Sashe 45
Kundin Cinikayya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*BOOK 2 PAGE1️⃣1️⃣0️⃣➡️1️⃣1️⃣1️⃣*
________________________
Da sauri Zubaida ta bi bayan Sooraj domin kada ya tona mata asiri. Daidai lokacin ta ga Zahra ta fito daga part ɗin ta. Da sauri Zubaida ta ja burki kana ta wayance da faɗin. "Wai ina na saka waya na ne?". Ta faɗa tana dube-dube.
Girgiza kai kawai Zahra ta yi ta ce. "Hmmm inda ranka zaka sha kallo, wai ga waya a hannun mutum amma bai san da ita a hannunsa".
Sai a lokacin Zubaida ta tuna cewa da ashe da wayarta a hannunta. Ɓata fuska ta yi ta ce. "Toh sai me?, ina ruwanki da hakan?, aikin banza". Ta faɗa tare da koma wa part ɗin ta.
________________
Dutse
Zaune suke a parlour suna cin abinci kallonta ya yi annuri kan fuskarsa ya ce. "Kin san mene ne my wife?". Girgiza kai Safira ta yi alamun a'a.
Nan ya kalle ta ya ce. "A gaskiya ina cikin farin ciki mara misaltuwa, kin cika min burina, i love you so much my wife, Allah ya bamu kwanciyar hankali da nutsuwa a zaman mu".
Murmushi Safira ta yi tare da amsa wa da. "Ameen". Bayan sun gama cin abincin Safira ta tattara abubuwan da suka ci abinci da su ta kai kitchen tare da wanke wa. Dawo wa ta yi sannan ya dube shi ta ce. "Bari naje na haɗa maka ruwan zafin da za ka yi wanka da shi".
Tashi Aliyu ya yi tare da janyo ta jikinta sannan ya rungume ta yana mai faɗin. "No Safira, bana son ki wahalar min da kanki, tunda safe ki ke ta aiki a gidan nan, ni yanzu ina buƙatar ki a kusa da ni, ina son ki bani lokacin ki".
Cire jikin ta Safira ta yi daga nashi ta ce. "A'a Habibi ni da na ce maka na gaji, ka barni yanzu haka ma wanka nake ƙoƙarin zuwa nayi sai nayi bacci kaɗan kafin nan kuma na san kaima ka dawo daga office ko. Yanzu dai ka tawo na fara saka maka ruwan zafin da za ka yi wanka idan ya so daga baya sai ni naje nayi nawa".
Murmushi Aliyu ya yi ya ce. "Wai wai ya ga ya miki cewar ango yana fita office?, to albishirinki, hutun wata guda haka bani a office dan haka kinga babu inda zani muna tare. Muje yanzu sai kiyi min wankan".
Rufe fuskarta Safira ta yi alamun kunya ta ce. "Ni ba zan iya ba kaje kayi kawai". Ta faɗa tare da saurin shiga ɗakinta. Kallon love kawai ya bita da shi tare da girgiza kansa. Sosa lallausar sumar kansa ya yi cikin wani irin yanayi na farin ciki, kana daga bisani ya bi bayanta.
Ɓangare su Umar kuwa. Babu abin da yake faman yi sai kallon kyakkyawar fuskar matarsa Amrah, yayin da yake ji tamkar yafi kowa sa'ar samun mata a duniya.
Ganin yadda yake ta binta da kallo ya sa Amrah ta kauda fuskarta sannan ta ce. "Yah Umar ka daina min irin wannan kallon". Ta faɗa a shagwaɓe.
Sakin murmushi Umar ya yi ya ce. "Amrah kenan, toh idan ban kalle ki ba wata ki ke so na ke na kalla?, ko so ki ke naje na kalli wata?".
Nan take Amrah ta ɗauki pillow kujerar da ke kusa da ita ta wurga masa sannan ta ce. "Karka ƙara yi min maganar wata".
Fashe wa da dariya Umar ya yi ya ce. "Dama kina da kishi?, chabn lallai, ki ce bani ba ƙara aure".
Haɗe rai Amrah ta yi alamun ta yi fushi. Nan Umar ya haɗiye dariyar da ke cinsa sannan ya tako zuwa har inda take kana ya zauna kusa da ita. Ɗago da haɓarta ya yi sannan ya dube ta ya ce. "Kema kin san babu wata mace a raina ina ba ke ba, wasa fa nake miki kinji".
Mintsinin sa Amrah ta yi ta ce. "Toh ba zan haƙura ba har sai ka goya ni".
Murmushi Umar ya yi tare da tsugunna wa sannan ya ce. "Toh zo na goya ki".
Kunya ne ya kama Amrah inda ta ce. "Ni fa wasa nake maka, ka tashi kaji".
Girgiza kai Umar ya yi alamun ba zai tashi ba har sai ta su bayansa. Ganin yaƙi tashi ya sanya Amrah ta su bayansa sannan ya goya ta tamkar wata ƴar shekara biyar. Inda ya shiga zagaye gida da ita suna tafe yana binta da wasa da dariya.
Ɓangaren su Khairiyya da Ramlah kuwa, makarantar suka koma na University F.U.D inda suka cigaba da karantun su. Yayin da Usman ya tafi ƙasar waje domin ƙarasa master's ɗin sa.
__________________________
TWO WEEK'S LATER
Kano
Shigo wa Sooraj ya yi hannunsa riƙe da leda yayin da ya kira so Zubaida da Zahra izuwa parlour. Cikin mintuna ƙalilan suka hallara a parlourn.
Zama suka yi suna mai fuskantar shi. Kallonsu ya yi ya ce. "Dama na kira ki ne domin faɗa muku cewar na siya wa kowaccen ku sabuwar waya". Maida kallonsa ya yi kan Zubaida ya ce. "Zubaida za ki bani wayar hannun ki da layin da ke ciki, wannan sabuwar wayar da na siya na saka wa kowaccen ku sabon layi a ciki".
Ɓata fuska Zubaida ta yi ta ce. "Kamar ya na bada waya na da layi na?, idan ƙawayena suka kira ni baya shiga fa?, ko kuwa Babana ya kira ko aka yi min kiran gaggawa ya sanyi?".
Haɗe rai Sooraj ya yi tamkar bai taɓa dariya ba ya ce. "Wannan ba damuwata bace ba, ni ke da iko a kanki dan haka ni ke da damar yanke duk abin da na gadama, maza ki ajiye wayar ki da sim card ɗin ki".
Yamutse fuska Zubaida ta yi kamar za ta yi kuka ta ce. "Toh ita Zahra ba za ka ƙwace nata ba sai ni kaɗai ".
Murmushi Sooraj ya yi ya ce. "Zahra ba ta da waya, shi ya sa ki ka ga ban tambaye ta ba".
Babu yacce Zubaida ta iya haka ta ɗauki wayarta da sim card ɗin ciki ta bawa Sooraj.
Nan ya miƙa mata sabuwar waya wacce ta kasance android Samsung Galaxy ya bata, sannan ya ɗauki iPhone 15 ya miƙa wa Zahra.
Nan take ran Zubaida ya ɓaci. Zumbur ta miƙe sannan ta ce. "Wannan ai rashin adalci ne, ya za'a yi ka siya min android phone ita kuma ka siya mata iPhone, wallahi nima iPhone ɗin nake so". Ta faɗa tare da riƙe ƙugu tamkar wacce zata yi dambe.
Ajiyar zuciya Zahra ta sauke, kana ta miƙe tsaye ta maida kallonta izuwa su biyun sannan ta dubi Sooraj ta ce. "Ni waya bata dame ni ba, saboda tunda nake ban taɓa riƙe waya nawa ba, dan haka ka bata guda biyun kawai, ita da ya dame ta sai ta riƙe. Ni yanzu ko ka bani wayar ma ban san me zan yi da ita ba".
Ta faɗa tare da kokarin koma wa part ɗin ta.
Nan ta ji muryar Sooraj daga sama ya ce. "Kada ki kuskure ki ƙara taku koda ɗaya ne". Chakk Zahra ta tsaya yayin da ta juyo kana ta maida kallonta kansa.
Haɗiye fusatar da Sooraj ya yi ya ce. "A kan me zan siyo muku abu kowaccen ku ta ce bata buƙata?, kenen ni ne wanda ban san me zan yi da kuɗi ba kenen. Ba laifin ku ba ne, laifi na ne".
Murmushi Zahra ta yi ta ce. "Mai gida kenen, ai dama chan baka San abin da za ka yi da kuɗi ba, da a ce ka san mahimmancin kuɗi a yanzu dai ba za ka ɗauko mana batun waya ba, a masarauta ma'akaita nawa ne suke rasa na bawa ƴaƴansu abinda zasu da a baki?, matsayin ka na Yarima guda a gari kamata ai a ce kana taimakon mutane tare da basu sadaka, amma ni tunda na sanka ma ban taɓa ganin ka bada zakka ba, shin ka ta.......
Bata ƙarasa ba ta ji ya gauraye ta da zafafan mari har guda biyu, wanda ya sa Zahra yin mutuwar tsaye.
Nan take idanunsa suka kaɗa suka yi jajir. "Zahra ban yi niyyar marin ki ba dan dole kin san na mare ki, aikin banza kawai". Ya faɗa tare da wurga musu wayar sannan ya ce. "Idan kun gadama ku ɗauka, idan baku ɗauka na gaba ta kaini wallahi". Ya faɗa tare da shiga part ɗin sa.
Ɓangaren Zubaida kuwa sosai marin da Sooraj ya yi wa Zahra ya mata daɗi. Nan ta fara zargin cewa kamar Sooraj baya son Zahra. Ɗaukar android phone ɗin ta yi tare da barin Zahra wanda ke riƙe da ƙuncinta a tsaye. Kana ta nufi ɗaƙin ta ranta fal.
Ƙunci da baƙin ciki ne suka bi suka cunkushe guri guda a zuciyar Zahra. Share hawayenta ta yi kana ta girgiza kai ta koma part ɗin ta ba tare da ta ɗauki wayar da Sooraj ya siya ba.
Da daddare da misalin ƙarfe takwas Sooraj da Zubaida suka ci abinci a dining ba tare da Zahra ta fito ba. Shi kuwa Sooraj ko a jikinsa.
Bayan sun gama cin abinci. Kamar ance ya juya, nan ya juya ya ga wayar da ya siyo a ajiye Zahra bata ɗauka ba.
Kallon Zubaida ya yi ya ce. "Kema baki ɗauki wayar ba ko?". Girgiza masa kai Zubaida ta yi ta ce. "Na ɗauka mana, me zai ana ni ɗauka tunda na san banda wani zaɓi".
Girgiza kai ya yi kana ya nufi inda wayar take ya ɗauka sannan ya nufi part ɗin Zahra.
Shiga ya yi cikin part ɗinta nan ya ga bata cikin parlourn ta hakan ya sa shi shiga ɗakinta, nan ya ga ta duƙunƙune guri guda cikin bargo kan gado. Mamaki ne ya kama shi.
Dubanta ya yi ya ce. "Ke Zahra ki daina wannan wasan kwaikwayon ki karɓi wayarki, kinga bana son a ce mun fara samun matsala da ke".
Jin ta yi masa shiru hakan ya sa shi ajiye wayar kusa da ita sannan ya ja tsaki tare da juya wa zai fita. Nan wani zuciyar ya ce da shi kada ya fita. Dawo wa ta yi tare da taɓa ta.
________________________
Da sauri Zubaida ta bi bayan Sooraj domin kada ya tona mata asiri. Daidai lokacin ta ga Zahra ta fito daga part ɗin ta. Da sauri Zubaida ta ja burki kana ta wayance da faɗin. "Wai ina na saka waya na ne?". Ta faɗa tana dube-dube.
Girgiza kai kawai Zahra ta yi ta ce. "Hmmm inda ranka zaka sha kallo, wai ga waya a hannun mutum amma bai san da ita a hannunsa".
Sai a lokacin Zubaida ta tuna cewa da ashe da wayarta a hannunta. Ɓata fuska ta yi ta ce. "Toh sai me?, ina ruwanki da hakan?, aikin banza". Ta faɗa tare da koma wa part ɗin ta.
________________
Dutse
Zaune suke a parlour suna cin abinci kallonta ya yi annuri kan fuskarsa ya ce. "Kin san mene ne my wife?". Girgiza kai Safira ta yi alamun a'a.
Nan ya kalle ta ya ce. "A gaskiya ina cikin farin ciki mara misaltuwa, kin cika min burina, i love you so much my wife, Allah ya bamu kwanciyar hankali da nutsuwa a zaman mu".
Murmushi Safira ta yi tare da amsa wa da. "Ameen". Bayan sun gama cin abincin Safira ta tattara abubuwan da suka ci abinci da su ta kai kitchen tare da wanke wa. Dawo wa ta yi sannan ya dube shi ta ce. "Bari naje na haɗa maka ruwan zafin da za ka yi wanka da shi".
Tashi Aliyu ya yi tare da janyo ta jikinta sannan ya rungume ta yana mai faɗin. "No Safira, bana son ki wahalar min da kanki, tunda safe ki ke ta aiki a gidan nan, ni yanzu ina buƙatar ki a kusa da ni, ina son ki bani lokacin ki".
Cire jikin ta Safira ta yi daga nashi ta ce. "A'a Habibi ni da na ce maka na gaji, ka barni yanzu haka ma wanka nake ƙoƙarin zuwa nayi sai nayi bacci kaɗan kafin nan kuma na san kaima ka dawo daga office ko. Yanzu dai ka tawo na fara saka maka ruwan zafin da za ka yi wanka idan ya so daga baya sai ni naje nayi nawa".
Murmushi Aliyu ya yi ya ce. "Wai wai ya ga ya miki cewar ango yana fita office?, to albishirinki, hutun wata guda haka bani a office dan haka kinga babu inda zani muna tare. Muje yanzu sai kiyi min wankan".
Rufe fuskarta Safira ta yi alamun kunya ta ce. "Ni ba zan iya ba kaje kayi kawai". Ta faɗa tare da saurin shiga ɗakinta. Kallon love kawai ya bita da shi tare da girgiza kansa. Sosa lallausar sumar kansa ya yi cikin wani irin yanayi na farin ciki, kana daga bisani ya bi bayanta.
Ɓangare su Umar kuwa. Babu abin da yake faman yi sai kallon kyakkyawar fuskar matarsa Amrah, yayin da yake ji tamkar yafi kowa sa'ar samun mata a duniya.
Ganin yadda yake ta binta da kallo ya sa Amrah ta kauda fuskarta sannan ta ce. "Yah Umar ka daina min irin wannan kallon". Ta faɗa a shagwaɓe.
Sakin murmushi Umar ya yi ya ce. "Amrah kenan, toh idan ban kalle ki ba wata ki ke so na ke na kalla?, ko so ki ke naje na kalli wata?".
Nan take Amrah ta ɗauki pillow kujerar da ke kusa da ita ta wurga masa sannan ta ce. "Karka ƙara yi min maganar wata".
Fashe wa da dariya Umar ya yi ya ce. "Dama kina da kishi?, chabn lallai, ki ce bani ba ƙara aure".
Haɗe rai Amrah ta yi alamun ta yi fushi. Nan Umar ya haɗiye dariyar da ke cinsa sannan ya tako zuwa har inda take kana ya zauna kusa da ita. Ɗago da haɓarta ya yi sannan ya dube ta ya ce. "Kema kin san babu wata mace a raina ina ba ke ba, wasa fa nake miki kinji".
Mintsinin sa Amrah ta yi ta ce. "Toh ba zan haƙura ba har sai ka goya ni".
Murmushi Umar ya yi tare da tsugunna wa sannan ya ce. "Toh zo na goya ki".
Kunya ne ya kama Amrah inda ta ce. "Ni fa wasa nake maka, ka tashi kaji".
Girgiza kai Umar ya yi alamun ba zai tashi ba har sai ta su bayansa. Ganin yaƙi tashi ya sanya Amrah ta su bayansa sannan ya goya ta tamkar wata ƴar shekara biyar. Inda ya shiga zagaye gida da ita suna tafe yana binta da wasa da dariya.
Ɓangaren su Khairiyya da Ramlah kuwa, makarantar suka koma na University F.U.D inda suka cigaba da karantun su. Yayin da Usman ya tafi ƙasar waje domin ƙarasa master's ɗin sa.
__________________________
TWO WEEK'S LATER
Kano
Shigo wa Sooraj ya yi hannunsa riƙe da leda yayin da ya kira so Zubaida da Zahra izuwa parlour. Cikin mintuna ƙalilan suka hallara a parlourn.
Zama suka yi suna mai fuskantar shi. Kallonsu ya yi ya ce. "Dama na kira ki ne domin faɗa muku cewar na siya wa kowaccen ku sabuwar waya". Maida kallonsa ya yi kan Zubaida ya ce. "Zubaida za ki bani wayar hannun ki da layin da ke ciki, wannan sabuwar wayar da na siya na saka wa kowaccen ku sabon layi a ciki".
Ɓata fuska Zubaida ta yi ta ce. "Kamar ya na bada waya na da layi na?, idan ƙawayena suka kira ni baya shiga fa?, ko kuwa Babana ya kira ko aka yi min kiran gaggawa ya sanyi?".
Haɗe rai Sooraj ya yi tamkar bai taɓa dariya ba ya ce. "Wannan ba damuwata bace ba, ni ke da iko a kanki dan haka ni ke da damar yanke duk abin da na gadama, maza ki ajiye wayar ki da sim card ɗin ki".
Yamutse fuska Zubaida ta yi kamar za ta yi kuka ta ce. "Toh ita Zahra ba za ka ƙwace nata ba sai ni kaɗai ".
Murmushi Sooraj ya yi ya ce. "Zahra ba ta da waya, shi ya sa ki ka ga ban tambaye ta ba".
Babu yacce Zubaida ta iya haka ta ɗauki wayarta da sim card ɗin ciki ta bawa Sooraj.
Nan ya miƙa mata sabuwar waya wacce ta kasance android Samsung Galaxy ya bata, sannan ya ɗauki iPhone 15 ya miƙa wa Zahra.
Nan take ran Zubaida ya ɓaci. Zumbur ta miƙe sannan ta ce. "Wannan ai rashin adalci ne, ya za'a yi ka siya min android phone ita kuma ka siya mata iPhone, wallahi nima iPhone ɗin nake so". Ta faɗa tare da riƙe ƙugu tamkar wacce zata yi dambe.
Ajiyar zuciya Zahra ta sauke, kana ta miƙe tsaye ta maida kallonta izuwa su biyun sannan ta dubi Sooraj ta ce. "Ni waya bata dame ni ba, saboda tunda nake ban taɓa riƙe waya nawa ba, dan haka ka bata guda biyun kawai, ita da ya dame ta sai ta riƙe. Ni yanzu ko ka bani wayar ma ban san me zan yi da ita ba".
Ta faɗa tare da kokarin koma wa part ɗin ta.
Nan ta ji muryar Sooraj daga sama ya ce. "Kada ki kuskure ki ƙara taku koda ɗaya ne". Chakk Zahra ta tsaya yayin da ta juyo kana ta maida kallonta kansa.
Haɗiye fusatar da Sooraj ya yi ya ce. "A kan me zan siyo muku abu kowaccen ku ta ce bata buƙata?, kenen ni ne wanda ban san me zan yi da kuɗi ba kenen. Ba laifin ku ba ne, laifi na ne".
Murmushi Zahra ta yi ta ce. "Mai gida kenen, ai dama chan baka San abin da za ka yi da kuɗi ba, da a ce ka san mahimmancin kuɗi a yanzu dai ba za ka ɗauko mana batun waya ba, a masarauta ma'akaita nawa ne suke rasa na bawa ƴaƴansu abinda zasu da a baki?, matsayin ka na Yarima guda a gari kamata ai a ce kana taimakon mutane tare da basu sadaka, amma ni tunda na sanka ma ban taɓa ganin ka bada zakka ba, shin ka ta.......
Bata ƙarasa ba ta ji ya gauraye ta da zafafan mari har guda biyu, wanda ya sa Zahra yin mutuwar tsaye.
Nan take idanunsa suka kaɗa suka yi jajir. "Zahra ban yi niyyar marin ki ba dan dole kin san na mare ki, aikin banza kawai". Ya faɗa tare da wurga musu wayar sannan ya ce. "Idan kun gadama ku ɗauka, idan baku ɗauka na gaba ta kaini wallahi". Ya faɗa tare da shiga part ɗin sa.
Ɓangaren Zubaida kuwa sosai marin da Sooraj ya yi wa Zahra ya mata daɗi. Nan ta fara zargin cewa kamar Sooraj baya son Zahra. Ɗaukar android phone ɗin ta yi tare da barin Zahra wanda ke riƙe da ƙuncinta a tsaye. Kana ta nufi ɗaƙin ta ranta fal.
Ƙunci da baƙin ciki ne suka bi suka cunkushe guri guda a zuciyar Zahra. Share hawayenta ta yi kana ta girgiza kai ta koma part ɗin ta ba tare da ta ɗauki wayar da Sooraj ya siya ba.
Da daddare da misalin ƙarfe takwas Sooraj da Zubaida suka ci abinci a dining ba tare da Zahra ta fito ba. Shi kuwa Sooraj ko a jikinsa.
Bayan sun gama cin abinci. Kamar ance ya juya, nan ya juya ya ga wayar da ya siyo a ajiye Zahra bata ɗauka ba.
Kallon Zubaida ya yi ya ce. "Kema baki ɗauki wayar ba ko?". Girgiza masa kai Zubaida ta yi ta ce. "Na ɗauka mana, me zai ana ni ɗauka tunda na san banda wani zaɓi".
Girgiza kai ya yi kana ya nufi inda wayar take ya ɗauka sannan ya nufi part ɗin Zahra.
Shiga ya yi cikin part ɗinta nan ya ga bata cikin parlourn ta hakan ya sa shi shiga ɗakinta, nan ya ga ta duƙunƙune guri guda cikin bargo kan gado. Mamaki ne ya kama shi.
Dubanta ya yi ya ce. "Ke Zahra ki daina wannan wasan kwaikwayon ki karɓi wayarki, kinga bana son a ce mun fara samun matsala da ke".
Jin ta yi masa shiru hakan ya sa shi ajiye wayar kusa da ita sannan ya ja tsaki tare da juya wa zai fita. Nan wani zuciyar ya ce da shi kada ya fita. Dawo wa ta yi tare da taɓa ta.