← Book details Kanwar Matata Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 88 OF 112

Sashe 88

Kanwar Matata Complete Hausa Novel · about 8 min read

ta shiga nunata da ɗan yatsa tana jijjigawa alamar gargaɗi. Zubewa Sarah tayi a ƙasa tama kasa kuka sai kalle-kalle kawai take yi a ɗakin, can kuma ta girgiza kai tare da faɗin, "Tabbas wannan ba Khalil ɗina bane, Khalil ɗina bai son ganin ɓacin raina kuma bai son damuwata, dole akwai abunda Aina'u tayi masa, haka nan Khalil ba zai taɓa canza min ba. Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!!!" Haka Sarah ta dunga maimaitawa har kuka ya kufce mata. Tafi ƙarfin awa guda a wajen kamun ta tashi ta haura sama, daidai ɗakin Khalil ta jiyo saurin da ya kusa tsayar da numfashinta, "Ohh my God! Aina'u you're soooo sweet, wallahi kinfi zuma daɗi!! Na baki kaina ki cinyeni tasssss, show me Ai'n, show me that you love me, do it properly, ohhh myyyyyyy.........." Da mugun gudu Sarah ta bar wajen tare da faɗawa ɗakinta, ko kula su Sauban dake kuka bata yi ba ta shiga rera nata kukan, bata gansu ba, amma idanunta ya gama hasaso mata hotonsu gaba ɗaya a idanunta, data kulle idanu abunda take gani kenan, nan da nan jikinta ya ɗauki wani irin zafi mai tsanani tare da ciwon kai. Sauban ne ya tako ya iso wajen gadon tare da kama rigar baccinta ya shiga ja yana faɗin, "momiiii." Shima Sam'an sai ya taho shima yana kukan, da kyar ta iya kai hannun ta ɗauko su duka ta rungume a jikinta ta kuma fashewa da kuka, kamar wanda suka san kukan da take yi, suma sai suka ƙara fashewa da kukan. A haka ta shayar dasu hawayeta na ɗiga a jikinsu har suka ƙoshi sannan ta miƙe da kyar ta cire masu pampers sannan ta kaisu bayi tayi masu wanka ta shiryasu duk tana kukan sannan itama tayi wankan ta fito ko mai bata shafa ba ta zura doguwar riga tare da haɗa kayanta da na twins ɗin a cikin akwati ta goya Sam'an ta riƙe Sauban a ɗaya hannun ɗayan Kuma ta shiga jan akwatin, tana fitowa Aina'u na fitowa daga ɗakin Khalil don bayan sun gama abunda suka yi da Khalil ɗin sai ta shafa hannunta ta shiga hango Sarah daga ɗakinta tana ɓaɓɓaka dariya, don ba ƙaramin daɗin ganin halin da Sarah take ciki take yi ba. Ko kallonta Sarah bata yi ba duk da kuwa tana fitowa ta ganta, amma sai tayi kamar bata ganta ba don zuciya zai iya sakawa ta caki maƙogwaranta ta faɗi ta mutu. "Ke dawo nan!" Aina'u ta faɗi bayan ta murza tafin hannunta. Babu musu Sarah ta juyo ta dawo inda Aina'un take, "Menene a cikin akwatin nan kuma ina zaki?" Faɗin Aina'u. "Kaya twins ne da nawa, kuma gida zani." Sarah ta bata amsa cikin zuciyarta tana mamakin yanda akai take sauraran Aina'un. "To ki koma, babu inda zaki, ai baki fara ganin komai ba tukun, so nake zuciyarki ta buga ki mutu saboda baƙin ciki kamar yanda nima kika ɗanɗanamin baƙin ciki. Maza koma ɗaki yanzun nan!" Aina'u ta ƙarisa maganar da ƙarfi, "My love meke faruwa?" Faɗin Khalil daga ciki jin ihun Aina'un. "No, babu komai yi kwanciyarka." Komawa yayi ya kwanta don dama a kwancen yake, ita kuma tabi bayan Sara dake ƙoƙarin buɗe ɗakinta da harara. Tun daga wannan ranar Sarah ta koma hoto a cikin gidan ita da yaranta, don sai ta kwana bakwai bata saka Khalil a cikin idanunta ba, tayi wani irin mugun rama kamar mai ciwon ƙanjamau, ga wani irin mugun tsoron Aina'un da take yi, don har ɗaki Aina'u ke biyota tana bata command, ita ke masu girki tayi serving ɗinsu, sannan idan sun gama taje ta kwashe kayan ta kai kitchen ta wanke, da daddare kuma su dame ta da ihu ita da Khalil ɗin, kwana take yi bata bacci, amma duk da haka bata taɓa tunanin ta tashi ta raya daren ba ko da da raka'a biyu ta kai kukanta wajen Allah, babu abunda take yi sai kuka, sallolin nan biyar dai basu wuce ta, amma bata san tayi azkar ɗin safe dana maraice ba, ko kuma ta buɗe Qur'ani ta karanta ba. Sai dai ta zauna tsakiyar gado tayi ta kuka. Ɓangaren Khalil kuwa, yafi Aina'u rama, a fuskane kawai kamar yana farin ciki, amma deepdown zuciyarsa ciwo take masa, duk lokacin da zai sadu da Aina'u, koma masa take yi Sarah, sai bayan ya kammala sai ta rikiɗe ta dawo masa Aina'u, haka shima zai ta kuka har gari ya waye, yanzu sallar ma ya daina zuwa masallaci kwata-kwata, a nan ɗaki yake yi, kamun Aina'u ta soma korashi parlourn don _Hell_ yayi mata warning akan idan har yana Sallah a inda kayan tsafinta yake, komai zai lalace. Yauma Sarah na zaune akan gado tana sana'arta, sai ji tayi an bugo ƙofar da ƙarfi, da sauri ta ɗago jikinta na rawa ganin Aina'u ce, su Sauban kuwa dake wasa a ƙasa har sun yo kan Aina'u sun ƙanƙame, "Ki tattara kayanki tsaf ki koma ɗakin ƙasa da zama, ko da wasa kar in ƙara ganin ƙafarki a saman nan." Aina'u na gama faɗin haka ta fice daga ɗakin, don yau kama Khalil tayi a bakin window ɗin Sarah yana kallonsu ita da ƴaƴanta kasancewar akwai haske a barandar, ita kuma Aina'u ta tashi fitsari taga bai ɗakin shine ta fito ta gansa jikin window ɗin yana hawaye. Yana jin motsinta ya share hawaye da sauri tare da soma kame-kame. Ɗaki ta nuna masa da hannu, suf-suf-suf ya wuce ita kuma tabi window ɗin da harara tare da yin kwafa ta bishi ɗakin. Wannan dalilin ne ya saka ita kuma ta kori Sarah daga saman gaba ɗaya. Ita Sarah har cikin ranta ta san Aina'u bata bar Khalil haka ba, amma rashin dabara da hankali ya saka ta kasa kai kukanta zuwa ga Allah. Watan Sarah Shidda a cikin wannan bala'in amma ko sau ɗaya bata taɓa jaraba kai kukanta ga mahalicci ba, sai dai kuka wani lokacin kuma tace Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, tuni ta yaye su twins don daga ita har Khalil ɗin duk sun zama abun tausayi da tsoro don ba ƙaramin rama suka yi ba, shi kuwa Khalil duk ranar da yaje asibiti, don asibitin ma ba kullum take bari yake zuwa ba, sai couligue ɗinsa sun yi masa caaaa akan mai ke damunsa duk ya rame, wasu kuwa sun fara zargin halin da yake ciki na neman ƙanwar matarsa, don Aina'u kullum sai ta saka shi a gaba sun fita zuwa wajajen shaƙatawa tare, suyi hotuna wani lokacin ma a hotel suke kwana. Yau ya kasance Sunday babu inda Khalil yake zuwa, sai dai sau da yawa basa wuni a gida shi da Aina'un, don yana daga cikin ranakun fita yawonsu, zaune yake a parlour daga shi sai gajeran wando, Aina'u kuwa ta ɗaura kanta a kan cinyarsa tana danna waya, can wata ƙawarta ta turo mata da bp sai da ta gama kallo sannan ta nunawa Khalil tare da faɗin, "My love yau wannan style ɗin za muyi!" Ƙarban wayar yayi ya kalla da kyau sannan yace, "Kuma fa zai yi suger." Tashi Aina'u tayi tare da faɗin, "Bari ma ka gani dama bamu taɓa yi a parlour ba." Tana faɗin hakan ta kai hannu zata zame boxer ɗinsa, da sauri ya riƙe tare da faɗin, "Sarah might come out ita da yara, muje ciki kawai." "Ni kuma anan nake son muyi!" Tana gama faɗin hakan ta sutale masa wando tare da soma yi masa blowjob, tuni ya manta da batun su Sarah zasu iya fitowa ya hau moaning, gaba ɗaya ya fice daga hankalinsa kuma dama abunda Aina'un take so kenan, nan da nan ta cire ƴar iskar doguwar rigar dake jikinta ta yar ta hau kan Khalil ɗin daidai lokacin da twins suka fito parlourn kamar an jeho su. Da gudu Sarah ta fito daga ɗayan parlourn jin ihun su Khalil ɗin a parlour kuma taga lokacin da twins suka fita, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Sarah ta faɗi da ƙarfi tare da kai hannu ta rufe idanun twins tana wani irin kuka, don ko da suka fito suka ga abunda Khalil ɗin suke yi, cak suka tsaya sunata kallo. Shi kuwa Khalil wani irin tsalle yayi tare da ture Aina'u yana kare jikinsa yana mai jin kamar ƙasa ta tsage ya shige ganin yaransa sun ga abunda yake yi. Hannunsu Sarah ta kama tana kuka tare da shigewa ɗayan parlourn. Da sauri Khalil ya saka wandonsa ba tare da ya kalli Aina'u ya wuce sama. Aina'u kuma tsaki tayi tare da ɗaukar rigarta ta saka ta zauna tana kaɗa ƙafa. Bayan mintuna talatin Sarah ta fito ta samu Aina'u a inda take, zubewa tayi kan guiwowinta tana kuka sosai tare da faɗin, "Aina'u dan girman Allah, dan ƙaunar da Allah yakewa Manzonsa s a w, idan kina ƙaunar ki shiga aljanna kiyi haƙuri ki koma gida ki fita daga rayuwar mijina ki warware koma menene ki kai masa don na san duk abunda yake yi ba cikin hayyacinsa yake ba." faɗin Sarah don ta mance Aina'un ma da daɗe da barin musulunci. Wani irin dariya Aina'u ta fashe dashi tare da faɗin, "Wallahi babu uban da ya isa ya raba ni da Khalil, kuma da gaske mijinki ba a hayyacinsa yake ba, amma kuma har ya mutu babu wanda ya isa ya warware abunda nayi." Faɗin Aina'u tare da miƙewa ta hau sama. Sarah ta jima tana kallonta kamun ta koma ta kamo hannun twins ɗin suka fita daga ɗakin don ta gama yanke hukuncin mayar dasu side ɗin Hajiya za tayi saboda gudun gurɓacewar tarbiyansu. Tana shiga ɗakin Hajiya ta idda Laure bisa darduma ta kai kanta ƙasa sa shashsheƙar kuka take yi tana ganawa da ubangijinta. Turus ta tsaya tana auna hauka da rashin hankalin ta, "Idan dai har Laure zata yi sujjada tana kuka domin buƙatarta wajen ubangiji, to ni mai na tsaya yi kenan? Tabbas babu maganin da Ubangiji bai dashi.........."
Chapter 88 · 0% Book details