Sashe 23
Hiyaam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani irin hawaye masu zafin gaske ne suka shiga sunturi a saman fuskarta, jikinta ya shiga rawa da ɓari a wahalar ce ta shiga faɗin. "Mijina Ya Allah. Ya zan ce bana son mijina? Gyara naka ne, shiriya taka ce, Allah ka shirya mini mijina ka dawo dashi hanyar tsira kar ya koma gare ka cikin wannan mummunan tufar, bana riƙon shi a raina bana jin zafinsa. Allah ka dawo dashi kan tafarki madaidaici, ka kiyaye masa alƙalaminsa daga aikata mugun abu akan kowacce ɗiya mace ko don tsoron dawowa gare ka. Ko don tarihin zuri'arsa.....,"
Bam! Ta ji ƙarar buɗe ƙofar da ya yi ya shigo, wata faɗuwar gaba ta saukar mata. Kafin ta yi yunƙurin matsawa ta ji saukar ita ce a gadon bayanta, azaba, raɗaɗin da bata taɓa jin irinsa ba ya saka ta saki wata ƙara haɗe da kiran sunan Allah. Daman niyyar tashi take yi saboda nishin da ta ji a ɗakin samarin yaranta wanda babu tantama Jadid ne ciwonsa ya tashi, ciwon ƙodar da yake fama dashi. Ƙarar da ta yi na farko ya fito da Jaheed daga cikin ɗaki dai-dai lokacin ma Ana ta fito ta kafe Daada da ido, yau ma tik yake haihuwar uwarsa babu kaya a jikinsa. Jaheed na ƙoƙarin janye Innti, Daada ya sake ɗaga icen hannunsa ya sake makawa Innti a gadon bayanta. A hargitse Jaheed ya nufi Daada zai ture shi. "Idan ka sake hannunka ya sauka akan mahafinka zan maka Allah Ya isa Jaheed. Mahafinka ne"
Cak Jaheed ya tsaya jikinsa na wani irin rawa da ɓari hawayen daya cika idanunsa ya shiga bin fuskarsa ya durƙushe a wajan.
"Daada ka yi haƙuri, ka ji tsoron Allah ka tuna mu da Innti amana ce a gare ka, matarka ce. Kar hakkin Innti ya bimu har gidan aurenmu" Iftihal ce ta furta hakan bayan ta fito daga ɗakin. "Daada ka tuna faɗar Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, dukan mata rashin adalci ne, idan ya zama tura da bakin riga ake dukan su, haka Mu'allim ya ce mana. Muna son ka muna kwaɗayin rayuwa da kai, kar ka kashe mana Innti" kallon Ifti ya yi zai kai mata duka sai ya tuna yarjejeniyar cacar da yake kanta, zai samu miliyan ashirin cif saboda ita, don haka a yanzu ita kallon kuɗi yake mata. Ya kalle su sama da ƙasa kafin ya ce
"Na tsani haihuwa, me ya saka ta saki jiki duk ta haife ku kamar wata dabba, uwarku bata da amfani ita da dabba ɗaya suke a wajena. Jaka ce, daƙiƙiyya mara amfani"
"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"
Iftihal ta furta tana fashewa da kuka, tana jin kamar zuciyarta ce zata fito waje.
Daada ya sake kallon Innti take durƙushe ya ce "Wallahi Tani ta fita armashi da garɗi, ta sani bana son haihuwa me ya saka ta haife ku har haka? Ku duka tsinannu ne ba za ku yi albarka ba. Allah wadaran....," a zabure Innti ta miƙe tana girgiza kai kafin ta ce
"Kar ka aibata mini zuri'a Daada, kar furucinka ya zame musu Harshen wuta, ka yi wa girman Allah Daada...," bai bari ta ƙarasa ba ya ɗauke ta da mari ya nuna ta da manuniyya "Na faɗa, Allah Ya tsine musu dake dasu gabaɗaya, zuri'ar da bata da wani amfani kema ba ki da amfani bare su, sai sun watse sun bi duniya. Allah ya tsine musu, Allah ya farraƙu gabaɗaya na huta"
"Allah Ya tsine maka dai Daada da kai da Tani Allah Ya tsine muku" muryar Ana ta sauka akan kunnuwansu....
*H I Y Y A M*
Page 7: Abbaa, Save Me
Bright pens
Yota/001
Stay blessing as always FALMATA.
Wani irin ɗauke ta da mari Innti ta yi, kafin Ana ta dawo hayyacinta ta sake sauke mata wani lafiyayyen mari a ɓarin dama na ƙuncin kyakkyawar fuskar yarinyar.
A firgice kuma ta ce
"Allah Ya shirya ki Allah kai bani yarinyar ka shirya mini Ayshatuna" ta ɗora "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Salatin Innti ya karaɗe cikin gidan har zuwa maƙota. Jikinta yana wani irin rawa ta sake durƙushewa a wajan ta kasa furta komai saboda yadda laɓɓanta suke rawa a saman bakinta. Da ƙyar ta ɗago kai ta kalli Ana, ta ɗauka za taga fuskar yarinyar cikin damuwa da tsoron kalaman data jefi mahaifin nata dasu, sai taga saɓanin hakan a tattare da ita. Babu tsoron, babu ladama ko guda dake mintsinin zuciyar Ana. Kamar ma ta shirya furta da wasu zantukan da suka fi na baya muni. Sharr hawaye ya sako a idanun Innti. Da rawar ɗari kamar jonin wutar lantarki haka Jaheed ya zame kusa da Innti da rawar murya cike da rauni ya ce
"Mun shiga uku....
"Kuka kike Innti? Hawaye kike fitarwa?" Ya yi furucin muryarsa na rawa tana kakkatse masa a maƙoshi saboda tsananin tsoro da tashin hankalin yau mahafiyarsu ke zubar wa da ƴar data haifa hawaye, duk da ta san hawayenta azaba ne a gare su, musamman ga Ana ɗin da take da busasshiyar zuciya, ba zata jure ba idan sun yi haƙuri wajan kawar da kai daga ƙaddararsu. Ƙaddarar da Ubangiji ya zaɓa musu yake son ganin su a cikinta.
Jadid ma riƙo hannun Inntin ya yi a cikin nasa yana kallon ta, a sanyaye kamar an watsawa kifi gishiri ya ce "hawaye kike zubarwa akan kalaman Daada? Kar ki yi kuka Innti, kar ki yi baƙin ciki don Allah" girgiza kai ta shiga yi a hankali tana ƙoƙarin dakatar da Jaheed daga goge mata hawayen idanunta. Ta riƙe su da ƙarfi ta ce
"Ana....
"Ka ji furucin da Ana ta yi? Ka ji me ta ce akan mahaifinku?" Ta ja numfashi me zafi ta yi feshin shi a gefen fuskar Jadid, da sauri ya yi ƙasa da kan shi yana kiran sunan Allah, hucin numfashinta ya bashi yaƙinin gwargwadon yadda zuciyarta ke ɗaukan ɗumi akan al'amuran Daada. Gashi wata haƙar na neman kai su ga rijiya madadin ganin ruwa, Ana na ƙoƙarin zame musu wata jarrabawa me wahalar gaske musamman ga Innti gama dukkan su gabaɗaya. "Jaheed, Jadid" ta kira sunayensu "Me ya sa ɗabi'un shalele yake da tawaya da naku? Me ya sa komai naku ya yi hannun riga da nata? Bafa ta san kuskure ta yi ba"
"Kuskure?" Ana ta faɗa tana wani irin lumshe manyan idanunta da suke gajiye da al'amuran gidan nasu ga raɗaɗin marin da Innti ta yi mata amma ko gezau ba ta yi ba, daman ita bata taɓa saka ciwon kan Daada a matsayin lalurarta ba, bata taɓa takaici akan abubuwan da yake yi na gurɓata musu suna ba. Da yawan lokaci tana cewa "Matsalolin Daada nasa ne, haka kuma damuwarsa tasa kawai bata Ana ba" yanzu ma take tsaye tana fuskantar Daada wanda ya yi mutuwar tsaye da jin furucin da ko matarsa bai taɓa hasasowa zata jefa masa su ba, balle ɗiyar daya haifa.
A hankali ta saka hannunta guda ɗaya ta ɗora a saitin ƙirjinta, ji take kamar zuciyarta ce take kekketa fatar ƙirjin tana ƙoƙarin ratso ƙirjinta ta fito waje. Bakinta ta ware tana ƙoƙarin cewa wani abu sai ta ji kamar ya tsaya mata, ta haɗe laɓɓanta waje guda ta taune su, taja idanunta ta lumshe su, idanun da shi kan shi Daada suke bashi ciwon kai a rayuwa. Da ƙyar ta iya cewa ta kalli Iftihal wacce take ta sharɓar kuka sosai. Da rashin fahimtar ma'anar kukan
Ana ta ce "Me na ce ne?"
"Tsoro nake ji mahaɗita, tsinewa Daada kikai" cewar Iftihal tana ƙanƙame jikinta. Ana ta juya ta ce
"Shine me? Daadan na farko ne da ba za'a iya tsine masa ba? Babu abin da zai faru sai hukuncin Allah" ta ƙarasa kusa da Iftihal ta ce "Ta ya kike tunanin bakin dake shan giya, jikin dake ɗaukan zunubi da Iskanci dana cin zarafin matarsa da ƴaƴansa don ya tsine mana zai yi tasiri akan mu? Wannan mutumin ko ledar pure water ya tsinewa babu abin da zai same ta, balle mu da muke tare da albarkar Innti" ƙuri Iftihal ta yi wa Ana da idanunta masu rauni da suka cika da tausayin Ana ɗin matuƙa saboda taurin kanta. Murmushi kawai Ana ta yi, tana ƙoƙarin riƙe kanta daga jirin dake ɗaukarta.
Sai ta ɗan daƙune fuska ta ce
"Rabin rai"
"Na'am Rabin rai" Iftihal ta amsa a sanyaye
"Smile for me, ki yi murmushi saboda ni" ta shafi fuskarta
"Kawai ina son ki ne Ana, ina jin kamar ba zan iya rayuwa ba idan babu ke a gefena"
Ana ta ware blue eyeballs ɗinta kamar za ta yi magana sai kuma ta fasa, ta kafe Iftihal da ido sai kallon ta take yi kamar zata mayar da ita ciki, a hankali kuma take shafa fuskarta ta ɗauki lokaci a haka kafin ta sauke ajjiyar zuciya saboda ƙwarin gwiwar data samu sanda ta fahimci nutsuwa a tattare da Iftihal, wani irin sarawa kanta yake mata gefe guda kamar me shirin tafiya da ganinta ko kai ta lahira. Durƙusawa ta yi daidai inda Innti take zaune cikin sanyin murya da confidence ta ce "Na ɗauka za ki bani tukucin kalamaina ne Innti ta hanyar yi wa cikina alheri da abinci kar na kwana da yunwa. Ciwon kai na ke ji sosai a tattare dani" Innti ta yi mata shiru sai kallon ta kawai take yi kamar bata fahimci me take faɗa ba. A hankali Ana ta ce "Na yafe abincin, ko albarka ki saka mini da addu'ar samun kyakkyawan miji ko Aljani ko maye..," Kyakkyawan marin da Innti ta ɗauke Ana dashi hagu da dama a karo na biyu shine ya hanata ƙarasa faɗar abin da ta yi niyya, ta yi baya tare da yin zama raƙuma ta dafe kuncinta tare da zubawa Innti idanunta masu kaifi da haske.
Cikin zafin nama Innti ta ce "Har kike da kalmomin tara ta dasu bayan kin yi wa mahafinki rashin É—a'a. Ba haka na ba ki tarbiyya ba, ba abin da na nuna muku kenan ba Aysha. Me ya sa don me ya sa?" Ta kalli Babban yaya da yake jingine da jikin bango yana kallon gefe guda kamar baya tsakar gidan abubuwan da suke faruwa suke wakana É—in. "Ko dai ina da tawaya wajan gina tarbiyyar Aysha ne Yaya?"
Bam! Ta ji ƙarar buɗe ƙofar da ya yi ya shigo, wata faɗuwar gaba ta saukar mata. Kafin ta yi yunƙurin matsawa ta ji saukar ita ce a gadon bayanta, azaba, raɗaɗin da bata taɓa jin irinsa ba ya saka ta saki wata ƙara haɗe da kiran sunan Allah. Daman niyyar tashi take yi saboda nishin da ta ji a ɗakin samarin yaranta wanda babu tantama Jadid ne ciwonsa ya tashi, ciwon ƙodar da yake fama dashi. Ƙarar da ta yi na farko ya fito da Jaheed daga cikin ɗaki dai-dai lokacin ma Ana ta fito ta kafe Daada da ido, yau ma tik yake haihuwar uwarsa babu kaya a jikinsa. Jaheed na ƙoƙarin janye Innti, Daada ya sake ɗaga icen hannunsa ya sake makawa Innti a gadon bayanta. A hargitse Jaheed ya nufi Daada zai ture shi. "Idan ka sake hannunka ya sauka akan mahafinka zan maka Allah Ya isa Jaheed. Mahafinka ne"
Cak Jaheed ya tsaya jikinsa na wani irin rawa da ɓari hawayen daya cika idanunsa ya shiga bin fuskarsa ya durƙushe a wajan.
"Daada ka yi haƙuri, ka ji tsoron Allah ka tuna mu da Innti amana ce a gare ka, matarka ce. Kar hakkin Innti ya bimu har gidan aurenmu" Iftihal ce ta furta hakan bayan ta fito daga ɗakin. "Daada ka tuna faɗar Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, dukan mata rashin adalci ne, idan ya zama tura da bakin riga ake dukan su, haka Mu'allim ya ce mana. Muna son ka muna kwaɗayin rayuwa da kai, kar ka kashe mana Innti" kallon Ifti ya yi zai kai mata duka sai ya tuna yarjejeniyar cacar da yake kanta, zai samu miliyan ashirin cif saboda ita, don haka a yanzu ita kallon kuɗi yake mata. Ya kalle su sama da ƙasa kafin ya ce
"Na tsani haihuwa, me ya saka ta saki jiki duk ta haife ku kamar wata dabba, uwarku bata da amfani ita da dabba ɗaya suke a wajena. Jaka ce, daƙiƙiyya mara amfani"
"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"
Iftihal ta furta tana fashewa da kuka, tana jin kamar zuciyarta ce zata fito waje.
Daada ya sake kallon Innti take durƙushe ya ce "Wallahi Tani ta fita armashi da garɗi, ta sani bana son haihuwa me ya saka ta haife ku har haka? Ku duka tsinannu ne ba za ku yi albarka ba. Allah wadaran....," a zabure Innti ta miƙe tana girgiza kai kafin ta ce
"Kar ka aibata mini zuri'a Daada, kar furucinka ya zame musu Harshen wuta, ka yi wa girman Allah Daada...," bai bari ta ƙarasa ba ya ɗauke ta da mari ya nuna ta da manuniyya "Na faɗa, Allah Ya tsine musu dake dasu gabaɗaya, zuri'ar da bata da wani amfani kema ba ki da amfani bare su, sai sun watse sun bi duniya. Allah ya tsine musu, Allah ya farraƙu gabaɗaya na huta"
"Allah Ya tsine maka dai Daada da kai da Tani Allah Ya tsine muku" muryar Ana ta sauka akan kunnuwansu....
*H I Y Y A M*
Page 7: Abbaa, Save Me
Bright pens
Yota/001
Stay blessing as always FALMATA.
Wani irin ɗauke ta da mari Innti ta yi, kafin Ana ta dawo hayyacinta ta sake sauke mata wani lafiyayyen mari a ɓarin dama na ƙuncin kyakkyawar fuskar yarinyar.
A firgice kuma ta ce
"Allah Ya shirya ki Allah kai bani yarinyar ka shirya mini Ayshatuna" ta ɗora "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Salatin Innti ya karaɗe cikin gidan har zuwa maƙota. Jikinta yana wani irin rawa ta sake durƙushewa a wajan ta kasa furta komai saboda yadda laɓɓanta suke rawa a saman bakinta. Da ƙyar ta ɗago kai ta kalli Ana, ta ɗauka za taga fuskar yarinyar cikin damuwa da tsoron kalaman data jefi mahaifin nata dasu, sai taga saɓanin hakan a tattare da ita. Babu tsoron, babu ladama ko guda dake mintsinin zuciyar Ana. Kamar ma ta shirya furta da wasu zantukan da suka fi na baya muni. Sharr hawaye ya sako a idanun Innti. Da rawar ɗari kamar jonin wutar lantarki haka Jaheed ya zame kusa da Innti da rawar murya cike da rauni ya ce
"Mun shiga uku....
"Kuka kike Innti? Hawaye kike fitarwa?" Ya yi furucin muryarsa na rawa tana kakkatse masa a maƙoshi saboda tsananin tsoro da tashin hankalin yau mahafiyarsu ke zubar wa da ƴar data haifa hawaye, duk da ta san hawayenta azaba ne a gare su, musamman ga Ana ɗin da take da busasshiyar zuciya, ba zata jure ba idan sun yi haƙuri wajan kawar da kai daga ƙaddararsu. Ƙaddarar da Ubangiji ya zaɓa musu yake son ganin su a cikinta.
Jadid ma riƙo hannun Inntin ya yi a cikin nasa yana kallon ta, a sanyaye kamar an watsawa kifi gishiri ya ce "hawaye kike zubarwa akan kalaman Daada? Kar ki yi kuka Innti, kar ki yi baƙin ciki don Allah" girgiza kai ta shiga yi a hankali tana ƙoƙarin dakatar da Jaheed daga goge mata hawayen idanunta. Ta riƙe su da ƙarfi ta ce
"Ana....
"Ka ji furucin da Ana ta yi? Ka ji me ta ce akan mahaifinku?" Ta ja numfashi me zafi ta yi feshin shi a gefen fuskar Jadid, da sauri ya yi ƙasa da kan shi yana kiran sunan Allah, hucin numfashinta ya bashi yaƙinin gwargwadon yadda zuciyarta ke ɗaukan ɗumi akan al'amuran Daada. Gashi wata haƙar na neman kai su ga rijiya madadin ganin ruwa, Ana na ƙoƙarin zame musu wata jarrabawa me wahalar gaske musamman ga Innti gama dukkan su gabaɗaya. "Jaheed, Jadid" ta kira sunayensu "Me ya sa ɗabi'un shalele yake da tawaya da naku? Me ya sa komai naku ya yi hannun riga da nata? Bafa ta san kuskure ta yi ba"
"Kuskure?" Ana ta faɗa tana wani irin lumshe manyan idanunta da suke gajiye da al'amuran gidan nasu ga raɗaɗin marin da Innti ta yi mata amma ko gezau ba ta yi ba, daman ita bata taɓa saka ciwon kan Daada a matsayin lalurarta ba, bata taɓa takaici akan abubuwan da yake yi na gurɓata musu suna ba. Da yawan lokaci tana cewa "Matsalolin Daada nasa ne, haka kuma damuwarsa tasa kawai bata Ana ba" yanzu ma take tsaye tana fuskantar Daada wanda ya yi mutuwar tsaye da jin furucin da ko matarsa bai taɓa hasasowa zata jefa masa su ba, balle ɗiyar daya haifa.
A hankali ta saka hannunta guda ɗaya ta ɗora a saitin ƙirjinta, ji take kamar zuciyarta ce take kekketa fatar ƙirjin tana ƙoƙarin ratso ƙirjinta ta fito waje. Bakinta ta ware tana ƙoƙarin cewa wani abu sai ta ji kamar ya tsaya mata, ta haɗe laɓɓanta waje guda ta taune su, taja idanunta ta lumshe su, idanun da shi kan shi Daada suke bashi ciwon kai a rayuwa. Da ƙyar ta iya cewa ta kalli Iftihal wacce take ta sharɓar kuka sosai. Da rashin fahimtar ma'anar kukan
Ana ta ce "Me na ce ne?"
"Tsoro nake ji mahaɗita, tsinewa Daada kikai" cewar Iftihal tana ƙanƙame jikinta. Ana ta juya ta ce
"Shine me? Daadan na farko ne da ba za'a iya tsine masa ba? Babu abin da zai faru sai hukuncin Allah" ta ƙarasa kusa da Iftihal ta ce "Ta ya kike tunanin bakin dake shan giya, jikin dake ɗaukan zunubi da Iskanci dana cin zarafin matarsa da ƴaƴansa don ya tsine mana zai yi tasiri akan mu? Wannan mutumin ko ledar pure water ya tsinewa babu abin da zai same ta, balle mu da muke tare da albarkar Innti" ƙuri Iftihal ta yi wa Ana da idanunta masu rauni da suka cika da tausayin Ana ɗin matuƙa saboda taurin kanta. Murmushi kawai Ana ta yi, tana ƙoƙarin riƙe kanta daga jirin dake ɗaukarta.
Sai ta ɗan daƙune fuska ta ce
"Rabin rai"
"Na'am Rabin rai" Iftihal ta amsa a sanyaye
"Smile for me, ki yi murmushi saboda ni" ta shafi fuskarta
"Kawai ina son ki ne Ana, ina jin kamar ba zan iya rayuwa ba idan babu ke a gefena"
Ana ta ware blue eyeballs ɗinta kamar za ta yi magana sai kuma ta fasa, ta kafe Iftihal da ido sai kallon ta take yi kamar zata mayar da ita ciki, a hankali kuma take shafa fuskarta ta ɗauki lokaci a haka kafin ta sauke ajjiyar zuciya saboda ƙwarin gwiwar data samu sanda ta fahimci nutsuwa a tattare da Iftihal, wani irin sarawa kanta yake mata gefe guda kamar me shirin tafiya da ganinta ko kai ta lahira. Durƙusawa ta yi daidai inda Innti take zaune cikin sanyin murya da confidence ta ce "Na ɗauka za ki bani tukucin kalamaina ne Innti ta hanyar yi wa cikina alheri da abinci kar na kwana da yunwa. Ciwon kai na ke ji sosai a tattare dani" Innti ta yi mata shiru sai kallon ta kawai take yi kamar bata fahimci me take faɗa ba. A hankali Ana ta ce "Na yafe abincin, ko albarka ki saka mini da addu'ar samun kyakkyawan miji ko Aljani ko maye..," Kyakkyawan marin da Innti ta ɗauke Ana dashi hagu da dama a karo na biyu shine ya hanata ƙarasa faɗar abin da ta yi niyya, ta yi baya tare da yin zama raƙuma ta dafe kuncinta tare da zubawa Innti idanunta masu kaifi da haske.
Cikin zafin nama Innti ta ce "Har kike da kalmomin tara ta dasu bayan kin yi wa mahafinki rashin É—a'a. Ba haka na ba ki tarbiyya ba, ba abin da na nuna muku kenan ba Aysha. Me ya sa don me ya sa?" Ta kalli Babban yaya da yake jingine da jikin bango yana kallon gefe guda kamar baya tsakar gidan abubuwan da suke faruwa suke wakana É—in. "Ko dai ina da tawaya wajan gina tarbiyyar Aysha ne Yaya?"