← Book details Kanwar Matata Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 51 OF 112

Sashe 51

Kanwar Matata Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai da suka je gaban Hajiya sannan suka durƙusar da Sarah. Da sauri Hajiya ta taro ta tare da faɗin, 'Ɗiyata dawo nan kusa dani ki zauna, kar ki zauna a ƙasa." Faɗin Hajiya bayan ta zaunar da Sarah kusa da ita wacce fuskarta ke lulluɓe da gyale. "To Hajiya ga ƴarki nan Sarah, don Allah a saka mata idanu, idan tayi ba dai-dai ba a kwaɓa mata. A riƙa nuna mata abunda ya kamata, sannan dan Allah a riƙa hakuri da ita yarinya ce. Ki ɗauke ta tamkar _Khalil_, yanda zaki hukuntasa idan yayi laifi, haka itama zaki hukuntata. Basu da bambamci a wajenki." Faɗin maman Muneeba. Murmushi Hajiya tayi tare da kamo kafaɗun Sarah tare da faɗin, "Sarah ɗiyata ce ba suruka ba. Ba kuda damuwa domin gida kuka kawota. Allah ubangiji ya basu zaman lafiya mai ɗorewa da zuri'a ɗayyiba." Da ameen duka ƴan ɗakin suka amsa. "Laure, fito min da akwatin nan." Hajiya ta faɗi da ƙarfi saboda Lauren ba a kusa da ita take ba. Laure ta fito tare da akwatin da hajiyan ta umurceta da ta fito dashi tana ja da kyar don danƙam yake da kaya a ciki. "Ga kyauta nan zuwa ga ɗiyata. Allah ya bada zaman lafiya mai amfani." Godiya su maman Muneeba suke tayi sannan suka ɗauki akwatin, har ƙofa Hajiya ta rako Sarah tana ta saka mata albarka. Bayan sun dawo ɗakin Sarah sai suka buɗe akwatin tare da fiddo kayan ciki. Turaruka ne irin na gida su humra masu ƙamshi da su turaren wuta na rushi na jiki, kaya, ɗaki da kuma tsuguno. Sai abayoyi da lafayas masu yawa da kuma tsana. Bayan kowa ya gama gani sai suka mayar da komai suka rufe suka ɗaura mata a saman wardrobe. A parlour kuwa, matan zumunta kowacce ta fiddo da hoda da jan baki tana ƙara gyara fuskarta saboda samun labarin za'a tafi dinner yanzu. Su maman Muneeba kuwa, faɗa suka ƙara yiwa Sarah sosai kamun suka yi mata sallama. Kuka Sarah ta fashe dashi ganin zasu tafi su barta har da Muneeba don mahaifinta yace ƙafarta ƙafar mahaifiyarta. Munee rungume Sarah tayi suna kukan tare. Dakyar mama ta raba su ganin zasu ɓata masu lokaci kuma ana jiransu a waje domin a maida su gida. Bayan sun tafi sai yarage daga ita sai matan zumunta da kuma ƴan uwanta dake ta shirye-shiryen zuwa party. Kowacce sai ƙure a daka take yi. Wata budurwa ce ta shigo hannunta riƙe da wani ƙatoton kit na makeup. "Dan Allah ina amaryar da za'a shirya? Lokaci na ƙurewa." Da hannu Na'ima tayi mata nuni da hanyar ɗakin da Sarah take ciki tare da cigaba da shafa powder ɗinta. Budurwar ta haura sama tare da shiga ɗakin da Sarah take ciki, waya ta sameta tana yi. Sai da ta gama wayar da take yi da _Khalil_ sannan ta juyo ta kalli budurwar. Murmushi budurwar tayi tare da faɗin, "Angonki ne ya turo ni inyi maki kwalliyar zuwa dinner." Murmushi Sarah ta mayar mata tare da faɗin, "Ok, amma dan Allah kiyi min haƙuri inyi sallar isha'i." Zama makeup artist ɗin tayi tare da faɗin, "Babu matsala. Yi sallar ki." Ko da Sarah ta idar da Sallah, gaba ɗaya an gama kwashe su Na'ima da ƴan matan zumunta zuwa wajen dinner. Sai da mekeup artist ɗinnan ta fiddo mata da wata lafiyayyiyar gown a cikin wani dogon kwali kalar milk ta saka sannan ta soma yi mata kwalliya. Ba ƙaramin kyau tayi ba. Rigar kamar don ita aka yi sa saboda yanda ya amshi jikinta. Ita kanta makeup artist ɗin bata taɓa yiwa amarya kwalliyar da ya ruɗa ta ba irin Sarah. Ba ƙaramin kyau tayi ba. Tuni tayi mata mahaukatan pictures ta watsa a whatsapp status, Facebook da instagram sannan ta rubuta _The beautiful bride of Ibrahim Khalilullah Nurudden Muhammad son of late ChiefJustice Nurudden Muhammad)_ a ƙasan hoton. Sai ga uban likes. Comment kuwa babu adadi, na masu addu'a da kuma masu mamakin auren don ba'a yaɗa a social media ba. Ƙarfe takwas da arba'in wata auntyn _Khalil_ ta shigo tare da kamo hannun Sarah suka fita daga dakin tare da rufowa. Har gaban lafiyayyiyar sabuwar motar _Khalil_ ta kaita tare da buɗe gidan baya ta saka ta a ciki sannan ta rufo ƙofar. Lumshe idanu tayi tare da shaƙo kamshin turaren _Imperial Majesty_. A hankali ta buɗe idanunta jin hannun _Khalil_ a cikin nata hannun. Kai hannun saitin bakinsa yayi tare da kissing sannan yace, "You look very beautiful wifey." Ɗagowa tayi suka haɗa idanun, kasa ƙifta idanun tayi saboda wani irin kyau da yayi, shi sanye yake cikin ɗanyan shadda golden colour wanda ɗinkin ya amshi kayan da kuma jikinsa. Hura mata iskar bakinsa yayi a fuska tare da ɗage gira yace, "Wannan kallo haka, cinyeni za kiyi?" Kau da kai tayi tare da faɗin, "Kayi kyau da yawa ne ai." Juyowa yayi yana facing ɗinta sosai tare da faɗin, "Juyo ki kalli mijinki da kyau, naki ne ke ɗaya. Ni wallahi duk kishi ya kama ni kamar mu juya kawai mu koma gida abun mu. Kyawun da kika yi is over love." Ya faɗi hakan yana mai jawota jikinsa gaba ɗaya. Da sauri ta tashi a kan jikin nasa tana mai nuna masa driver da idanunta. Ɗage gira yayi tare da faɗin, "Kar ki damu makaho ne baya ganin mutanen dake cikin motarsa musamman da daddare. Bar ni naji ɗumin matata." Ya faɗi yana mai ƙara jawota jikinsa. "Ni dai kwalliyata wallahi!" Ta faɗi cike da shagwaɓa. "Ai ni akai wa. Barni na more abuna." Ya faɗi hakan ba tare da ya sake ta ba har suka cikin wajen da ake taron. Sai da aka shiga aka sanar da zuwansu sannan su Na'ima suka fito tare da abokan _Khalil_ ɗin waɗanda za suyi masu jagora zuwa ciki. Su Na'ima sune a gaba sai ango da amarya a tsakiya, abokan ango kuma a baya. Sai da suka zo kofar shiga hall ɗin sai suka tsaya, MC kuma ya saki wakar _Laye_ ta kiss Daniel. Gaba ɗaya hall ɗin ya kaure da tafi saboda shigowar ango da amarya. Sai da suka ɗan taka kamun suka isa wajen da aka tanada domin su suka zauna. Mc ya kira sunan Hajiya umaima k'anwar mahaifin _Khalil_ tazo ta buɗe taro da addu'a tare da yiwa ango da amarya fatan alkhairi. Tun tana yi aunty Rose Merry taje ta yiwa Mc raɗa a kunne. Aunty Umaima na komawa wajen zamanta Mc ya kira aunty Rose Merry daga da dangin amarya domin itama tayi jawabi tare da sakawa ango da amarya albarka. Da taku ɗai-ɗai aunty Rose Merry ta fito tare da karɓan mic ɗin tace, "Da farko dai ina godiya ga Yesu Almasihu da ya nuna mana wannan rana na auren ƴata Sera (Sarah). Praise the Lord!" Ta faɗi da ƙarfi yayin da matan zumunta suka haɗa baki da ƙarfi suka bata amsa da "Hallelujah!" Gaba ɗaya hall ɗin ya ɗau wani irin shuru kowa da abunda yake faɗi a zuciya. Aunty Rose Merry ta cigaba da faɗin, "Na dawo gareka ɗana. Wannan yarinya dake kusa da kai, ka riƙe ta gaskiya bisa amana. Idan kayi haka, Allah zai yi maka albarka. Praise the Lord!" Ta ƙarisa maganar da ƙarfi ƴan matan zumunta suka amsa mata da "Hallelujah!" Ta cigaba, "Ka bata duk hakkinta da yake kanka. Kar ka barta da yunwan ciki. Sannan kar ka riƙa yin nisa da ita, ka kasance kullum a tare da ita kusa-kusa sosai. Kar ka barta da yunwarka, ka bata kanka da lokacin ka duk lokacin da ta buƙata. Kar ka bari ta kalli waninka da sha'awa, ka kasance jarumi sosai." Tana kawowa nan gaba ɗaya hall ɗin aka fashe da dariya don kowa ya fahimci mai take nufi. Ita kuwa sai cigaba da magana tayi ko a jikinta, "Ke kuma amarya na dawo kanki, kar ki kuskura ki bari mijinki yaji sha'awar wata mace, ki bashi hakkinsa gaba ɗaya, kiyi masa girki mai daɗi, ki bashi a baki, idan yazo saduwa dake kar kiyi masa yanga. Duk position da ya saki, ki tsaya cak, idan kuma kince za kiyi yanga, kina kallo karuwai za su tafi da kurwar mijinki. A toh!" Nan ma Wani dariyar aka kuma fashewa dashi, Sarah kuwa kunya kamar zata kashe ta. _Khalil_ kuwa murmushi kawai yayi tare da girgiza kai. Aunty Rose Merry kai mic dai-dai bakinta tayi kamar zata cinye tare da soma waƙa, " _Ango idan kayi da kyau, akwai sakamo, kar kayi mugunta zaka girbe watarana!" Ƴan matan zumunta an kunnosu, gaba ɗaya suka fito suka hau amshi da, " _Amarya idan kinyi da kyau akwai sakamakon, kar kiyi mugunta zaki girbe watarana_" Mc yace, "Mun gode, mun gode, mun gode. Dan Allah jama'a a tafa masu" Gaba ɗaya wajen ya kaure da tafi shi kuma ya karɓi Mic ɗin hannun aunty Rose Merry suka koma mazauninsu. Daga nan aka shiga shagulgulan biki. Mc ya kira ango da amarya domin su ɗan taka tare da nishaɗantar da mutane. Hannun Sarah cikin na _Khalil_ suka taso daga wajen zaman su tare da tsayuwa a filin. A kunna _Khalil_ yayiwa Mc magana, shi kuma MC yace, "To jama'a, magana ake yi na ango da amarya. Ango yace a saka masa wak'ar soyayya mai daɗi don tare zasu waƙe kansu shi da amaryarsa. Dj idan ka shirya." Ya faɗi hakan tare da miƙawa Sarah mic kasancewar ya riga ya bawa _Khalil_ nashi. Ɗagewa Sarah gira _Khalil_ yayi tare da faɗin, "Wannan gasa ce tsakanina dake. Kuma ni zan ci" Itama ɗage masa girar tayi tare da faɗin, "Da gaske kai zaka ci?" Gaba ɗaya a idanun mutane suka yi komai, sai hall ɗin ya kaure da tafi har da masu fito da cike da wani irin salo mai tafe da ƙauna sukai maganar. Dai-dai nan DJ ya saki waƙar auta MGboy ina ji dake. *_Ina ji da ke ni ba zan barki ba, ni kullum a fatana mu kai har ga ran aure* *_Ina ji da kai nima bazan barka ba, kullum tunanina yaushe ne za muyo aure_* *_Idan lokaci yayi ni naki ne, idan lokaci yayi ni mijin ki ne. Idan lokaci yayiiiii! Idan rabbi yaso na aureki ƴan mata_* *_Ba
Chapter 51 · 0% Book details