Sashe 14
Kanwar Matata Complete Hausa Novel · about 8 min read
*_DAN DARAJAR GIRMAN UBANGIJI KAR KI FITAR MIN DA BOOK. WALLAHI TYPING AKWAI MATUK'AR WAHALA DA CIN RAI. KI TAIMAKA MIN Y'AR UWA!_*
*_DUK MAI SONA TA HANYAR SAYAN BOOK D'INA KAWAI ZAI GWADA MIN, TURA D'ARIN KI BIYAR KI SHA KARATU CIKIN SALAMA BISA WANGA ACCOUNT 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK SAI KI TURA DA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA 08128755583_*
*_MATAR SAYYADEE_*
[9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜
*PAGE 8*
Kuka take yi sosai har da shashshek'a tana jin ina ma bata zo duniyar ba balle wannan abun ya same ta. Taso ta kasance ta daban a cikin y'an uwanta, sai gashi ita ma an rubuto a cikin k'addararta akwai samun ciki ba tare da aure ba. Sosai ta tsani rayuwar da y'an uwanta suke yi wanda mahaifiyarsu ita ce ta d'aura su a kan wannan turba saboda son abun duniya. Da ana canza mahaifiya da tabbas ta jima da canza nata mahaifiyar. Mahaifinta ne ya fad'o mata a rai, ta san tabbas shi zai fahimceta, to amma wanda zata aura fa? Tuno hakan ya saka ta kuma rushewa da kuka. "Shikenan ni ba'a rubutomin aure a nawa littafin ba. Na shiga uku! Ni wallahi da nayi ta zama a cikin gidan mu ina kwasar bak'in ciki, gwara na tafi *_Wamba_* wajen dangin mahaifina nayi zama na a can. Ban damu da ko k'auye bane ko birni! Buri na in ganni a d'akin mijina ina bautar ubangiji!" Sarah ta fad'i a bayyane tare da mik'ewa ta soma tafiya a k'afa kasancewar layuka shidda ne ya rabasu da inda take. Kan titi _Kasuwar gwari_ ta mik'e tayi ta tafiya har ta iso _Jos road_ sannan tayi k'asa kasancewar can k'asan Jos road d'in suke. Ga zafin rana, ga kuma zazzab'in dake damunta da matsanaici ciwon kai wanda ya ninku sakamakon kukan da tasha. Tana isa k'ofar gidansu gabanta ya yanke ya fad'i ganin motar y'an sanda da kuma y'an sandar a kwar gidansu ga kuma uban cincirundon samari da y'an mata har da wasu matan auren layin da suka fito suna baiwa idanunsu abincin. Tana isowa gaba d'aya idanun jama'a ya dawo kanta. "Yauwa, ga d'aya karuwar ta dawo. Da gani ba gida ta kwana ba. Ai mu dai Allah bai had'a mu da makwaftar kirki ba. Ni dama tashin su za ayi daga unguwar nan don muna da y'ay'a mata dake tasowa kada suga abunda suke yi suma su soma jin sha'awar yi." Fad'in wata mata tana hararar Sarah. Sarah kuwa kutsawa tayi cikin mutanan nan ta shige cikin gidan. Turus ta tsaya ganin Baba a tsakar gida dafe da goshi gaban rigarsa duk jini yana kuka, gefe kuma su aunties d'in Farouq ne da k'annansa maza da mata a gefe sai girgiza suke yi suna fad'in wallahi baza su yarda ba. Nuratu, Aina'u, Na'ima, da Hassana kuma a waje d'aya suna fad'in babu inda zasu je kuma babu uban da ya isa fitar dasu zuwa police station. Lami kuwa sai fad'i take, "Ko kotu za'a je, aje ban jin tsoron uban kowa, sune suka biyo mu har gida da fitina, mu kuma muka kare kanmu." Baba dake kuka ya kalli officer d'in da yake magana cikin lalama akan su Lami su biyosa zuwa station yace, "Bawan Allah d'an sanda, ni na baka umarnin ka tafi dasu da tsiya, idan sunk'i kuyi amfani da k'arfin ku na hukuma ku fitar dasu, amma kuma banda wancen da ta shigo yanzu, don babu hannunta a kan duk abunda ya faru." Ya k'arisa maganar yana nuna Sarah. Police d'in kuwa, bai saurari maganar Baba, sai bada baki yake yi, don babu yanda za ayi ya nuna power ya fitar dasu Nuratu zuwa police station domin Hassana budurwarsa ce, Marfu'a kuma yanzu haka ma tana d'akinsa a wajensa ta kwana jiya. Hassanar ya kira gefe, da kyar taje tana wani cin magani. Sun jima suna magana, a yanda yake lallaminta, zaka d'auka uwarsa ce ita. "To naji, amma wallahi baza mu wuce mintuna ashirin ba a can." Da sauri yace "Na maki alk'awarin haka." Sai da taja tsaki sannan ta koma tayiwa y'an uwanta magana sannan suka fita su duka banda Sarah da ta jingina da bango abun duniya duk ta ishe ta. Ta gaji da matsalar mahaifiyarta da y'an uwanta. K'arisawa tayi wajen Baba duk da jirin da take ji domin taimaka masa ya tashi. Rik'e mata hannu yayi tare da fad'in, "Bari zan iya tashi Saratu. Kema naji jikin naki da zafi sosai. Ya aka yi Aina'u ta rigaki dawowa daga asibitin, ko fad'a kuka yi?" Sai da ta taimaka masa ya mik'e tukun sannan tace, "A'a ba fad'a muka yi ba, nice na baro ta a can asibitin." Baba bai k'ara cewa komai ba sai nufa wajen pamfo da yayi ya wanke goshinsa sannan ya nufi kan baranda ya zauna a kan tabarma tare da fad'in, "Saratu, kiyi hak'uri duk laifi nane da na kasa zab'a maku uwa ta gari. Y'an uwana sun nuna basu son na auri Elizabeth (Lami) amma na nace ni ita nake so sabida yanda ta nuna min k'auna a wancen lokacin. Ban tab'a d'auka Elizabeth za tayi min butulci a rayuwata ba." Kallonsa Sarah tayi tare da fad'in, "Baba ka bani labari, ta yaya ka had'u da Lami har kuka yi aure, kuma mai yasa danginka suke fushi da kai har yanzu? Bamu san kowa naka ba, haka suma basu san mu ba. Dangin Lami ma babu wanda ya san mu, muna bamu san kowa ba sai aunty Rose Merry wanda Lami tace mana y'ar uwarta ce." Sunkuyar da kai Baba yayi tare da fad'in, "Rose Merry ba y'ar uwar mahaifiyarku bace, asali ma itace mai d'aura mahaifiyarku akan turba mara kyau. Taso mahaifiyarku ta koma addininta da ta baro, amma kuma sai mahaifiyarku ta nuna ita tana son addinin musuluncin da ta karb'a." Sarah tace, "To amma Baba Lami bata sallah, bata azumi, duk wani abu na musulunci Lami bata yi. Kuma a hakan ne take cewa tana son musuluncin?" Ajiyar zuciya Baba yayi tare da fad'in, "Nima na jima ina wannan zargin Saratu. Anya kuwa mahaifiyarku bata koma addinin kiristancinta ba kuwa? Domin duk ranar lahadi da sassafe take barin gidan nan, kuma bata dawowa Sia wajajen d'aya ko biyu." Shuru Sarah tayi tana tuno wata rana da mahaifiyar tasu ta dawo daga inda take zuwa duk ranar lahadi, sai ta ganta d'aure da wani zani mai hoton k'atoton cross a jiki, zanin biyu ne, da ta d'aura d'aya a k'ugu, sai ta d'aura wani a sama kasancewar dama farar rigar less ce a jikinta. Ga wani k'aramin Bible a kan gado. "Lami! Wannan wani irin kaya ne haka a jikinki irin na y'an coci?" Saurin kallon jikinta Lami tayi tare da fad'in, "Kai, kin ganni nan d'azu da na fita, shine wata mota tayo kaina, garin na kauce mata sai na fad'a cikin kwata, kuma dama kusa nake da gidan auntynku Rose Merry, shine ta bani wad'annan kayan na saka. Yanzu ma Allah-Allah nake in cire su." Sarah ta kalli Bible d'in tare da fad'in, "Wannan kuma fa Lami!" A harzuk'e tace, "Ke dan ubanki uwata ce ke? Kin cika ni da tsinannun tambayarki. To Rose Merry d'in ce ta bani na ajiye mata a nan anjima idan zata wuce gida zata biyo tanan ta karb'a." Kallonta Baba yayi tare da fad'in, "Lafiya Saratu kike dogon tunani haka?" Sauke ajiyar zuciya Sarah tayi tare da fad'in, "Baba ina tuna wani abu ne. Ina ji a jikina Lami ta koma addinin kiristanci." Daga nan ta kwashe duk labarin abunda ya faru wancen ranar ta fad'a masa. Da mugun mamaki Baba ke kallon Sarah, sai kuma ya girgiza kai tare da fad'in, "Babu abunda Lami ba zata iya aikatawa ba. Lami ta daina bani mamaki sai dai tsoro. "Baba mai ya same ka a goshin ka?" Fad'in Sarah ganin har goshin ya tasa. Sai da ya shafa wajen sannan yace, "Lami ce taje jifan y'an uwan saurayinki da suka yi cincirundo domin d'aukar fansar abunda suka yi shine ta same ni a goshi, kuma kin san budar ba ta roba bace. Don ma Allah ya tsare." Cike da tausayi Sarah yace, "Allah ya k'ara tsareka Baba." Da ameen ya amsa tare da kallonta yace, "To Sarah ya ake ciki? Mai likitocin suka ce wannan karon?" Fad'in Baba yana kallon Sarah data sunkuyar da kai tana hawaye. "Baba akwai cikin?" Sai da gaban Baba ya fad'i da jin haka, amma ya d'aure tare da fad'in, "Kuma Saratu har yanzu baki gano bakin zaren ba?" Shuru Sarah tayi don bata san ta inda zata fara yiwa Baba bayani ba. Hawaye ne kawai ke zubowa daga idanunta yana d'iga a kan tabarmar da suke kai. "Saratu ni mahaifinki ne. Kuma kin san duk fad'in gidan nan babu wanda na shak'u kuma nake jinsa har cikin raina cikin y'ay'ana idan ba ke ba. Kar ki damu, zan fahimceki. Zan kuma yi maki nasiha matsayina na mahaifinki kuma in karb'i k'addararki da hannu bibbiyu. Sai dai ba zan tab'a jin dad'i ba idan har ke da kanki kika kai kanki wajen wani namijin bayan kin yi mi alk'awarin baza ki tab'a yin irin rayuwar da y'an uwanki suke yi ba." Kuka Sarah ta fashe dashi tare da fad'in, "Na rantse da girman ubangijin halittu ban tab'a kaiwa wani namijin jikina ba domin yayi amfani dani. Wallahi, tallahi duk abunda ya faru tsausayi ne Baba. Ban san ta yanda zanyi maka bayani ba Baba. Amma wallahi ban tab'a karya maka alk'awarin da ba d'auka ba." Ko kamun Baba yayi wata maganar wani yaro ya kwad'o sallama tare da fad'in, "Wai ana sallama da Sarah a waje. Wai dan girman Allah ta fito mintuna biyar kawai!"
*_Kuyi hak'uri da wannan, anticipate a long page tomorrow _*
*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*
*_ZULFA'U SA'EED IBRAHIM AKA 👉MATAR SAYYADEE_*
[9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜
*PAGE 9*
*_DUK MAI SONA TA HANYAR SAYAN BOOK D'INA KAWAI ZAI GWADA MIN, TURA D'ARIN KI BIYAR KI SHA KARATU CIKIN SALAMA BISA WANGA ACCOUNT 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK SAI KI TURA DA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA 08128755583_*
*_MATAR SAYYADEE_*
[9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜
*PAGE 8*
Kuka take yi sosai har da shashshek'a tana jin ina ma bata zo duniyar ba balle wannan abun ya same ta. Taso ta kasance ta daban a cikin y'an uwanta, sai gashi ita ma an rubuto a cikin k'addararta akwai samun ciki ba tare da aure ba. Sosai ta tsani rayuwar da y'an uwanta suke yi wanda mahaifiyarsu ita ce ta d'aura su a kan wannan turba saboda son abun duniya. Da ana canza mahaifiya da tabbas ta jima da canza nata mahaifiyar. Mahaifinta ne ya fad'o mata a rai, ta san tabbas shi zai fahimceta, to amma wanda zata aura fa? Tuno hakan ya saka ta kuma rushewa da kuka. "Shikenan ni ba'a rubutomin aure a nawa littafin ba. Na shiga uku! Ni wallahi da nayi ta zama a cikin gidan mu ina kwasar bak'in ciki, gwara na tafi *_Wamba_* wajen dangin mahaifina nayi zama na a can. Ban damu da ko k'auye bane ko birni! Buri na in ganni a d'akin mijina ina bautar ubangiji!" Sarah ta fad'i a bayyane tare da mik'ewa ta soma tafiya a k'afa kasancewar layuka shidda ne ya rabasu da inda take. Kan titi _Kasuwar gwari_ ta mik'e tayi ta tafiya har ta iso _Jos road_ sannan tayi k'asa kasancewar can k'asan Jos road d'in suke. Ga zafin rana, ga kuma zazzab'in dake damunta da matsanaici ciwon kai wanda ya ninku sakamakon kukan da tasha. Tana isa k'ofar gidansu gabanta ya yanke ya fad'i ganin motar y'an sanda da kuma y'an sandar a kwar gidansu ga kuma uban cincirundon samari da y'an mata har da wasu matan auren layin da suka fito suna baiwa idanunsu abincin. Tana isowa gaba d'aya idanun jama'a ya dawo kanta. "Yauwa, ga d'aya karuwar ta dawo. Da gani ba gida ta kwana ba. Ai mu dai Allah bai had'a mu da makwaftar kirki ba. Ni dama tashin su za ayi daga unguwar nan don muna da y'ay'a mata dake tasowa kada suga abunda suke yi suma su soma jin sha'awar yi." Fad'in wata mata tana hararar Sarah. Sarah kuwa kutsawa tayi cikin mutanan nan ta shige cikin gidan. Turus ta tsaya ganin Baba a tsakar gida dafe da goshi gaban rigarsa duk jini yana kuka, gefe kuma su aunties d'in Farouq ne da k'annansa maza da mata a gefe sai girgiza suke yi suna fad'in wallahi baza su yarda ba. Nuratu, Aina'u, Na'ima, da Hassana kuma a waje d'aya suna fad'in babu inda zasu je kuma babu uban da ya isa fitar dasu zuwa police station. Lami kuwa sai fad'i take, "Ko kotu za'a je, aje ban jin tsoron uban kowa, sune suka biyo mu har gida da fitina, mu kuma muka kare kanmu." Baba dake kuka ya kalli officer d'in da yake magana cikin lalama akan su Lami su biyosa zuwa station yace, "Bawan Allah d'an sanda, ni na baka umarnin ka tafi dasu da tsiya, idan sunk'i kuyi amfani da k'arfin ku na hukuma ku fitar dasu, amma kuma banda wancen da ta shigo yanzu, don babu hannunta a kan duk abunda ya faru." Ya k'arisa maganar yana nuna Sarah. Police d'in kuwa, bai saurari maganar Baba, sai bada baki yake yi, don babu yanda za ayi ya nuna power ya fitar dasu Nuratu zuwa police station domin Hassana budurwarsa ce, Marfu'a kuma yanzu haka ma tana d'akinsa a wajensa ta kwana jiya. Hassanar ya kira gefe, da kyar taje tana wani cin magani. Sun jima suna magana, a yanda yake lallaminta, zaka d'auka uwarsa ce ita. "To naji, amma wallahi baza mu wuce mintuna ashirin ba a can." Da sauri yace "Na maki alk'awarin haka." Sai da taja tsaki sannan ta koma tayiwa y'an uwanta magana sannan suka fita su duka banda Sarah da ta jingina da bango abun duniya duk ta ishe ta. Ta gaji da matsalar mahaifiyarta da y'an uwanta. K'arisawa tayi wajen Baba duk da jirin da take ji domin taimaka masa ya tashi. Rik'e mata hannu yayi tare da fad'in, "Bari zan iya tashi Saratu. Kema naji jikin naki da zafi sosai. Ya aka yi Aina'u ta rigaki dawowa daga asibitin, ko fad'a kuka yi?" Sai da ta taimaka masa ya mik'e tukun sannan tace, "A'a ba fad'a muka yi ba, nice na baro ta a can asibitin." Baba bai k'ara cewa komai ba sai nufa wajen pamfo da yayi ya wanke goshinsa sannan ya nufi kan baranda ya zauna a kan tabarma tare da fad'in, "Saratu, kiyi hak'uri duk laifi nane da na kasa zab'a maku uwa ta gari. Y'an uwana sun nuna basu son na auri Elizabeth (Lami) amma na nace ni ita nake so sabida yanda ta nuna min k'auna a wancen lokacin. Ban tab'a d'auka Elizabeth za tayi min butulci a rayuwata ba." Kallonsa Sarah tayi tare da fad'in, "Baba ka bani labari, ta yaya ka had'u da Lami har kuka yi aure, kuma mai yasa danginka suke fushi da kai har yanzu? Bamu san kowa naka ba, haka suma basu san mu ba. Dangin Lami ma babu wanda ya san mu, muna bamu san kowa ba sai aunty Rose Merry wanda Lami tace mana y'ar uwarta ce." Sunkuyar da kai Baba yayi tare da fad'in, "Rose Merry ba y'ar uwar mahaifiyarku bace, asali ma itace mai d'aura mahaifiyarku akan turba mara kyau. Taso mahaifiyarku ta koma addininta da ta baro, amma kuma sai mahaifiyarku ta nuna ita tana son addinin musuluncin da ta karb'a." Sarah tace, "To amma Baba Lami bata sallah, bata azumi, duk wani abu na musulunci Lami bata yi. Kuma a hakan ne take cewa tana son musuluncin?" Ajiyar zuciya Baba yayi tare da fad'in, "Nima na jima ina wannan zargin Saratu. Anya kuwa mahaifiyarku bata koma addinin kiristancinta ba kuwa? Domin duk ranar lahadi da sassafe take barin gidan nan, kuma bata dawowa Sia wajajen d'aya ko biyu." Shuru Sarah tayi tana tuno wata rana da mahaifiyar tasu ta dawo daga inda take zuwa duk ranar lahadi, sai ta ganta d'aure da wani zani mai hoton k'atoton cross a jiki, zanin biyu ne, da ta d'aura d'aya a k'ugu, sai ta d'aura wani a sama kasancewar dama farar rigar less ce a jikinta. Ga wani k'aramin Bible a kan gado. "Lami! Wannan wani irin kaya ne haka a jikinki irin na y'an coci?" Saurin kallon jikinta Lami tayi tare da fad'in, "Kai, kin ganni nan d'azu da na fita, shine wata mota tayo kaina, garin na kauce mata sai na fad'a cikin kwata, kuma dama kusa nake da gidan auntynku Rose Merry, shine ta bani wad'annan kayan na saka. Yanzu ma Allah-Allah nake in cire su." Sarah ta kalli Bible d'in tare da fad'in, "Wannan kuma fa Lami!" A harzuk'e tace, "Ke dan ubanki uwata ce ke? Kin cika ni da tsinannun tambayarki. To Rose Merry d'in ce ta bani na ajiye mata a nan anjima idan zata wuce gida zata biyo tanan ta karb'a." Kallonta Baba yayi tare da fad'in, "Lafiya Saratu kike dogon tunani haka?" Sauke ajiyar zuciya Sarah tayi tare da fad'in, "Baba ina tuna wani abu ne. Ina ji a jikina Lami ta koma addinin kiristanci." Daga nan ta kwashe duk labarin abunda ya faru wancen ranar ta fad'a masa. Da mugun mamaki Baba ke kallon Sarah, sai kuma ya girgiza kai tare da fad'in, "Babu abunda Lami ba zata iya aikatawa ba. Lami ta daina bani mamaki sai dai tsoro. "Baba mai ya same ka a goshin ka?" Fad'in Sarah ganin har goshin ya tasa. Sai da ya shafa wajen sannan yace, "Lami ce taje jifan y'an uwan saurayinki da suka yi cincirundo domin d'aukar fansar abunda suka yi shine ta same ni a goshi, kuma kin san budar ba ta roba bace. Don ma Allah ya tsare." Cike da tausayi Sarah yace, "Allah ya k'ara tsareka Baba." Da ameen ya amsa tare da kallonta yace, "To Sarah ya ake ciki? Mai likitocin suka ce wannan karon?" Fad'in Baba yana kallon Sarah data sunkuyar da kai tana hawaye. "Baba akwai cikin?" Sai da gaban Baba ya fad'i da jin haka, amma ya d'aure tare da fad'in, "Kuma Saratu har yanzu baki gano bakin zaren ba?" Shuru Sarah tayi don bata san ta inda zata fara yiwa Baba bayani ba. Hawaye ne kawai ke zubowa daga idanunta yana d'iga a kan tabarmar da suke kai. "Saratu ni mahaifinki ne. Kuma kin san duk fad'in gidan nan babu wanda na shak'u kuma nake jinsa har cikin raina cikin y'ay'ana idan ba ke ba. Kar ki damu, zan fahimceki. Zan kuma yi maki nasiha matsayina na mahaifinki kuma in karb'i k'addararki da hannu bibbiyu. Sai dai ba zan tab'a jin dad'i ba idan har ke da kanki kika kai kanki wajen wani namijin bayan kin yi mi alk'awarin baza ki tab'a yin irin rayuwar da y'an uwanki suke yi ba." Kuka Sarah ta fashe dashi tare da fad'in, "Na rantse da girman ubangijin halittu ban tab'a kaiwa wani namijin jikina ba domin yayi amfani dani. Wallahi, tallahi duk abunda ya faru tsausayi ne Baba. Ban san ta yanda zanyi maka bayani ba Baba. Amma wallahi ban tab'a karya maka alk'awarin da ba d'auka ba." Ko kamun Baba yayi wata maganar wani yaro ya kwad'o sallama tare da fad'in, "Wai ana sallama da Sarah a waje. Wai dan girman Allah ta fito mintuna biyar kawai!"
*_Kuyi hak'uri da wannan, anticipate a long page tomorrow _*
*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*
*_ZULFA'U SA'EED IBRAHIM AKA 👉MATAR SAYYADEE_*
[9/29, 12:59 PM] AMINA KABIR CAPS: 🦜 *KANWAR MATATA* 🦜
*PAGE 9*