← Book details Hiyaam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 55 OF 64

Sashe 55

Hiyaam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ya juya ya kalli Liman, juyawa ya yi sai da ya je bakin ƙofa ya yi musu yanayin da yake nufin "Ka shirya mota ina fitowa yanzu" wata ajjiyar zuciya Al'ameen ya sauke cikin sauri ya rungume Liman yana faɗin "Finally.... Allahamdulillah!"

"Congratulations"

"Thank you Akhy Asad Hafiz Hafiz Baffa Jazakalla bil khair"

Cikin ƙaramin lokaci Malami ya zo da sauran ƴan'uwa. Liman ya shirya cikin wata dakakkiyar shadda domin har dashi za'a je ɗaurin auren na Mu'allim. Sanda ya fito Hajiya Umaimah ta ce "Zai wahala idan matar Asad ƴar arziƙi ce, kina ganin Baffa yaƙi zuwa neman auren Liman gashi zai je na Mu'allim. Kuma ka tabbata ka biya ta gidansu yarinyar ka kawo mini ita, tunda wancan zuwan bana nan tazo" shi dai bai ce komai ba ya fice. Malami ya shigo yana faɗin. "To yanzu ya ce baikon ma an warware baya son auren, when he's ready zai yi magana, bai duba cewa Azizah ƙanwar Hajiya Umaimah bace ba, kalli abin da ya yi" Hajiya Umaimah ta ce

"Malami me nake ji kana faÉ—a ne haka?"

Yana gyara babbar rigarsa ya ce "Baffa ya fasa auren Azizah an warware baikon"

Kafin ta yi magana Al'ameen ya shigo cikin farar shadda me É—auke da babbar riga da hula kana ganinsa kaga ango ya ce "Baffa ya fito, baya jira kun san dai ko?" Yana faÉ—in hakan ya fice. Asad ma ya yi waje abinsa.

Wata baƙar mota Baffa ya shiga me duhun glasses shi ɗaya a Baya sai Al'ameen matsayin driver, Malami da sauran suka shiga motar Asad ya shiga yaja. Suka nufi Kankarofi.

Sanda suka isa suka tarar da unguwar a cike da jama'a, Al'ameen ya sake jin daɗi wato ma an san da zuwan nasu gashi an yi taron ɗaurin aure. Liman ya fito yana ɗan duba lokaci domin yau suna da taron ƙarshen shekara na ƴan jarida. "Ina ne gidan"?

Al'ameen ya ce "Gashi.....," bai ƙarasa faɗa ba yaga an fito da makara Babban yaya ne a gaba shi da Yaa Sam suna riƙe da Gawar Iftihal.

*H I Y A A M*

Page 15: She ran away

Bright pens
Yota/001

I dedicated to her. Pixie ceo NAZY's KITCHEN.

Liman ma sak ya yi ganin an fito da makara da gawa a ciki daga gidan da Mu'allim yazo neman aure, ya yi baya kaɗan yana ƙoƙarin basu waje cikin sauri jikinsa na matuƙar rawa da ɓari Mu'allim ya tari gaban Babban yaya da Yaa Sam, ya kasa magana sai kallon makarar yake a zauce yana riƙe kan shi.

Yaa Sam ne ya samu ƙwarin gwiwar kallon Mu'allim a hankali ya ce "Lafiya dai ko?"

"No, aa". Shine kawai abin da Mu'allim ya iya furtawa. Liman na tsaye yana kallon su.

"Mene ya faru?"

"Sunana Al'ameen Hafizz Hafizz Baffa, ni ne wanda ya nemi auren Iftihal a wajan yayanta Muraad, kuma ya bani izinin zuwa da iyayena domin ɗaura auren a yau ɗin duka" da ƙyar yake haɗe laɓɓansa wajan yin maganar, tsoro yake ji sosai, ba tsoron mutuwa yake yi ba, tunda ya san raɗaɗi da ɗacinta, ya san yadda take saka kaɗaici da mayar da mutum maraya abin tausayi. Ya rasa mahaifinsa Hafizz Hafizz Baffa, yana jin duk wani rashi da za'ayi wa mutum a bayan ta iyaye take. Bai sani ba, amma ya samu kan shi da tsakanin tsoron abin da zuciyarsa ke raya masa, da fargabar jin wanda yake cikin makara ɗin. Yaa Sam ya juya kaɗan.

Tsakanin Yaa Sam da Babban yaya aka rasa mai tankawa Mu'allim maganarsa sbd tsoro.

"Yawwa, na ce zan iya wa Baffa magana?"

"Allah Ya wa Iftihal rasuwa jiya da daddare"

"What!" Mu'allim ya ce da ƙarfin gaske.

Hakan ya janyo hankalin Malami da yake jingine a jikin mota, shima yana mamakin cikar da aka yi a unguwar ta Kankarofi ɗin. Jin sautin muryar Mu'allim ya saka Malami ƙarasawa wajan ya kalle su ya ce "Menene?"

"Abba, wai cewa sukai ta rasu"

Ya runtse idanunta numfashinsa na kakkatse masa a ƙirji ya ce "I couldn't believe, wai ce mini sukai ta rasu, wai ta mutu, ko dan kar su bani aurenta ne? Ko ban cancanci zama mijinta bane? Ko ina da wani aibu ko mummunan hali ne Abba?" Abba Malami ya riƙo Mu'allim, Liman ya ƙarasu yana dafe kafaɗar Mu'allim ya ce

"Please Al'ameen, ka nutsu"

"Ahky Liman ya zan nutsu? Jiya nina kawo Iftihal gidan nan da kaina, kuma yau sai ace ta rasu? Ai data rasu da na ji hakan a jikina da kuma zuciyata. Aurenta ne kawai basa son bani. Me ya sa ba ku faɗa musu ni jinin Hafiz Baffa ne, ni ɗaya daga cikin zuri'ar Sayyadi Baffa bane, bani da mugun hali" idanunsa ya yi jajur jikinsa na rawa, Liman ya saka hannunsa ya riƙo shi sosai da ƙoƙarin janye shi domin ya basu waje a yi mata sallar Jana'iza kamar yadda addini ya tanadar. Abba Malami ya kalli Mu'allim ya ce "Dawa kukai magana a jiya ɗin Al'ameen?"

Ya nuna Babban yaya ya ce "Yayanta"

Abba Malami ya kalli Yaya ya ce "Bawan Allah mene gaskiyar magana? Yarinyar da Al'ameen ya kawo mu domin nema masa aurenta ne ta rasu ko wata ce a cikin gidan daban?" Kallon su kawai Babban yaya yake yi, zuciyarsa ta masa nauyi laɓɓansa sun bushe. Da wani irin yanayi kuma ya ce "Eh"

"Ina nufin da gaske ta rasu jiya da daddare"

"Mene ya same ta? Jinya ta yi?"

Yaa Sam ya ce "Tana da mutanen ɓoye ne, ta fito zata banɗaki shine suka tashi ta faɗa cikin rijiya, sanda aka shiga ceto ta, already ta rasu a cikin rijiyar, ka yi haƙuri, tunda har yayanta ya amince da auren to kamala da mutumcinka ya kai har ya yi yawa, ai babu wanda bai san sunan Baffas family ba"

"Abba ban yadda ta rasu ba, ba Iftihal bace ta rasu. Don Allah Yaa Muraad ka bani auren Iftihal, wallahi ina son ta zan kula da ita sosai" Babban yaya baya buƙatar sabon tashin hankali da hayaniya, duk abin da zai saka ya yi magana a yanzu baya buƙata, a birkice yake jin kan shi sosai. Ya juya kaɗan ya kalli Yaa Sam ya kalli Jaheed dake baya yana riƙe da hannun makarar sai mahaifin Haysaam. "Ku ajjiye makarar ya gani" sannu a hankali suka sauke makarar a ƙasa, jikin Mu'allim na rawa ya durƙushe a wajan da farar shaddarsa ta angwanci, ya miƙa hannunsa kaɗan ya yaye likkafanin. Kyakkyawar fuskarta me cike da annuri ce ta fara yi masa sallama a cikin idanunsa. Ita ɗin ce dai, yarinyar da zuciyarsa ta so a lokaci guda, son da yake jin ba zai sake samun wacce zai yi wa irinsa ba. A hankali ya ja idanunsa ya lumshe, da tunanin mafarki ne, da tunanin zai farka ya ji shelar an ɗaura musu aure, da tunanin zai farka ya ji ta amsa sunan Mrs Al'ameen Hafizz Baffa.

Ya buɗe idanun da ƙyar da nauyin zuciya ya ce "Allah Ya yi miki rahama Aysha, Allah Ya ji ƙan ki, Ubangiji Ya sa mutuwa hutu ce a gare ki, Allah Ya haskaka miki makwancinki"

Luu idanunsa suka fara lumshe.

Liman dake tsaye shima yana kallon fuskar yarinyar domin tabbas ita ya gani sanda suka zo shi da Ahlam gidan. "Take heart"

Ya ce yana É—an bubbuga kafaÉ—arsa.

Ya ja likkafanin ya rufe mata fuska, Liman ya ɗago shi tsaye yana miƙawa ya faɗa jikin Liman shi kuma ya yi saurin rungume shi cike da soyayya yana bubbuga bayansa.

Abba Malami ya juya zuwa motar da Sayyadi Baffa yake ciki, ya yi knocking ya ɗauki wajan 10 seconds a tsaye kafin a sauke glasses ɗin ƙasa, yana kishingiɗe a bayan motar idanunsa rufe, farar shadda ce a jikinsa, ya zagaya scarf a samanta wanda ya sake fito da martabarsa ta kasancewarsa shugaban Hisba, malamin addinin Islama, me zuwa yaɗa Musulunci gari-gari, ƙasa ƙasa yana yin da'awa. Kamar kodayaushe ya yi rawani a fuskarsa, hatta idanunsa ya saka su cikin glasses ba zaka taɓa sanin wanene ba, hannunsa riƙe da ƙaramin littafi yana dubawa, ɗaya hannun ƙaramar counter ce yana tasbihi da ita. Luf luf haka gargasa ta lulluɓe farar fatar hannunsa, ba zaka taɓa kallon Sayyadi Baffa ba ka ɗauka ya yi shekarun da suke jingine da rayuwarsa, jikinsa gabaɗaya bai nuna shekarun ba.

Ba kuma zaka taɓa yadda ya haifi tagwayen yara mata masu shekaru har sha bakwai ba.

Abba Malami ya yi ƙasa muryarsa ya ce

"Yarinyar da aka zo nemawa Al'ameen aurenta Allah Ya yi mata rasuwa, yanzu haka Jana'izarta za'ayi ba, shine ka ga taron jama'a" A nutse ya juya kamar zai kalli Malami sai ya fasa, ya ajjiye azkar ɗin hannunsa bai ce komai ba ya ɗauke kai. Abba Malami ya juya zuwa inda aka ajjiye gawar za'ayi Jana'iza, jama'a duk an hau jam'i ana jiran liman, Mu'allim da Liman suna sawun gaba. Malami ya san Baffa ba zai taɓa fitowa ba. Bisa mamaki sai ya ji saukar kamilalliyar muryarsa me cike da kamala da zallar kwarjini ta sauka a kunnen ɗaruruwar jama'ar da suka samu jana'izar Iftihal. A kabbarar da ya yi ta farko wajan ya yi tsit, muryar Sayyadi Baffa na dukan kunnawansu suka samu kan su da yin wata sabuwar nutsuwa bayan wacce suke ciki.

Shi da kan shi ya yi wa Iftihal sallah, kuma ya sunkuya aka É—auki makara dashi aka saka a mota, ya koma cikin motarsa. Babu wanda ya san waye shi, amma muryarsa na tunawa jama'a da babban malamin nan.

Wato Sayyadi Baffa. Sai suka yi tunanin ko wani ne yake kwaikwayon Sayyadi Baffa É—in.
Chapter 55 · 0% Book details