Sashe 24
Kundin Cinikayya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Maza ku fice min daga ɗakin ƴan wahala kawai".
Jikin kowannensu ne ya yi sanyi ganin a karo na farko Mami ta tsawatar musu. Simi-simi suka fita ba tare da wanin su ya ce ƙala ba.
Zama Mami ta yi a bakin kujera tana mai maida numfashi. Hawaye ne ya sauka kan fuskarta.
Duk abinda ya faru su Amrah naji yayin da Safira ta kalli Amrah ta ce. "Lallai Mami tana fuskantar kalubale, hanya ba za mu taimaka mata ba?".
Murmushi Amrah ta yi ta ce. "Hmm wai shin kin manta akwai Zahra, indai har Zahra na raye ba ta mutu ba, to tabbas ita ɗaya ta ishe su, bama sai mun taimaka mata ba, Zahra ai ita ce daidai da su".
Murmushi Safira ta yi ta ce. "Haka ne, nidai fata na shi ne Allah ya sa Zahra tana cikin ƙoshin lafiya, sannan Allah ya bawa yarima Sooraj ikon fito da ita lafiya daga wannan dajin".
Jin su Aliyu na kiran sunayensu daga waje ya sanya su suka fita daga ɗakin tare da nufar inda suke.
Da sauri suka karasa inda suke. Kallonsu Umar ya yi ya ce. "Maza ku ɗauko hujjojin yanzu zamu wuce Jigawa za'a dawo da case ɗin sannan ayi wa gov. Musa hukunci".
Kallonsa Aliyu ya yi ya ce. "Amma ai naga wannan mutumin da ka ke magana a kansa mahaifinka na, shin ba za ka ji babu dad'i ba idan aka ce maka kotu ta yi yanke masa hukuncin zaman kurkuku?".
Kallonsa Umar ya yi ido na ganin ido sannan ya ce. "Ko hukuncin rataya haka yanke masa bani da matsala da hakan".
Ya karashe maganar tare da fice wa daga cikin fadan.
Da sauri su Amrah da Aliyu suka bi bayanshi.
Junaid da ke kallon duk abinda ke faruwa ne ya yi saurin bin bayansu yayin da ya dakatar da su da faɗin. "Ku tsaya mana, ku bari mai martaba ya fito da Mami, kada ku tafi hannu a bushe babu komai".
Murmushi Umar ya yi masa sannan ya ce. "Kada ka samu damuwa bro mu wanda ku kayi mana ma ya ishe mu, kace da Mami ta yi haƙuri bamu sanar mata da zamu tafi ba, domin idan muka faɗa mata ba za ta bari mu tafi ba sai ta jiƙa mana hannu da abubuwan ci, yanzu dai ka faɗa mata cewa mun tafi".
Girgiza kai kawai Junaid ya yi.
Suna gama magana gaba ɗaya suka shiga mota tare da barin masarauta baki ɗaya.
Ganin cewa babu fetur cikin motarsu ya sanya Umar nufa gidan mai domin ya sha mai a motarsu.
********
Sooraj na isa dajin, ko ƙwaƙwarar parking bai yi ba ya fito daga cikin motan. Yayin da ya fara neman inda rijiyar take. Daga nesa ya hango rijiyar. Da sauri ya fara tafiya har yana tuntuɓe. A haka ya isa wajan daga bisani ya tsaya da tafiya.
Kallon rijiyar ya yi ba tare da ba ta lokaci ba ya faɗa cikin rijiyar. Saida ya ɗau wajan mintuna ashirin bai sauka ƙasa ba. Kafin daga bisani ya faɗi a ƙasa kan ciyawa. Jiri ne ya ɗebe shi ya faɗi a wajan sumamme.
Ɓangaren Zahra kuwa, a cikin kejin ƙarfe halittun wajan suka saka ta yayin da suka zagaye ta da sarƙoƙi.
A galaibaice take kallon munanan halittun da ke gabanta wanda babu abinda suke faman yi sai zagaye ta suna ihuu suna kururuwa. Kallonsu ta yi ta ce. "Wai me ku ke da buƙata a gare ni, ku sake ni nayi tafiya ta". Ta faɗa murya a galabaice.
Dariya halittun suka babbake da shi yayin da suka ce. "Tunda ki ka shigo kin shigo kenen, dama kafin ku shigo littafin hannun ku ya gaya muku cewa dole a cikin ku mutum ɗaya za ta mutu, to kece wannan mutum ɗayar".
Take gaban Zahra ya yanke ya faɗi, nan take ta saki wani marayan kuka.
"Dan Allah ku barni naje naga mahaifiyata
KADA KU MANTA DA LIKE, COMMENTS, AND SHARE FISABILILLAH 🙏🙏🙏🙏🙏🙏🙏
ALƘALAMIN ✍️
A'ISHA M.B💞💞💞
ZINARIYAR JAJIRTATTU
بسم الله الرحمن الرحيم
*BISSMILLAHI RAHAMANI RAHIM*
Da sunan Allah mai rahama mai jinƙai!
*🔥KUNDIN CINIKAYYA* *🌎
*BOOK 2*
PAGE 8️⃣2️⃣▶️8️⃣3️⃣
_________________________
Mamaki ne ya kama kowannensu a wajan. Fashe wa da kuka Zubaida ta yi tana mai faɗin. "Kenen ba za'a yi aure na ba da Yarima Sooraj?, ya fifita wata ƴar aiki sama da ni".
Kallonta sarki ya yi ya ce. "Ki kwantar da hankalin ki, auren ki da Sooraj babu fashi wannan alƙawari na ne, yana dawo wa za'a ɗaura miki aure da shi".
Kallonsa Gimbiya Saratu ta yi ta ce. "Ai tunda lokaci ya kusa me zai ana a ɗaura masa auren naga dai ana yin hakan, a ɗaura mai aure a masallaci yana dawo wa kawai saidai ya wuce gidan matarsa.
"Wannan ba shawara ba ce mai kyau gwara a ce yana wajan kuma ya bada sadaki da kansa ba tare da wani ya yi masa hakan ba". Cewar sarki.
Nan sarki ya bawa duk wanɗan da suka hallaci masarauta domin auren Sooraj haƙuri. Yayin da gaba ɗaya suka wuce masallaci kawai don sallah juma'a.
Da sauri Mami ta nufi inda su Amrah suke murmushi kan fuskarta. Ƙarasawa ta yi wajan su ta ce. "Yara na ku shigo ciki nan gidan sarki ne ku ɗauka tamkar kuna gidan ku kunji. Ki shigo".
Murmushi Safira ta yi ta ce. "Mun gode da kulawa, amma a halin yanzu bamu ga ta zama ba. Munje waccan dajin ne domin nema wa mahaifiyar mu ƴanci yanzu tunda mun samu abin da ya kai mu shi ke nen tafiya zamu yi".
Girgiza kai Mami ta yi ta ce. "Tafiya kuma, daga zuwanku fa ko hutawa baku yi ba. To tun da sun tafi masallaci ki ku shigo kuyi sallah sai kuyi wanka ko, kafin nan kunci abinci".
Girgiza kai suka yi ba tare da sun musa da abinda ta ce ba suka bita izuwa ciki.
Kai tsaye ɗakin da aka bawa Zahra suka nufa yayin da take nan da chan da su.
Murmushi ta yi ta ce. "Karfa ku ƙullace ni na wahalar da ku da nake, ina yin hakan ne saboda ina farin cikin ganin ƴan uwan Zahra. Kunga wannan ɗakin shi ne ɗakin da Zahra ta zauna a ciki. Tunda ta shigo masarautar nan rayuwata ta sauya daga ƙunci zuwa farin ciki. Gaba ɗaya saida ta saita wa kowa zama a gidan nan, shi ya sa nake alfahari da ita".
Murmushi kawai suka sakar mata. Nan Safira ta miƙe tare da kama hannun Amrah suka je suka yi alwala duk da cewar Amrah bawani sanin addini ta yi ba hakan ya sa duk abin da ta ga Safira ta yi ita ma saita yi. A haka har suka yi sallah.
Suna zaune a ɗaƙi masu aiki suka kawo musu abinci. Nan suka zaune suka fara ci domin dama yunwa suke ji.
B
Ita kuwa Mami bar musu ɗakin ta yi ta nufi hanyar part ɗin ta.
*****
Kuka kawai Zubaida ke faman yi ganin yadda ta ga soyayyar Zahra ƙarara cikin idanuwan Sooraj.
A daidai lokacin ne su kuma Gimbiya Saratu suka shigo ɗakin nata, nan suka sa ƴan aikin su fita daga cikin ɗakin. Ba tare da ɓata lokacin ba suka fice daga ɗakin.
Kallon Zubaida suka yi wacce ta yi shaɓe-shaɓe da hawaye. Ba tare da ɓata lokaci ba suka bushe da dariya.
Cikin dariya Gimbiya Talatu ta ce. "Wai ke ƴar soyayya ko?, maganinki kenen ai, gashi nan wata ƴar aiki ta zo ta kama zuciyar Sooraj ke kina nan zaune tamkar wata bahamagiya. Dama an ce wanda yaƙi ji ba zaiƙi gani ba".
"Rabu da ita Talatu, dama ai na gaya miki duk wanda ya ci tuwo da mu miya yasha, ba da kina wani jijida kanki ba kina wani cewa babu mai raba ki da Sooraj, gashi a gaban kowa ya ce Zahra ita rayuwar sa ce. Hmm Allah sarki amma fa naju miki ba dad'i". Cewar Gimbiya Saratu wanda ta ƙara kwashe wa da dariya a karo mara adadi.
Share hawayenta Zubaida ta yi ta ce. "Dan Allah kuyi haƙuri tabbas na gane kuskure na, yanzu ina son nima na zama ɗaya daga cikin ku, dan Allah ku taimaka min please".
Kallon juna Saratu da Talatu suka yi sannan Talatu ta ce. "shi ke nen zamu taimaka miki, amma kiyi alƙawarin cewa ba za ki juya mana baya ba kuma ba za ki ci amanar mu ba".
Girgiza kai Zubaida ta yi ta ce. "Nayi alƙawarin cewa ba zan juya muku baya ba, na rantse".
Murmushi Saratu ta yi ta ce. "Good girl, yanzu abin da za mu yi shi ne ki tawo mu je ɗakin A'isha".
Tana idda maganarta suka nufi hanyar ɗaƙin Mami.
Banka ƙofar da ƙarfi Zubaida ta yi wanda ya sanya Mami razana.
Da sauri Mami wacce ke kwance kan gado ta miƙe tana mai binsu da idanuwa. "Lafiya?, me ya faru naga kunzo a wannan lokacin?".
Tsaki Zubaida ta buga sannan ta ce. "Munafuka algunguma, ni dama na san ba san aure na ki ke yi da Sooraj ba shi ya sa lokacin da ya tafi baki dakatar da shi ba matsayin ki na uwarsa".
Sakin baki Mami ta yi yayin da ta ji maganganunta tamkar saukar aradu. Nuna kanta Mami ta yi yayin da ta ce. "Zubaida ni ki ka buɗe baki ki ka cewa munafuka algunguma?, kina cikin hayyacin ki kuwa?".
Amsa Zubaida ta ba ta da cewar. "Ƙwarai ina cikin hayyaci na ba giya nasha ba balle ki ce na bugu, wallahi idan baki bari aurena da Sooraj ya faru ba sai na nuna miki cewa tabbas ni ƴar ƙwalta ce, kuma ki sani muddin Sooraj ya dawo da wannan tsinanniyar yarinyar nan gidan baki ce ta bar masarautar nan ba, saina nuna miki cewa ruwa ba sa'ar kwando ba ne".
Sakin baki Mami kawai ta yi tana kallon Zubaida da su Saratu. Ji take tamkar a mafarki, wai Zubaida da ce ke kallon tsabar idanuwanta take gaya mata maganganu masu ɗaci.
Jikin kowannensu ne ya yi sanyi ganin a karo na farko Mami ta tsawatar musu. Simi-simi suka fita ba tare da wanin su ya ce ƙala ba.
Zama Mami ta yi a bakin kujera tana mai maida numfashi. Hawaye ne ya sauka kan fuskarta.
Duk abinda ya faru su Amrah naji yayin da Safira ta kalli Amrah ta ce. "Lallai Mami tana fuskantar kalubale, hanya ba za mu taimaka mata ba?".
Murmushi Amrah ta yi ta ce. "Hmm wai shin kin manta akwai Zahra, indai har Zahra na raye ba ta mutu ba, to tabbas ita ɗaya ta ishe su, bama sai mun taimaka mata ba, Zahra ai ita ce daidai da su".
Murmushi Safira ta yi ta ce. "Haka ne, nidai fata na shi ne Allah ya sa Zahra tana cikin ƙoshin lafiya, sannan Allah ya bawa yarima Sooraj ikon fito da ita lafiya daga wannan dajin".
Jin su Aliyu na kiran sunayensu daga waje ya sanya su suka fita daga ɗakin tare da nufar inda suke.
Da sauri suka karasa inda suke. Kallonsu Umar ya yi ya ce. "Maza ku ɗauko hujjojin yanzu zamu wuce Jigawa za'a dawo da case ɗin sannan ayi wa gov. Musa hukunci".
Kallonsa Aliyu ya yi ya ce. "Amma ai naga wannan mutumin da ka ke magana a kansa mahaifinka na, shin ba za ka ji babu dad'i ba idan aka ce maka kotu ta yi yanke masa hukuncin zaman kurkuku?".
Kallonsa Umar ya yi ido na ganin ido sannan ya ce. "Ko hukuncin rataya haka yanke masa bani da matsala da hakan".
Ya karashe maganar tare da fice wa daga cikin fadan.
Da sauri su Amrah da Aliyu suka bi bayanshi.
Junaid da ke kallon duk abinda ke faruwa ne ya yi saurin bin bayansu yayin da ya dakatar da su da faɗin. "Ku tsaya mana, ku bari mai martaba ya fito da Mami, kada ku tafi hannu a bushe babu komai".
Murmushi Umar ya yi masa sannan ya ce. "Kada ka samu damuwa bro mu wanda ku kayi mana ma ya ishe mu, kace da Mami ta yi haƙuri bamu sanar mata da zamu tafi ba, domin idan muka faɗa mata ba za ta bari mu tafi ba sai ta jiƙa mana hannu da abubuwan ci, yanzu dai ka faɗa mata cewa mun tafi".
Girgiza kai kawai Junaid ya yi.
Suna gama magana gaba ɗaya suka shiga mota tare da barin masarauta baki ɗaya.
Ganin cewa babu fetur cikin motarsu ya sanya Umar nufa gidan mai domin ya sha mai a motarsu.
********
Sooraj na isa dajin, ko ƙwaƙwarar parking bai yi ba ya fito daga cikin motan. Yayin da ya fara neman inda rijiyar take. Daga nesa ya hango rijiyar. Da sauri ya fara tafiya har yana tuntuɓe. A haka ya isa wajan daga bisani ya tsaya da tafiya.
Kallon rijiyar ya yi ba tare da ba ta lokaci ba ya faɗa cikin rijiyar. Saida ya ɗau wajan mintuna ashirin bai sauka ƙasa ba. Kafin daga bisani ya faɗi a ƙasa kan ciyawa. Jiri ne ya ɗebe shi ya faɗi a wajan sumamme.
Ɓangaren Zahra kuwa, a cikin kejin ƙarfe halittun wajan suka saka ta yayin da suka zagaye ta da sarƙoƙi.
A galaibaice take kallon munanan halittun da ke gabanta wanda babu abinda suke faman yi sai zagaye ta suna ihuu suna kururuwa. Kallonsu ta yi ta ce. "Wai me ku ke da buƙata a gare ni, ku sake ni nayi tafiya ta". Ta faɗa murya a galabaice.
Dariya halittun suka babbake da shi yayin da suka ce. "Tunda ki ka shigo kin shigo kenen, dama kafin ku shigo littafin hannun ku ya gaya muku cewa dole a cikin ku mutum ɗaya za ta mutu, to kece wannan mutum ɗayar".
Take gaban Zahra ya yanke ya faɗi, nan take ta saki wani marayan kuka.
"Dan Allah ku barni naje naga mahaifiyata
KADA KU MANTA DA LIKE, COMMENTS, AND SHARE FISABILILLAH 🙏🙏🙏🙏🙏🙏🙏
ALƘALAMIN ✍️
A'ISHA M.B💞💞💞
ZINARIYAR JAJIRTATTU
بسم الله الرحمن الرحيم
*BISSMILLAHI RAHAMANI RAHIM*
Da sunan Allah mai rahama mai jinƙai!
*🔥KUNDIN CINIKAYYA* *🌎
*BOOK 2*
PAGE 8️⃣2️⃣▶️8️⃣3️⃣
_________________________
Mamaki ne ya kama kowannensu a wajan. Fashe wa da kuka Zubaida ta yi tana mai faɗin. "Kenen ba za'a yi aure na ba da Yarima Sooraj?, ya fifita wata ƴar aiki sama da ni".
Kallonta sarki ya yi ya ce. "Ki kwantar da hankalin ki, auren ki da Sooraj babu fashi wannan alƙawari na ne, yana dawo wa za'a ɗaura miki aure da shi".
Kallonsa Gimbiya Saratu ta yi ta ce. "Ai tunda lokaci ya kusa me zai ana a ɗaura masa auren naga dai ana yin hakan, a ɗaura mai aure a masallaci yana dawo wa kawai saidai ya wuce gidan matarsa.
"Wannan ba shawara ba ce mai kyau gwara a ce yana wajan kuma ya bada sadaki da kansa ba tare da wani ya yi masa hakan ba". Cewar sarki.
Nan sarki ya bawa duk wanɗan da suka hallaci masarauta domin auren Sooraj haƙuri. Yayin da gaba ɗaya suka wuce masallaci kawai don sallah juma'a.
Da sauri Mami ta nufi inda su Amrah suke murmushi kan fuskarta. Ƙarasawa ta yi wajan su ta ce. "Yara na ku shigo ciki nan gidan sarki ne ku ɗauka tamkar kuna gidan ku kunji. Ki shigo".
Murmushi Safira ta yi ta ce. "Mun gode da kulawa, amma a halin yanzu bamu ga ta zama ba. Munje waccan dajin ne domin nema wa mahaifiyar mu ƴanci yanzu tunda mun samu abin da ya kai mu shi ke nen tafiya zamu yi".
Girgiza kai Mami ta yi ta ce. "Tafiya kuma, daga zuwanku fa ko hutawa baku yi ba. To tun da sun tafi masallaci ki ku shigo kuyi sallah sai kuyi wanka ko, kafin nan kunci abinci".
Girgiza kai suka yi ba tare da sun musa da abinda ta ce ba suka bita izuwa ciki.
Kai tsaye ɗakin da aka bawa Zahra suka nufa yayin da take nan da chan da su.
Murmushi ta yi ta ce. "Karfa ku ƙullace ni na wahalar da ku da nake, ina yin hakan ne saboda ina farin cikin ganin ƴan uwan Zahra. Kunga wannan ɗakin shi ne ɗakin da Zahra ta zauna a ciki. Tunda ta shigo masarautar nan rayuwata ta sauya daga ƙunci zuwa farin ciki. Gaba ɗaya saida ta saita wa kowa zama a gidan nan, shi ya sa nake alfahari da ita".
Murmushi kawai suka sakar mata. Nan Safira ta miƙe tare da kama hannun Amrah suka je suka yi alwala duk da cewar Amrah bawani sanin addini ta yi ba hakan ya sa duk abin da ta ga Safira ta yi ita ma saita yi. A haka har suka yi sallah.
Suna zaune a ɗaƙi masu aiki suka kawo musu abinci. Nan suka zaune suka fara ci domin dama yunwa suke ji.
B
Ita kuwa Mami bar musu ɗakin ta yi ta nufi hanyar part ɗin ta.
*****
Kuka kawai Zubaida ke faman yi ganin yadda ta ga soyayyar Zahra ƙarara cikin idanuwan Sooraj.
A daidai lokacin ne su kuma Gimbiya Saratu suka shigo ɗakin nata, nan suka sa ƴan aikin su fita daga cikin ɗakin. Ba tare da ɓata lokacin ba suka fice daga ɗakin.
Kallon Zubaida suka yi wacce ta yi shaɓe-shaɓe da hawaye. Ba tare da ɓata lokaci ba suka bushe da dariya.
Cikin dariya Gimbiya Talatu ta ce. "Wai ke ƴar soyayya ko?, maganinki kenen ai, gashi nan wata ƴar aiki ta zo ta kama zuciyar Sooraj ke kina nan zaune tamkar wata bahamagiya. Dama an ce wanda yaƙi ji ba zaiƙi gani ba".
"Rabu da ita Talatu, dama ai na gaya miki duk wanda ya ci tuwo da mu miya yasha, ba da kina wani jijida kanki ba kina wani cewa babu mai raba ki da Sooraj, gashi a gaban kowa ya ce Zahra ita rayuwar sa ce. Hmm Allah sarki amma fa naju miki ba dad'i". Cewar Gimbiya Saratu wanda ta ƙara kwashe wa da dariya a karo mara adadi.
Share hawayenta Zubaida ta yi ta ce. "Dan Allah kuyi haƙuri tabbas na gane kuskure na, yanzu ina son nima na zama ɗaya daga cikin ku, dan Allah ku taimaka min please".
Kallon juna Saratu da Talatu suka yi sannan Talatu ta ce. "shi ke nen zamu taimaka miki, amma kiyi alƙawarin cewa ba za ki juya mana baya ba kuma ba za ki ci amanar mu ba".
Girgiza kai Zubaida ta yi ta ce. "Nayi alƙawarin cewa ba zan juya muku baya ba, na rantse".
Murmushi Saratu ta yi ta ce. "Good girl, yanzu abin da za mu yi shi ne ki tawo mu je ɗakin A'isha".
Tana idda maganarta suka nufi hanyar ɗaƙin Mami.
Banka ƙofar da ƙarfi Zubaida ta yi wanda ya sanya Mami razana.
Da sauri Mami wacce ke kwance kan gado ta miƙe tana mai binsu da idanuwa. "Lafiya?, me ya faru naga kunzo a wannan lokacin?".
Tsaki Zubaida ta buga sannan ta ce. "Munafuka algunguma, ni dama na san ba san aure na ki ke yi da Sooraj ba shi ya sa lokacin da ya tafi baki dakatar da shi ba matsayin ki na uwarsa".
Sakin baki Mami ta yi yayin da ta ji maganganunta tamkar saukar aradu. Nuna kanta Mami ta yi yayin da ta ce. "Zubaida ni ki ka buɗe baki ki ka cewa munafuka algunguma?, kina cikin hayyacin ki kuwa?".
Amsa Zubaida ta ba ta da cewar. "Ƙwarai ina cikin hayyaci na ba giya nasha ba balle ki ce na bugu, wallahi idan baki bari aurena da Sooraj ya faru ba sai na nuna miki cewa tabbas ni ƴar ƙwalta ce, kuma ki sani muddin Sooraj ya dawo da wannan tsinanniyar yarinyar nan gidan baki ce ta bar masarautar nan ba, saina nuna miki cewa ruwa ba sa'ar kwando ba ne".
Sakin baki Mami kawai ta yi tana kallon Zubaida da su Saratu. Ji take tamkar a mafarki, wai Zubaida da ce ke kallon tsabar idanuwanta take gaya mata maganganu masu ɗaci.