ƙara tuwon nan kaɗan mana, ina so ka ƙara kiba."
Zubaida na gefe, zucisrta yana cike da wuta.
Wannan sauyin na Zahra ba haka kawai ba ne, hakan ya faru ne a dalilin wata rana lokacin da Zahra ke shirin fita zuwa Garden, ta tsaya kusa da ƙofar ɗakin Zubaida domin ɗaukar takalminta. Bai kamata ta ji ba, amma sai ta jiyo murya daga cikin ɗakin, kamar ana waya, kuma kamar ana magana da zuciya.
Zubaida ce ke magana a waya tana faɗin. "Wallahi sai na mallaki Yarima Sooraj. Ko me zai faru. Zahra ba komai bace a gabana. Da sannu zan kore ta daga gidan nan. Ina da yanda zan yi."
Zahra ta tsaya kamar an dasa ta. Idonta ya cika da ƙwalla, amma ta dannata. Ta juya ba tare da ta yi magana ba. Amma zuciyarta ta ƙona kamar wutar daji.
Tun daga wannan rana, Zahra ta ɗaura ɗamara. Bata sake zama irin Zahra mai jurewa ba.
Wannan shi ne.
Zubaida ba ta iya cin wannan maganar haka ba. Ta wuce ɗaki, tana kukan rai. Washe gari ta tura saƙo zuwa wayar Zahra da nufin barazana.
"Zahra, idan kika ci gaba da wannan hali, sai na tabbatar kin fita daga gidan nan da kuka da nadama. Ki dinga rike baki da kamun kai. Kar ki farka da bala’i."
Zahra ta karanta saƙon tana dariya mai ɓacin rai. Ta ce a ranta:
"To, yanzu ne farawa. Ba ke kika fara ba? Muje zuwa."
A daren ranar, Zahra na zaune cikin ɗakin Sooraj, fuskar ta ɗaure tamkar wacce aka ci amanarta. Ta kalle shi, sannan cikin murya mai cike da ciwo da daci ta ce,
"Ka san kuwa har yanzu fushi nake da kai? Duk wannan wasa da muke a gaban Zubaida, bana jin daɗi da kai ko kaɗan."
Murmushi Sooraj ya yi ya ce. "Hmm nima na sani shi ya sa na biye miki".